< Ezekiel 21 >

1 Then came the word of Jehovah to me, saying:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Son of man, set thy face toward Jerusalem, and drop thy word toward the holy places, and prophesy against the land of Israel,
“Ɗan mutum, ka kafa fuskarka gāba da Urushalima ka kuma yi wa’azi a kan wuri mai tsarki. Ka yi annabci gāba da ƙasar Isra’ila
3 and say to the land of Israel, Thus saith Jehovah: Behold, I am against thee, and I will draw forth my sword out of its sheath, and will cut off from thee the righteous and the wicked.
ka faɗa mata, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce ina gāba da ke. Zan ja takobina daga kubensa in karkashe adalai da mugaye daga cikinki.
4 Seeing then that I cut off from thee the righteous and the wicked, therefore shall my sword go forth out of its sheath against all flesh from the south to the north.
Domin zan karkashe adalai da kuma mugaye, ba zan rufe takobina a kan kowa daga kudu zuwa arewa ba.
5 And all flesh shall know that I, Jehovah, have drawn forth my sword out of its sheath; it shall not return any more.
Sa’an nan duka mutane za su san cewa Ni Ubangiji na ja takobina daga kubensa; ba zai sāke koma kuma ba.’
6 Thou, therefore, O son of man, sigh! With the breaking of thy loins, and with bitterness, sigh before their eyes!
“Saboda ka yi nishi, ɗan mutum! Yi nishi a gabansu da ajiyar zuciya da ɓacin rai.
7 And when they shall say to thee, “Wherefore sighest thou?” thou shalt say, “For the rumor, because it cometh; and every heart shall melt, and all hands shall be feeble, and every spirit shall fail, and all knees shall flow with water. Behold it cometh, it shall be brought to pass, saith the Lord Jehovah.”
Kuma sa’ad da suka tambaye ka, ‘Me ya sa kake nishi?’ Sai ka ce musu, ‘Domin labarun da suke fitowa. Kowace zuciya za tă narke kowane hannu kuma ya gurgunta; kowane ruhu zai sume kowane gwiwa kuma ta rasa ƙarfi kamar ruwa.’ Yana zuwa! Tabbatacce zai faru, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
8 Also the word of Jehovah came to me, saying:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
9 Son of man, prophesy, and say, Thus saith Jehovah: Say, The sword, the sword is sharpened and furbished.
“Ɗan mutum, yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji ya faɗa, “‘Takobi, takobi, wasasshe da kuma gogagge,
10 It is sharpened, that it may make sore slaughter; it is furbished that it may glitter. Or shall we make mirth? The staff of my son despiseth every rod.
wasasshe don kisa, gogagge har yana walwal kamar walƙiya! “‘Kada ku yi farin ciki, hukunci yana zuwa, domin kowa ya ƙi jin abin da na yi gargaɗi a kai.
11 And he gave it to be furbished that it might be handled. The sword is sharpened and furbished, to be given into the hand of the slayer.
“‘An ba da wannan takobi don a goge, don a kama da hannu; an washe shi aka kuma goge, shiryayye don a yi kisa da shi.
12 Cry and howl, son of man! for it cometh upon my people, upon all the princes of Israel. They are given up to the sword with my people. Therefore smite upon thy thigh.
Ka yi kuka ka yi makoki, ɗan mutum, gama yana gāba da dukan sarakunan Isra’ila. An jefa su ga takobi tare da jama’ata. Saboda haka ku buga ƙirjinku.
13 The trial is made. And what if even the contemning staff should be no more? saith the Lord Jehovah.
“‘Gwaji tabbatacce zai zo. Kuma a ce sandan Yahuda, wanda takobi ya ƙi, ya ci gaba? In ji Ubangiji Mai Iko Duka.’
14 Thou, therefore, son of man, prophesy, and smite thine hands together! for twice, yea thrice, cometh the sword, a sword of slaughter, a sword of great slaughter, that besetteth them on every side.
“Saboda haka fa, ɗan mutum ka yi annabci ka kuma tafa hannuwanka. Bari takobi ya yi sara sau biyu, har sau uku ma. Takobin kisa ne, takobi ne don kisa mai girma, zai kewaye su a kowane gefe.
15 That their hearts may faint, and their overthrown may be multiplied, I have set the terror of the sword against all their gates. Ah, how is it made to glitter, polished for slaughter!
Domin zukata su narke da yawa kuma su fāɗi, na tsai da takobin kisa a dukan ƙofofinsu. Kash! A sa ya haska kamar walƙiya, ana riƙe da shi don kisa.
16 Unite thyself, smite to the right, prepare thyself, smite to the left, whithersoever thine edge is turned!
Ya takobi, yi sara zuwa dama ka yi kuma zuwa hagu, duk inda aka juya ka.
17 I also will smite my hands together, and cause mine anger to cease. I, Jehovah, have spoken it.
Zan tafa hannuwana, fushina kuwa zai sauka. Ni Ubangiji na faɗa.”
