< Ezekiel 43 >
1 Then he brought me to the gate, even to the gate that looketh toward the east.
Sai mutumin ya kawo ni ƙofar da take fuskantar gabas,
2 And behold, the glory of the God of Israel came from the east; and the sound thereof was as the sound of great waters, and the earth shone with his glory.
sai na ga ɗaukakar Allah na Isra’ila tana tahowa daga gabas. Muryarsa ta yi kamar rurin ruwaye masu gudu, ƙasa kuma ta haskaka da ɗaukakarsa.
3 And the appearance was like the vision which I saw, like the vision which I saw when I came to destroy the city; it was a vision like the vision which I saw at the river Chebar. And I fell upon my face.
Wahayin da na gani ya yi kamar wahayin da na gani sa’ad da ya zo don yă hallaka birnin, kamar kuma wahayin da na gani kusa da Kogin Kebar, na kuwa fāɗi rubda ciki.
4 And the glory of Jehovah came into the house by way of the gate, whose prospect was toward the east.
Ɗaukakar Ubangiji ta shiga haikali ta ƙofar da take fuskantar gabas.
5 Then the spirit took me up and brought me into the inner court; and behold, the glory of Jehovah filled the house.
Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama ya kawo ni cikin fili na can ciki, ɗaukakar Ubangiji kuwa ta cika haikalin.
6 And I heard one speaking to me out of the house, and a man was standing by me.
Yayinda mutumin yana tsaye kusa da ni, na ji wani yana magana da ni daga cikin haikalin.
7 And he said to me: Son of man, this is the place of my throne, and the place of the soles of my feet, where I will dwell in the midst of the sons of Israel forever; and the house of Israel shall no more pollute my holy name, neither they nor their kings, by their fornication, and by the dead bodies of their kings in their sepulchres;
Ya ce, “Ɗan mutum, wannan shi ne kursiyina da wurin tafin ƙafafuna. A nan ne zan zauna a cikin Isra’ilawa har abada. Gidan Isra’ila ba zai ƙara ɓata sunana mai tsarki ba, ko su ko sarakunansu, ta wurin karuwanci da gumakan da ba su da rai, sarakunansu a masujadan kan tudu.
8 in that they set their threshold by my threshold, and their post near my post, so that there was only a wall between me and them, and defiled my holy name by the abominations which they committed; wherefore I have consumed them in my anger.
Sa’ad da suka sa madogarar ƙofarsu kusa da madogarar ƙofata, da katanga kawai a tsakanina da su, sun ɓata sunana mai tsarki ta wurin ayyukansu masu banƙyama. Saboda haka na hallaka su cikin fushina.
9 Now let them remove far away from me their fornication, and the carcasses of their kings; and I will dwell in the midst of them forever.
Yanzu bari su kawar da karuwancinsu da gumakansu waɗanda ba su da rai na sarakunansu daga gabana, zan kuwa zauna a cikinsu har abada.
10 And thou, son of man, show this house to the house of Israel, that they may be ashamed of their iniquities, and that they may measure the pattern.
“Ɗan mutum, ka bayyana haikalin ga mutanen Isra’ila, don su ji kunya saboda zunubansu. Bari su yi la’akari da fasalin,
11 And if they be ashamed of all which they have done, let them know the form of the house and the fashion thereof, and the passages for going out and coming in, and all the forms thereof, and all the statutes thereof, and all the laws thereof, and write it in their sight, that they may keep the whole form thereof, and all the statutes thereof, and do them.
kuma in suka ji kunyar abubuwan da suka aikata, sai ka sanar musu fasalin haikalin da shirye-shiryensa, ƙofofinsa na shiga da fita, dukan fasalinsa da dukan ƙa’idodinsa da dokokinsa. Ka rubuta waɗannan a gabansu saboda su yi aminci da fasalinsa su kuma kiyaye dukan ƙa’idodinsa.
12 This is the law of the house. Upon the top of the mountain, all within its limits shall be most holy. Behold, this is the law of the house.
“Wannan ita ce dokar haikalin. Dukan filin da yake kewaye a kan dutsen, zai zama wuri mafi tsarki. Dokar haikalin ke nan.
13 And these are the measures of the altar by cubits; each cubit being a cubit and a hand-breadth. The bottom shall be a cubit high and a cubit broad; and the border thereof, by the edge thereof round about, shall be a span; and this shall be the outer part of the altar.
“Waɗannan su ne aune-aunen bagade a tsawon kamu, wannan kamu shi ne kamun tafin hannu. Zurfin magudanar ruwansa kamu ɗaya ne fāɗinsa kuma kamu ɗaya, tare da da’ira kamun tafi ɗaya kewaye da gefensa. Wannan kuma shi ne tsayin bagaden.
