< Ezekiel 47 >

1 Afterward he brought me again to the door of the house; and behold, waters issued forth from under the threshold of the house eastward; for the fore-front of the house stood toward the east. And the waters flowed down from the side of the house, south of the altar.
Mutumin ya komo da ni zuwa mashigin haikalin, sai na kuwa ga ruwa yana malalowa daga ƙarƙashin madogarar ƙofar haikalin wajen gabas (gama haikalin yana fuskantar gabas). Ruwan yana malalowa daga ƙarƙashin gefen kudun haikalin, kudu da bagaden.
2 Then he brought me out by the way of the gate northward; and he brought me round by the way without to the outer gate, that looked toward the east; and behold, there ran out waters from the right side.
Sai ya fitar da ni ta ƙofar arewa ya kewaye da ni ta waje zuwa ƙofar da take waje mai fuskantar gabas, ruwan kuwa yana malalowa daga wajen kudu.
3 And when the man that had the line in his hand went forth eastward, he measured a thousand cubits, and he led me through the waters, and the waters were to the soles of the feet.
Yayinda mutumin ya yi wajen gabas da karan awo a hannunsa, sai ya auna kamu dubu ya kuma bi da ni ta ruwan da zurfinsa ya kama ni a idon ƙafa.
4 Again he measured a thousand cubits, and led me through the waters, and the waters were to the knees. Again he measured a thousand cubits, and led me through, and the waters were to the loins.
Ya auna wani kamu dubu ya kuma bi da ni a ruwan da zurfinsa ya kai ni gwiwa. Ya sāke auna kamu dubu ya kuma bi da ni a ruwan da zurfinsa kama ni a gindi.
5 Again he measured a thousand cubits, and it was a river, which I could not pass through; for the waters were high, waters to swim in, a river which could not be passed through.
Ya auna wani kamu dubu, amma a yanzu ruwan ya zama kogin da ban iya hayewa ba, domin ruwan ya taso ya kuma yi zurfin da ya isa a yi iyo a ciki, kogin da ba za a iya hayewa ba.
6 And he said to me, Hast thou seen this, son of man? Then he brought me back to the brink of the river.
Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, ka ga wannan?” Sa’an nan ya komo da ni zuwa bakin kogin.
7 Now when I had returned, behold, at the brink of the river were very many trees, on the one side and on the other.
Sa’ad da na iso can, sai na ga itatuwa masu yawa a kowane gefen kogin.
8 Then said he to me, These waters issue forth toward the east region, and run down into the desert, and go into the sea; they go forth into the sea, and the waters shall be healed.
Sai ya ce mini, “Wannan ruwa yana malalowa zuwa yankin gabas ya kuma gangaro zuwa cikin Araba, inda zai shiga Teku. Sa’ad da ya shiga cikin Tekun sai ruwan a can ya zama mai daɗi.
9 And it shall come to pass, that every living thing that moveth, whithersoever the river shall come, shall live, and there shall be very many fish there; for when these waters shall come thither, [[the waters of the sea]] shall be healed, and everything shall live whither the river cometh.
Tarin halittu masu rai za su rayu a duk inda ruwan ya malalo. Za a kasance da kifi masu yawa, domin wannan ruwa yana malalowa a can yana kuma mai da ruwan gishiri yă zama ruwa mai daɗi; saboda haka duk inda ruwan ya malalo, kome zai rayu.
10 And it shall come to pass that fishers shall stand upon it; from En-gedi to En-eglaim shall be places to spread nets; and therein shall be fish according to their kinds, like the fish of the great sea, exceeding many.
Masunta za su tsaya a gaɓar; daga En Gedi zuwa En Eglayim, za a kasance da wuraren jefa abin kamun kifi. Za a sami kifayen iri-iri, kamar kifaye Bahar Rum.
11 But the miry places thereof, and the marshes thereof, shall not be healed; they shall be appointed for salt.
Amma fadamun da tafkunan ba za su zama masu daɗi ba; za a bar su a gishirinsu.