18 The word of Jehovah came to me again, saying:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
19 Do thou, son of man, appoint thee two ways by which the sword of the king of Babylon may come; from one land shall both of them come; and choose thou a place, choose it at the head of the way to the city.
“Ɗan mutum, ka nuna hanyoyi biyu inda takobin sarkin Babilon zai bi, duka biyun su fara daga ƙasa guda. Ka kafa shaida inda hanyar za tă rabu zuwa cikin birni.
20 Appoint a way, that the sword may come towards Rabbath of the sons of Ammon, and towards Judah, to Jerusalem, the fenced city.
Ka nuna hanya guda wadda takobi zai fāɗo wa Rabba ta Ammonawa ɗayan kuma da zai fāɗo a kan Yahuda da kuma Urushalima mai katanga.
21 For the king of Babylon shall stand at the parting of the way, at the head of the two ways, to use divination; he shall shake together his arrows, he shall consult the teraphim, he shall look at the liver.
Gama sarkin Babilon zai tsaya a mararrabar hanya, a inda hanyar ta rabu biyu, don yă yi duba. Zai jefa ƙuri’a da kibiyoyinsa, zai nemi shawarar gumakansa, zai bincike hanta.
22 In his right hand shall be the lot: Jerusalem, to set battering-rams, to open the mouth with the war-cry, to lift up the voice in shouting, to set battering-rams against the gates, to cast up a mound, to build a tower.
A hannunsa na dama ƙuri’a don Urushalima za tă fito, inda zai kafa dundurusai, ya ba da umarni kisa, a yi kururuwar yaƙi, a kafa dundurusai a kan ƙofofi, a gina mahaurai a kuma yi ƙawanya.
23 And this shall appear a false divination in their sight, because they swore oaths to them. But he shall call to remembrance their iniquity, that they may be taken.
Zai zama kamar duban ƙarya ne ga waɗanda suka yi rantsuwar yin masa biyayya, amma zai tunashe su game da laifinsu ya kuma kama su.
24 Therefore thus saith the Lord Jehovah: Because ye make your iniquity to be remembered, in that your transgressions are discovered, so that in all your doings your sins do appear, —because, I say, ye bring yourselves into remembrance, ye shall be taken with that hand.
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin ku mutanen nan kun tuna da laifinku ta wurin tawaye, kun kuma bayyana zunubanku cikin dukan abin da kuke yi, domin kun yi haka, za a kama ku.
25 And thou, profane, wicked prince of Israel, whose day cometh in the time when iniquity bringeth destruction!
“‘Ya kai ƙazantaccen mugu, yerima Isra’ila, wanda kwanansa ta zo, wanda lokacin hukuncinsa ya cika fal,
26 Thus saith the Lord Jehovah: I will remove the diadem, and take away the crown! This shall no more be this. I exalt him that is low, and abase him that is high.
ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ka kunce rawanin, ka ɗauke rawanin nan. Ba zai zama kamar yadda yake ba. Za a ɗaukaka ƙasƙantacce, amma a ƙasƙantar da mai girma.
27 I will destroy, destroy, destroy it; and it shall be no more until he come to whom the right belongeth, and to whom I will give it.
Hallaka! Hallaka! Zan hallaka shi! Ba za a maido da shi ba sai ya ga ainihin mai shi; gare shi zan bayar da shi.’
28 And thou, son of man, prophesy, and say: Thus saith the Lord Jehovah concerning the sons of Ammon and their scorn; even say thou, The sword, the sword is drawn; to slay, to consume, is it furbished, so that it glittereth;
“Kai kuma, ɗan mutum, ka yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa game da Ammonawa da kuma zarginsu. “‘Takobi, takobi, an ja don kisa, an goge don cinyewa yana haske kamar walƙiya!
29 while they see deceit for thee, and prophesy falsehood, that it may bring thee to the necks of the wicked that are slain, whose day cometh in the time when iniquity bringeth destruction.
Duk da wahayin ƙarya game da kai, duban ƙarya game da kai, za a sa shi a wuyan mugaye waɗanda za a kashe, waɗanda kwanansu ta zo, waɗanda lokacin hukuncinsu ya cika fal.
30 Return the sword into its sheath! In the place where thou wast created, in the land of thy nativity, I will judge thee,
“‘Ka mai da takobi a kubensa. A inda aka halicce ka, a ƙasar kakanninka, zan hukunta ka.
31 and I will pour upon thee my indignation, I will blow upon thee in the fire of my wrath, and deliver thee into the hands of brutal men, skilful to destroy.
Zan zub da hasalata a kanka in hura maka wutar fushina; Zan ba da kai a hannun mugayen mutanen da suka gwanince a hallakarwa.
32 Thou shalt be fuel for the fire; thy blood shall be in the midst of the land; men shall no more remember thee. I, Jehovah, have spoken it.
Za ka zama itacen wuta, za a zub da jininka a ƙasarka, ba za a ƙara tuna da kai ba; gama Ni Ubangiji na faɗa.’”

< Ezekiel 21 >