14 And from the bottom upon the ground to the lower ledge shall be two cubits, and the breadth one cubit; and from the lesser ledge to the greater ledge shall be four cubits, and the breadth a cubit.
Daga lambatun da yake a ƙasa har zuwa ƙaramin mahaɗin da yake ƙasa wanda ya kewaye bagade, tsayinsa kamu biyu ne, fāɗinsa kuma kamu guda. Daga ƙaramin mahaɗi zuwa babban mahaɗin wanda ya kewaye bagade, zai zama kamu huɗu, fāɗinsa kuwa kamu ɗaya.
15 And the altar shall be four cubits; and from the altar upward shall be four horns.
Murhun bagaden kamu huɗu ne, akwai ƙahoni guda huɗu sun miƙe sama daga murhun.
16 And the altar shall be twelve cubits long by twelve broad; square on the four sides thereof.
Murhun bagaden murabba’i ne, tsawonsa kamu goma sha biyu, fāɗinsa kuma kamu goma sha biyu.
17 And the ledge shall be fourteen cubits long by fourteen broad on the four sides thereof; and the border about it shall be half a cubit; and the bottom thereof shall be a cubit round about; and its steps shall look toward the east.
Gefen bisa ma murabba’i ne, tsawonsa kamu goma sha huɗu fāɗinsa kuma kamu goma huɗu, da da’ira da yake da fāɗin rabin kamu da magudanan ruwa kamu guda kewaye. Matakan bagaden suna fuskantar gabas.”
18 And he said to me, Son of man, thus saith the Lord Jehovah: These are the statutes of the altar, in the day when it is made, to offer burnt-offerings thereon, and to sprinkle blood thereon.
Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa waɗannan su ne za su zama ƙa’idodi don yin hadaya ta ƙonawa da yayyafawar jini a kan bagaden sa’ad da aka gina shi.
19 To the priests, the sons of Levi, of the race of Zadok, that come near to me, saith the Lord Jehovah, to minister to me, thou shalt give a young bullock for a sin-offering.
Za ka ba da ɗan bijimi a matsayin hadaya ta ƙonawa ga firistoci, waɗanda suke Lawiyawa, na iyalin Zadok, waɗanda suke zuwa kusa don hidima a gabana, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
20 And thou shalt take of the blood thereof, and put it on its four horns, and on the four corners of the ledge, and on the border round about, and thus cleanse and purge it.
Za ka ɗibi jininsa ka zuba shi a ƙahoni huɗu na bagaden a gefen bisa da kuma kewaye da da’irar, ta haka za ka tsarkake bagaden ka kuma yi kafara dominsa.
21 And thou shalt take the bullock of the sin-offering, and it shall be burned in the appointed place of the house, without the sanctuary.
Za ka ɗauki bijimi na hadaya don zunubi ka ƙone shi a sashen da aka shirya na haikalin a wani wuri waje da wuri mai tsarki.
22 And on the second day thou shalt offer a he-goat without blemish for a sin-offering; and they shall cleanse the altar, as they cleansed it with the bullock.
“A rana ta biyu za ka miƙa bunsuru marar lahani domin hadaya don zunubi, za a kuma tsarkake bagaden yadda aka yi da bijimin.
23 And when thou hast made an end of cleansing it, thou shalt offer a young bullock without blemish, and a ram out of the flock without blemish.
Sa’ad da ka gama tsarkake shi, sai ka miƙa ɗan bijimi da kuma rago daga cikin garke, dukansu marasa lahani.
24 And thou shalt offer them before Jehovah, and the priests shall cast salt upon them, and offer them up for a burnt-offering to Jehovah.
Za ka miƙa su a gaban Ubangiji, firistoci kuma za su barbaɗe gishiri a kansu su kuma miƙa su kamar hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji.
25 Seven days shalt thou sacrifice daily a goat for a sin-offering; they shall also sacrifice a young bullock, and a ram out of the flock without blemish.
“Kwana bakwai za ka tanada bunsuru kullum domin hadaya don zunubi; za ka kuma tanada ɗan bijimi da rago daga garke, dukansu marasa lahani.
26 Seven days shall they purge the altar, and purify it, and consecrate themselves.
Kwana bakwai za su yi kafara saboda bagaden su kuma tsarkake shi; ta haka za su keɓe shi.
27 And when they have finished these days, it shall be that on the eighth day and forward the priests shall present your burnt-offerings and your thank-offerings upon the altar, and I will accept you, saith the Lord Jehovah.
A ƙarshen waɗannan kwanaki, daga rana ta takwas zuwa gaba, firistoci za su miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama a kan bagade. Sa’an nan zan karɓe ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”