< Ezekiel 22 >
1 And the word of Jehovah came to me, saying:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Punish, punish, son of man, the city of blood, and show her all her abominations, and say,
“Ɗan mutum, za ka shari’anta ta? Za ka shari’anta wannan birni mai kisankai? To, sai ka kalubalance ta da dukan ayyukanta na banƙyama
3 Thus saith the Lord Jehovah: O city that sheddest blood in the midst of thee, that thy time may come, and makest idols to defile thyself!
ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce ya birnin da take kawo wa kansa hallaka ta wurin kisankai a cikinta kina kuma ƙazantar da kanki ta wurin yin gumaka,
4 Through the blood which thou sheddest thou bringest guilt upon thyself, and through the idols which thou makest thou pollutest thyself, and thou causest thy days to draw near, and comest to thy years. Therefore do I make thee a reproach to the nations, and a derision to all countries.
kin zama mai laifi saboda jinin da kika zubar kika kuma zama ƙazantacciya ta wurin gumakan da kika yi. Kin kawo kwanakinki ga ƙarshe, kuma ƙarshen shekarunki sun zo. Saboda haka zan mai da ke abar ba’a ga al’ummai da abin dariya ga dukan ƙasashe.
5 Those that are near, and those that are far from thee, shall mock thee as infamous, full of confusion.
Waɗanda suke kusa da waɗanda suke nesa za su yi miki ba’a, ya ke birni marar kunya, cike da rigima.
6 Behold the princes of Israel are engaged every one according to his strength within thee to shed blood.
“‘Duba yadda kowane yerima Isra’ila waɗanda suke cikinki yake yin amfani da ikonsa yana kisankai.
7 In thee they set light by father and mother; in thee are they guilty of oppression to the stranger; in thee do they oppress the fatherless and the widow.
A cikinki sun rena mahaifi da mahaifiya; a cikinki sun zalunci baƙo suka wulaƙanta maraya da gwauruwa.
8 Thou hast despised my holy things, and profaned my sabbaths.
Kin rena abubuwana masu tsarki kika kuma ƙazantar da Asabbataina.
9 In thee are men who carry tales, that they may shed blood; in thee do they eat upon the mountains; in the midst of thee do they commit lewdness.
A cikinki akwai mutane waɗanda suka nace su yi kisankai; a cikinki akwai waɗanda suke ci a dutsen tsafi suna yin ayyukan lalata.
10 In thee doth the son uncover the father's nakedness; in thee do they lie with a woman in her uncleanness.
A cikinki akwai waɗanda suke kwana da matan mahaifansu; a cikinki akwai waɗanda suke kwana da mata a lokacin da suke al’adarsu, sa’ad da suke da rashin tsarki.
11 And one committeth abomination with his neighbor's wife; and another, with incestuous lewdness, defileth his daughter-in-law; and in thee another lieth with his sister, his father's daughter.
A cikinki mutum guda yakan yi laifi abin ƙyama da matar maƙwabcinsa, wani cikin rashin kunya ya ƙazantar da matar ɗansa, wani kuma ya kwana da’yar’uwansa,’yar mahaifinsa.
12 In thee do they take a reward to shed blood. Thou takest usury and increase, and thou hast enriched thyself from thy neighbor by extortion, and hast forgotten me, saith the Lord Jehovah.
A cikinki mutane suna karɓan cin hanci don su yi kisankai; kina ba da rance da ruwa da ƙari, kina kuma cin riba a kan maƙwabcinki ta wurin ƙwace. Kina kuma manta da ni, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
13 Therefore, behold, I have smitten my hands together at thy dishonest gain which thou hast made, and at the blood which hath been shed in the midst of thee.
“‘Tabbatacce zan tafa hannuwana a kan ƙazamar riba da kika ci da jinin da kin zubar a cikinki.
14 Can thy heart endure, or can thy hands be strong, in the day when I shall deal with thee? I, Jehovah, have spoken it, and will do it.
Ƙarfin halinki zai jure ko kuwa hannuwanki za su yi ƙarfi a ranar da na gamu da ke? Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata.
15 I will scatter thee among the nations, and disperse thee in the countries, and will consume thine impurity out of thee;
Zan watsar da ke cikin al’ummai in warwatsa ke cikin ƙasashe; zan kuma kawo ƙarshen rashin tsarkinki.
16 and thou shalt through thyself be profaned before the eyes of the nations, and thou shalt know that I am Jehovah.
Sa’ad da ki ƙazantu a idanun al’umma, za ki san cewa ni ne Ubangiji.’”
