< Acts 9 >

1 But Saul, yet breathing out threatening and slaughter against the disciples of the Lord, went to the high priest,
Amma Shawulu, ya cigaba da maganganun tsoratarwa har ma da na kisa ga almajiran Ubangiji, ya tafi wurin babban firist
2 and asked of him letters to Damascus to the synagogues, that if he found any who were of this way of belief, whether they were men or women, he might bring them bound to Jerusalem.
kuma ya roke shi wasiku zuwaga majami'un da ke Dimashku, domin idan ya sami wani da ke na wannan hanya, maza ko mata, ya kawo su Urushalima a daure.
3 And as he journeyed, he came near Damascus; and suddenly there shone around a him a light from heaven;
Yayin da yana tafiya, ya kasance da ya iso kusa da Dimashku, nan da nan sai ga wani haske daga sama ya haskaka kewaye da shi;
4 and he fell to the earth, and heard a voice saying to him, Saul, Saul, why persecutest thou me?
Sai ya fadi a kasa kuma yaji wata murya na ce da shi, ''Shawulu, Shawulu, me yasa kake tsananta mani?''
5 And he said, Who art thou, Lord? And he answered, I am Jesus whom thou persecutest.
Shawulu ya amsa, ''Wanene kai, Ubangiji?'' Ubangiji ya ce, ''Nine Yesu wanda kake tsanantawa;
6 But arise, and go into the city, and it shall be told thee what thou must do.
amma ka tashi, ka shiga cikin birnin, kuma za a gaya maka abinda lallai ne kayi.
7 And the men that journeyed with him stood speechless, hearing the voice, but seeing no one.
Mutanen da ke tafiya tare da Shawulu suka tsaya shiru sun rasa abin fada, suna sauraron muryar, amma ba su ga kowa ba.
8 And Saul arose from the earth; but when his eyes were opened, he saw nothing; and they led him by the hand, and brought him into Damascus.
Shawulu ya tashi daga kasa, kuma daga ya bude idanunsa, baya ganin komai; sai suka kama hannuwansa suka yi masa jagora suka kawo shi cikin birnin Dimashku.
9 And he was three days without sight, and neither ate nor drank.
Har kwana uku ba ya kallo, kuma ba ya ci balle sha.
10 And there was a certain disciple at Damascus, named Ananias, and to him the Lord said in a vision, Ananias! And he said, Behold, I am here, Lord.
Akwai wani almajiri a Dimashku mai suna Hananiya; sai Ubangiji ya yi magana da shi cikin wahayi, ya ce, ''Hananiya.'' Sai ya ce, ''Duba, gani nan Ubangiji.''
11 And the Lord said to him, Arise, and go into the street called Straight, and inquire in the house of Judas for one called Saul, of Tarsus; for lo! he prayeth,
Ubangiji ya ce masa, ''Tashi, ka tafi titin da ake kira Mikakke, kuma a gidan wani mai suna Yahuza ka tambaya mutum daga Tarsus mai suna Shawulu; gama yana addu'a;
12 and hath seen a man, named Ananias, coming in and putting his hand on him, that he might receive sight.
kuma ya gani cikin wahayi mutum mai suna Hananiya na shigowa kuma ya daura masa hannu, domin idanunsa su bude.''
13 But Ananias answered, Lord, I have heard from many about this man, how great evils he hath done to thy saints at Jerusalem.
Amma Hananiya ya amsa, ''Ubangiji, na ji labari daga wurin mutane da yawa game da mutumin nan, da irin muguntar da ya aikata ga tsarkakan mutanenka da ke Urushalima.
14 And here he hath authority from the chief priests to bind all that call on thy name.
An bashi izini daga babban firist domin ya kama dukan wanda ke kira bisa sunanka.''
15 But the Lord said to him, Go; for this man is to me a chosen vessel, to bear my name before nations, and kings, and the sons of Israel.
Amma Ubangiji ya ce masa, ''Jeka, gama shi zababben kayan aiki na ne, wanda zai yada sunana ga al'ummai da sarakuna da 'ya'yan Isra'ila;
16 For I myself will show him how great things he must suffer for my name's sake.
Domin zan nuna masa irin wahalar da zai sha sabo da sunana.''
