< Daniel 8 >

1 In the third year of the reign of King Belshazzar, a vision appeared to me, to me, Daniel, after that which appeared to me at the first.
A shekara ta uku ta mulkin sarki Belshazar, ni, Daniyel, na ga wahayi, bayan wancan da na riga gani.
2 And I saw in a vision, and when I saw, I was in Shushan, in the palace, which is in the province of Elam; and I saw in a vision, and was by the river Ulai.
A cikin wahayin, na ga kaina a mafakar Shusha a yankin Elam; a wahayin na ga ina a bakin Kogin Ulai.
3 And I lifted up my eyes and saw, and behold, there stood before the river a ram, which had two horns; and the two horns were high, and one was higher than the other; and the higher came up last.
Na ɗaga ido, a gabana kuwa sai ga rago mai ƙahoni biyu, yana tsaye a gefen mashigin kogin, ƙahonin kuma suna da tsawo. Ɗaya daga cikin ƙahonin ya fi ɗayan tsawo. Wanda ya fi tsawon shi ne ya tsiro daga baya.
4 I saw the ram pushing westward and northward and southward, and no beast could stand before him, and none could deliver out of his hand; but he did according to his will and became great.
Na lura da ragon sa’ad da ya kai karo wajen yamma da arewa da kudu. Babu wata dabbar da ta iya ƙarawa da shi, babu kuma wanda ya iya kuɓuta daga ikonsa. Ya yi yadda ya ga dama, ya kuma zama mai girma.
5 And I gave heed, and behold, a he-goat came from the west, over the face of the whole earth, without touching the ground; and the goat had a conspicuous horn between his eyes.
Yayinda nake tunani game da wannan, farat ɗaya sai ga bunsurun da yake da sanannen ƙaho tsakanin idanunsa ya ɓullo daga wajen yamma, yana ratsa dukan duniya ba ya ko taɓa ƙasa.
6 And he came to the ram which had two horns, which I had seen standing before the river, and ran against him in the fury of his power.
Ya zo wajen rago mai ƙahoni biyu ɗin nan da na riga na gani tsaye a gefen mashigin kogin nan ya tasar masa da fushi mai zafi.
7 And I saw him come close to the ram, and he was enraged against him, and smote the ram, and broke in pieces his two horns; and there was no power in the ram to stand before him; and he cast him down to the ground, and stamped upon him; and none could deliver the ram out of his hand.
Na ga ya zo kusa da ragon, ya husata da shi ƙwarai, ya kai wa ragon hari. Ya kakkarya ƙahoninsa nan biyu. Ƙarfin ragon ya kāsa, bai iya kāre kansa daga bunsurun ba. Bunsurun ya buge shi ƙasa ya tattake shi. Ba wanda ya iya ceton ragon daga bunsurun.
8 And the he-goat became exceedingly great; but when he became strong the great horn was broken, and instead of it grew up four conspicuous ones toward the four winds of heaven.
Bunsurun kuwa ya ƙasaita, amma a ƙwanƙolin ikonsa sai aka karye babban ƙahonsa, kuma a wurin da ƙahon nan ya kasance waɗansu sanannun ƙahoni huɗu suka tsiro suna fuskantar kusurwoyin nan huɗu.
9 And out of one of them came forth a little horn, which became exceedingly great toward the south, and toward the east, and toward the beautiful land.
Daga cikin ɗayansu kuma wani ƙaramin ƙaho ya fito, ya yi girma ya ƙasaita ƙwarai zuwa kudu da kuma gabas da wajen Kyakkyawar Ƙasa.
10 And it exalted itself even to the host of heaven, and some of the host and of the stars it cast down to the ground, and stamped upon them.
Ya yi girma sai da ya kai rundunar sammai, ya kuma fid da waɗansu rundunar taurari zuwa ƙasa ya kuma tattake su.
11 Yea, he magnified himself even to the Prince of the host, and the daily sacrifice did he take away from him, and the place of his sanctuary was cast down.
Sai ya ɗora kansa ya zama mai girma kamar Sarkin runduna; sai aka ɗauke hadaya ta kullayaumi daga gare shi, aka kuma saukar da wurin masujadarsa ƙasa.
12 And a host was placed over the daily sacrifice with impiety, and it cast down truth to the ground, and it accomplished its purpose and prospered.
Saboda tawaye, sai aka ba da rundunar tsarkaka da kuma hadayar ƙonawa ta kowace rana ga ƙahon. Sai ya yi watsi da gaskiya, ya yi abin da ya ga dama, ya kuwa yi nasara.
13 And I heard a holy one speak; and another holy one said to the one that had spoken, To how long a time extendeth the vision concerning the daily sacrifice, and the impiety of the destroyer, to give both the sanctuary and the host to be trodden under foot?
