< Amos 1 >

1 The words of Amos, one of the shepherds of Tekoa, which he prophesied concerning Israel in the days of Uzziah king of Judah, and in the days of Jeroboam, the son of Joash, king of Israel, two years before the earth quake. He said: —
Kalmomin Amos, ɗaya daga cikin makiyayan Tekowa, abubuwan da ya gani game da Isra’ila shekaru biyu kafin a yi girgizar ƙasa, a lokacin da Uzziya yake sarkin Yahuda, Yerobowam ɗan Yowash kuma yake sarkin Isra’ila.
2 Jehovah will roar from Zion, And utter his voice from Jerusalem; The habitations of the shepherds shall mourn, And the top of Carmel shall wither.
Ya ce, “Ubangiji ya yi ruri daga Sihiyona ya kuma yi tsawa daga Urushalima; wuraren kiwo duk sun bushe, dutsen Karmel kuma ya yi yaushi.”
3 Thus saith Jehovah; For three transgressions of Damascus, And for four, will I not turn away its punishment; For they thrashed Gilead with thrashing-wains of iron.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Damaskus, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Domin sun ci zalunci Gileyad zalunci mai tsanani,
4 I will send a fire upon the house of Hazael, Which shall devour the palaces of Benhadad.
zan sa wuta a gidan Hazayel, da za tă ƙona kagarun Ben-Hadad.
5 I will also break the bar of Damascus, And I will destroy the inhabitant from the valley of Aven, And him that holdeth the sceptre from Beth-Eden, And the people of Syria shall be led captive to Kir: Jehovah hath said it.
Zan kakkarye ƙofofin Bet-Damaskus; zan hallaka sarkin da yake cikin Kwarin Awen da kuma mai riƙe da sandar mulkin Bet-Eden. Mutanen Aram za su je bauta a ƙasar Kir,” in ji Ubangiji.
6 Thus saith Jehovah: For three transgressions of Gaza, And for four, I will not turn away its punishment; For they led captive all that fell into their hands, And delivered them up to Edom.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Gaza, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun kwashe al’umma gaba ɗaya sun sayar wa Edom,
7 But I will send a fire upon the wall of Gaza, Which shall devour her palaces.
Zan aika da wuta a katangar Gaza ta ƙone duk kagarunta.
8 And I will destroy the inhabitant from Ashdod, And him that holdeth the sceptre from Ashkelon; And I will turn my hand against Ekron, And the residue of the Philistines shall perish. The Lord, Jehovah, hath said it.
Zan hallaka sarkin Ashdod da kuma mai riƙe da sandar mulki na Ashkelon. Zan hukunta Ekron, har sai dukan Filistiyawa sun mutu,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
9 Thus saith Jehovah: For three transgressions of Tyre, And for four, will I not turn away its punishment; Because they delivered up all their captives to Edom, And remembered not the brotherly covenant.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Taya, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun kwashe al’umma gaba ɗaya sun kai su bauta a Edom, ba su kula da yarjejjeniyar da aka yi ta zama kamar’yan’uwa ba,
10 But I will send a fire on the wall of Tyre, Which shall devour her palaces.
zan aika da wuta a Taya, da za tă ƙone kagarunta.”
11 Thus saith Jehovah: For three transgressions of Edom, And for four, will I not turn away his punishment; For he pursued his brother with the sword, And cast off all pity, And his anger tore perpetually; Yea, he kept his wrath forever.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Edom, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta shi ba. Don ya fafari ɗan’uwansa da takobi, babu tausayi, domin ya ci gaba da fusata bai yarda yă huce daga fushinsa ba.
12 But I will send a fire upon Teman. Which shall devour the palaces of Bozrah.
Zan aika wuta a Teman da za tă ƙone kagarun Bozra.”
13 Thus saith Jehovah: For three transgressions of the children of Ammon, And for four, will I not turn away their punishment; For they ripped up the women with child of Gilead, That they might enlarge their border.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Ammon, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta shi ba. Don ya tsaga cikin matan Gileyad masu juna biyu don kawai yă ƙwace ƙasar.
14 But I will kindle a fire on the wall of Rabbah, Which shall devour her palaces, Amid the war-shout in the day of battle, In a whirlwind in the day of the storm.
Zan sa wuta a katangar Rabba da za tă ƙone kagarunta za a yi kururuwa a ranar yaƙi, faɗan kuwa zai yi rugugi kamar hadiri.
15 Their king shall go into captivity, He and his princes together, saith Jehovah.
Sarkinta zai je bauta, shi da ma’aikatansa,” in ji Ubangiji.

< Amos 1 >