17 And the word of Jehovah came to me, saying:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
18 Son of man, the house of Israel is become dross to me; all of them are brass, and tin, and iron, and lead, in the midst of the furnace; they are the dross of silver.
“Ɗan mutum, gidan Isra’ila ta zama ƙwan maƙera a gare ni; dukansu tagulla ne, kuza, ƙarfe da darma da suka rage a tanderu. Su ƙwan maƙerar azurfa ne kawai.
19 Therefore thus saith the Lord Jehovah: Because ye are all of you become dross, therefore, behold, I will gather you into the midst of Jerusalem.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin ku duka kun zama ƙwan maƙera, zan tattara ku a Urushalima.
20 As men gather silver, and brass, and iron, and lead, and tin, into the midst of the furnace, to blow the fire upon it, to melt it, so will I gather you in my anger and in my fury, and I will place you there and melt you.
Kamar yadda mutane sukan tattara azurfa, tagulla, ƙarfe, darma da kuza a cikin tanderu don su narkar da su da wuta, haka zan tattara ku cikin fushina da kuma hasalata in sa ku cikin birnin in narkar da ku.
21 Yea, I will gather you, and blow upon you with the fire of my wrath, and ye shall be melted in the midst thereof.
Zan tattara ku zan kuma hura muku wutar hasalata, za ku kuma narke a cikinta.
22 As silver is melted in the midst of the furnace, so shall ye be melted in the midst thereof; and ye shall know that I, Jehovah, have poured out my fury upon you.
Kamar yadda azurfa kan narke a tanderu, haka za ku narke a cikinta, kuma za ku san cewa Ni Ubangiji na zubo muku da zafin fushina.’”
23 And the word of Jehovah came to me, saying:
Har yanzu maganar Ubangiji ta zo gare ni cewa,
24 Son of man, say to her, Thou art a land that is not cleansed, nor rained upon in the day of indignation.
“Ɗan mutum, ka faɗa wa ƙasar, ‘Ke ƙasa ce marar ruwan sama ko yayyafi a ranar hasala.’
25 There is a conspiracy of her prophets in the midst of her; like a roaring lion tearing the prey, they devour the lives of men; they take possession of treasures, and precious things, and make many widows in the midst of her.
Akwai haɗin bakin sarakunanki a cikinki kamar rurin zaki mai yayyage ganimarsa; suna cin mutane, suna kwashe dukiya da abubuwa masu daraja suna mai da yawanci gwauraye a cikinki.
26 Her priests violate my law, and profane my holy things. They make no distinction between the holy and profane, and show not the difference between the clean and the unclean; and they hide their eyes from my sabbaths, and I am profaned among them.
Firistocinki suna karya dokokina, sun ƙazantar da tsarkakan abubuwana; ba sa bambanta tsakanin tsarki da marar tsarki; suna koyarwa cewa babu bambanci tsakanin marar tsarki da mai tsarki; suna kuma rufe idanunsu ga kiyaye Asabbataina, da haka suke saɓon sunana.
27 Her princes in the midst of her are like wolves tearing the prey. They shed blood, they destroy life, that they may get gain.
Shugabanninki a cikinki suna kama da kyarketai masu yayyage ganimarsu; suna kisa suna kuma kashe mutane don samun ƙazamar riba.
28 Her prophets daub for them with untempered mortar, seeing falsehood, and divining to them, saying, “Thus saith the Lord Jehovah,” when Jehovah hath not spoken.
Annabawanki sun yi wa waɗannan ayyuka shafe da farar ƙasa ta wurin wahayin ƙarya da duban ƙarya. Suna cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa’ alhali kuwa Ubangiji bai faɗa ba.
29 The people of the land are guilty of oppression, and practise robbery, and distress the poor and needy; yea, they oppress the stranger, and have no justice.
Mutanen ƙasar na yin ƙwace suna yin fashi; suna cin zalin matalauta da mabukata suna wulaƙanta baƙo suna hana musu adalci.
30 I have sought for a man among them that should make a wall, and stand in the gap before me for the land, that I might not destroy it; but I found none.
“Na nemi mutum guda a cikinsu wanda zai gina katanga ya tsaya a gabana a tsakani a madadin ƙasar don kada in hallaka ta, amma ban sami ko ɗaya ba.
31 Therefore will I pour out my indignation upon them; I will consume them with the fire of my wrath; I will bring their way upon their heads, saith the Lord Jehovah.
Saboda haka zan zuba hasalata a kansu in cinye su da wutar fushina, ina ɗora alhakin ayyukansu a bisa kawunansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”