17 And Ananias went away, and entered the house; and putting his hands on him, he said, Brother Saul, the Lord, even Jesus who appeared to thee in the way thou camest, hath sent me, that thou mayst receive sight, and be filled with the Holy Spirit.
Sai Hananiya ya tafi, ya shiga gidan. Ya dora masa hannu a kai, ya ce, ''Dan'uwa Shawulu, Ubangiji Yesu, wanda ya bayyana a gareka a hanya sa'adda kake zuwa, ya aiko ni domin ka sami ganin gari ka kuma cika da Ruhu Mai Tsarki.''
18 And immediately there fell off from his eyes as it were scales; and he received sight, and arose, and was baptized.
Nan take wani abu kamar bawo ya fado daga idanun Shawulu, kuma ya sami ganin gari; ya tashi aka yi masa baftisma;
19 And having taken some food he was strengthened. And he was some days with the disciples in Damascus.
kuma ya ci abinci sai aka karfafa shi. Ya zauna tare da almajirai a Dimashku kwanaki da yawa.
20 And immediately he preached Jesus in the synagogues, that he is the Son of God.
Nan take ya fara shellar Yesu cikin haikali, yana cewa shine dan Allah.
21 And all that heard him were amazed, and said, Is not this he that destroyed in Jerusalem those who called on this name? And he hath come hither for this purpose, that he may bring them bound to the chief priests.
Dukan wadanda suka saurare shi suka yi mamaki suka ce ''Ba wannan mutumin ne yake hallaka mutanen Urushalima da ke kira bisa ga wannan suna ba? Ya kuma zo nan domin ya ba da su a daure ga manyan firistoci.''
22 But Saul gained still more strength, and confounded the Jews who dwelt at Damascus, proving that this is the Christ.
Amma Shawulu kuwa ya sami iko sosai, kuma yana haddasa damuwa tare da rinjaya tsakanin Yahudawan dake zama a Dimashku ta wurin tabbatar da Yesu shine Almasihu.
23 But after many days had passed, the Jews took counsel together to kill him;
Bayan kwanaki da yawa, sai Yahudawan suka yi shiri domin su kashe shi.
24 but their plot became known to Saul; and they were even watching the gates day and night to kill him.
Amma shirin su ya zama sananne ga Shawulu. Suna fakkon sa ta wurin tsaron kofar birnin dare da rana domin su kashe shi.
25 But his disciples took him by night, and let him down through the wall, lowering him in a basket.
Amma da tsakar dare almajiransa suka daukeshi a kwando, suka zurara shi ta katanga.
26 And when he had come to Jerusalem, he attempted to join himself to the disciples; and they were all afraid of him, not believing that he was a disciple.
Sa'adda ya zo Urushalima, Shawulu ya yi niyyar hada kai da almajirai, amma dukansu suna tsoronsa, domin ba su yarda cewa shima ya zama almajiri ba.
27 But Barnabas took him, and brought him to the apostles, and related to them how he had seen the Lord on the road, and that he had spoken to him, and hew he had preached boldly at Damascus in the name of Jesus.
Amma Barnaba ya dauke shi ya kawo shi wurin manzannin. Ya kuwa gaya musu yadda Shawulu ya sadu da Ubangiji a hanya, har Ubangiji ya yi magana da shi, kuma yadda Shawulu ya yi wa'azi cikin sunan Yesu gabagadi a Dimashku.
28 And he was with them going in and out at Jerusalem,
Ya sadu da su lokacin shigar su da fitar su a Urushalima. Ya yi wa'azi gabagadi cikin sunan Ubangiji Yesu
29 speaking boldly in the name of the Lord. And he often spoke and disputed with the Hellenists; but they were endeavoring to slay him.
kuma yana muhawara da Yahudawan Helenanci; amma sun ci gaba da kokarin kashe shi.
30 But the brethren obtaining knowledge of it, brought him down to Caesarea, and sent him forth to Tarsus.
Da 'yan'uwa suka gane haka, sai suka kawo shi Kaisariya, suka kuwa tura shi zuwa Tarsus.