12 And by the river, upon the bank thereof, on this side and on that side, shall grow all trees for food, whose leaf shall not fade, and whose fruit shall not fail; every month shall they bring forth new fruit; because their waters issue forth from the sanctuary. And their fruit shall be for food, and their leaves for medicine.
’Ya’yan itatuwa na kowane iri za su yi girma a kowane gefen kogin. Ganyayensu ba su bushe ba, ba kuwa za su fasa yin’ya’ya ba. Kowane wata za su ba da’ya’ya domin ruwa daga wuri mai tsarki yana malalo musu.’Ya’yansu za su zama abinci, ganyayensu kuma za su zama magani.”
13 Thus saith the Lord Jehovah: This is the border, according to which ye shall distribute the land among the twelve tribes of Israel. Joseph shall have two portions.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Waɗannan su ne iyakokin da za ku raba ƙasar gādo cikin kabilan Isra’ila goma sha biyu, da rabo biyu don Yusuf.
14 And ye shall inherit it, one like another. For I have lifted up my hand, that I would give it to your fathers; and this land shall fall to you for an inheritance.
Za ku raba ta daidai a cikinsu. Gama na ɗaga hannu na rantse zan ba da ita ga kakanninku, wannan ƙasa za tă zama gādonku.
15 And this shall be the border of the land toward the north side: from the great sea toward the way of Hethlon, as men go to Zedad,
“Wannan ce za tă zama iyakar ƙasa. “A wajen arewa za tă fara daga Bahar Rum ta hanyar Hetlon ta wuce Lebo Hamat zuwa Zedad,
16 Hamath, Berothah, Sibraim, which is between the border of Damascus and the border of Hamath, and Hazar-hatticon, which is by the coast of Hauran.
Berota da Sibrayim (wadda take a iyaka tsakanin Damaskus da Hamat), har zuwa Hazer-Hattikon, wadda take a iyakar Hauran.
17 And the border from the sea shall be Hazar-Enon, the border of Damascus and farther northward, and the border of Hamath.
Iyakar za tă miƙe daga teku zuwa Hazar-Enon, ta iyakar Damaskus, da iyakar Hamat a arewa. Wannan ita ce iyakar a wajen arewa.
18 This is the north side. And the east side ye shall measure between Hauran and Damascus, and between Gilead and the land of Israel by the Jordan, from the border to the east sea. This is the east side.
A wajen gabas iyakar za tă kama tsakanin Hauran da Damaskus, ta bi ta Urdun tsakanin Gileyad da ƙasar Isra’ila, zuwa tekun gabas har zuwa Tamar. Wannan ita ce iyakar a wajen gabas.
19 And the south side southward shall be from Tamar to the waters of strife in Kadesh, as far as the river by the great sea.
A wajen kudu za tă fara daga Tamar har zuwa ruwan Meriba Kadesh, sa’an nan ta bi Rafin Masar zuwa Bahar Rum. Wannan ita ce iyakar a wajen kudu.
20 This is the south side southward. And the west side shall be the great sea, from the border till a man come over against Hamath. This is the west side.
A wajen yamma, Bahar Rum ne zai zama iyakar zuwa wani wuri ɗaura da Lebo Hamat. Wannan ita ce iyakar a wajen yamma.
21 So shall ye divide this land among you, according to the tribes of Israel.
“Za ku rarraba wannan ƙasa a tsakaninku bisa ga kabilan Isra’ila.
22 And ye shall divide it by lot for an inheritance to you, and to the strangers that sojourn among you, who have begotten children among you; and they shall be to you as born in the country among the sons of Israel; they shall have an inheritance with you among the tribes of Israel.
Za ku raba ta kamar gādo wa kanku da kuma wa baƙin da suka zauna a cikinku waɗanda suke da’ya’ya. Za ku ɗauka su kamar’yan ƙasa haifaffun Isra’ilawa; za su yi gādo tare da ku a cikin kabilan Isra’ila.
23 And it shall come to pass, that in what tribe the stranger sojourneth there shall ye appoint him his inheritance, saith the Lord Jehovah.
A duk kabilar da baƙon yake zama, a can za ku ba shi gādonsa,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.

< Ezekiel 47 >