Sa’an nan na ji mai tsarkin nan yana magana, wani mai tsarki kuma ya ce da wancan, “Har yaushe wannan wahayi zai tabbata, wahayi game da hadaya ta kullayaumi, da tawayen da yake kawo lalacewa, da kuma miƙa wuri mai tsarki da kuma na rundunar da za a tattake a ƙarƙashin sawu?”
14 And he said to me, To two thousand and three hundred evenings and mornings; then shall the sanctuary be cleansed.
Sai ya ce mini, “Zai ɗauki safiya da yamma 2,300; sa’an nan za a sāke tsarkake wuri mai tsarki.”
15 And it came to pass, that when I Daniel saw the vision, I sought for the meaning; and behold, there stood one before me having the appearance of a man.
Yayinda ni, Daniyel, nake duban wahayi ina ƙoƙari in fahimce shi, sai ga wani a gabana wanda ya yi kama da mutum.
16 And I heard a man's voice between the banks of Ulai, which called and said, Gabriel, make this man to understand the vision.
Sai na ji muryar wani mutum daga Ulai tana cewa, “Jibra’ilu, faɗa wa wannan mutum ma’anar wahayin.”
17 And he came near where I stood; and when he came, I was afraid, and fell upon my face, and he said to me, Understand, O son of man! for this vision relateth to the time of the end.
Da ya zo kusa da inda nake tsaye, na firgita na kuma fāɗi rubda ciki. Ya ce da ni “Ɗan mutum, ka gane da cewa wannan wahayi yana magana ne a kan kwanakin ƙarshe.”
18 But when he spake to me, I sank senseless upon my face to the ground; but he touched me, and lifted me up where I had stood.
Yayinda yake magana da ni, barci mai nauyi ya kwashe ni, da nake kwance rubda ciki. Sai ya taɓa ni ya kuma tashe ni tsaye.
19 And he said, Behold, I make known to thee what shall be in the latter time of the indignation; for [[the vision relateth]] to the time of the end.
Sai ya ce, “Zan faɗa maka abin da zai faru a lokacin fushi, saboda wahayin yana magana ne a kan lokacin da aka ƙayyade na ƙarshe.
20 The ram which thou sawest, having two horns, denoteth the kings of Media and Persia.
Rago mai ƙahoni biyu da ka gani, yana a madadin sarakunan Medes da Farisa ne.
21 And the rough goat is the king of Greece; and the great horn between his eyes is the first king.
Bunsurun kuwa sarkin Girka ne, kuma babban ƙahon da yake tsakanin idanunsa, sarki na farko ne.
22 And as that was broken, and four arose in its place, four kingdoms shall arise out of the nation, but not with his power.
Ƙahoni huɗu da suka maya wannan da ya karye yana a madadin masarautu huɗu da za su tashi daga cikin al’ummarsa amma ba za su sami irin ikonsa ba.
23 And toward the end of their reign, when the transgressors have filled up the measure of their iniquities, a king shall arise of a fierce countenance, and cunning in artifices.
“Can wajen ƙarshe mulkinsu, sa’ad da muguntarsu ta kai intaha, wani mugun sarki mai rashin hankali, uban makirci, zai fito.
24 And his power shall become mighty, but not by his own strength; and wonderfully will he destroy, and prosper, and accomplish his purposes, and he will destroy many, even the people of the holy ones.
Zai yi ƙarfi ƙwarai da gaske, amma ba da ikonsa ba. Zai jawo mummunar hallakarwa kuma zai yi nasara a duk abin da ya sa gaba. Zai hallakar da majiya ƙarfi da kuma tsarkaka.
25 And through his cunning will he cause fraud to prosper in his hand, and he will magnify himself in his heart, and he will destroy many in the midst of security, and against the Prince of princes will he stand up; but he shall be broken without hand.
Zai sa yaudara ta ƙara yin yawa, zai ɗaukaka kansa. Sa’ad da suke ji sun sami mafaka, zai hallaka mutane da yawa sa’an nan kuma yă fara gāba da Sarkin sarakuna. Duk da haka za a hallaka shi, amma ba da ikon mutum ba.
26 And the vision of the evening and the morning, which was told thee, is true; but do thou seal up the vision, for it relates to many days.
“Wahayin nan na safiya da yamma da aka nuna maka gaskiya ne, amma ka ɓoye wahayin, gama ya shafi nan gaba mai tsawo ne.”
27 And I Daniel fainted, and was sick some days; then I rose up and did the king's business; and I was astonished at the vision, but no one explained it.
Ni, Daniyel, na gaji matuƙa na kuma yi rashin lafiya na kwanaki masu yawa. Sa’an nan sai na tashi na ci gaba da hidimar sarki. Wahayin ya shige mini duhu, ya fi ƙarfin fahimtata.

< Daniel 8 >