31 The church therefore throughout all Judaea and Galilee and Samaria had peace, being built up, and walking in the fear of the Lord; and by the exhortation of the Holy Spirit it was greatly increased.
Sa'annan iklisiya dake dukan kasar Yahudiya, Galili da kuma Samariya suka sami salama da kuma ginuwa; suka kuwa ci gaba da tafiya cikin tsoron Ubangiji, da kuma ta'aziyar Ruhu Mai Tsarki, iklisiyar kuwa ta karu da yawan mutane.
32 And it came to pass, that as Peter went through the whole country, he came down also to the saints who dwelt at Lydda.
Har ta kai, yayin da Bitrus ya zaga dukan yankin kasar, ya dawo wurin masu bi dake zama a garin Lidda.
33 And there he found a certain man named AEneas, who had lain on a bed eight years, and was palsied.
A can kuwa ya sami wani mutum mai suna Iniyasu, wanda yake shanyayye ne, yana kwance har tsawon shekara takwas a kan gado.
34 And Peter said to him, AEneas, Jesus the Christ healeth thee; arise, and make thy bed. And he arose immediately.
Bitrus ya ce masa, ''Iniyasu, Yesu Almasihu ya warkar da kai. Tashi ka nade shimfidarka.'' Nan take sai ya mike.
35 And all that dwelt in Lydda and Sharon saw him; and they turned to the Lord.
Sai duk mazauna kasar Lidda da kasar Sarona suka ga mutumin, suka kuma juyo ga Ubangiji.
36 Now at Joppa there was a certain disciple named Tabitha, which name being interpreted is the same as Dorcas, that is, Gazelle. This woman was full of good works and alms-deeds which she did.
Yanzu kuwa a Yafa akwai wata almajira, mai suna Tabita, ma'ana ''Dokas.'' Wannan matar kuwa tana chike da ayyukan nagarta da halin tausayi da take yi ga mabukata.
37 And it came to pass in those days, that she fell sick, and died; and when they had washed her, they laid her in an upper chamber.
Ya kai ga cewa a kwanakin can ta yi rashin lafiya har ta mutu; da suka wanke gawar ta suka kwantar da ita a bene.
38 And as Lydda was near Joppa, the disciples, having heard that Peter was there, sent to him two men with the entreaty, Do not delay to come to us.
Da shike Lidda na kusa da Yafa, almajiran kuma sun ji cewa Bitrus yana can, suka aika mutane biyu wurinsa. Suna rokansa, ''Ka zo garemu ba tare da jinkiri ba.''
39 Then Peter arose, and went with them. When he was come, they brought him into the upper chamber; and all the widows came to him weeping, and showing the coats and cloaks which Dorcas made while she was with them.
Bitrus ya tashi ya tafi da su, da isowar sa, suka kai shi benen. Sai dukan gwamrayen suka tsaya kusa da shi suna kuka, sai suka dauko riguna da sutura da Dokas ta dinka lokacin da take tare da su.
40 But Peter put them all forth, and kneeled down and prayed; and turning to the body he said, Tabitha, arise. And she opened her eyes; and seeing Peter, she sat up.
Bitrus ya fitar da su duka daga cikin dakin, ya durkusa, ya yi addu'a; sai, ya juya wurin gawar, ya ce, ''Tabita, tashi.'' Ta bude idanunta, da ta ga Bitrus ta zauna,
41 And he gave her his hand, and raised her up; and calling the saints and the widows, he presented her alive.
Bitrus kuwa ya mika hannunsa ya tashe ta; sa'annan ya kira masu bi da gwamrayen, ya mika ta a raye garesu.
42 And it became known throughout all Joppa; and many believed in the Lord.
Wannan al'amari ya zama sananne cikin dukan Yafa, kuma mutane da yawa suka bada gaskiya ga Ubangiji.
43 And it came to pass, that he tarried many days in Joppa with one Simon, a tanner.
Ya kasance, cewa, Bitrus ya zauna kwanaki da dama a Yafa tare da wani mutum mai suna Saminu, majemi.

< Acts 9 >