< Acts 4 >
1 And while they were speaking to the people, the priests and the captain of the temple and the Sadducees came upon them,
Yayin da Bitrus da Yahaya suna kan magana da mutanen, sai firistoci da shugaban masu tsaron Haikali da kuma Sadukiyawa suka afko masu.
2 being indignant that they taught the people, and proclaimed in Jesus the resurrection from the dead.
Sun damu sosai domin Bitrus da Yahaya suna koyar da mutane game da Yesu kuma suna shelar tashinsa daga matattu.
3 And they laid hands upon them, and put them in prison until the next day; for it was now evening.
Suka kama su suka jefa kurkuku sai washegari, domin yamma ta riga ta yi.
4 Many however of those who heard the word believed; and the number of the men became five thousand.
Amma mutane da yawa da suka ji sakon suka ba da gaskiya; kimanin mazaje dubu biyar ne kuwa suka ba da gaskiya.
5 And it came to pass on the next day, that their rulers and elders and scribes,
Washegari, da shugabaninsu, da dattawansu, da Marubuta suka taru a Urushalima.
6 and Annas the high-priest, and Caiaphas, and John, and Alexander, and as many as were of the kindred of the high-priest, were gathered together at Jerusalem.
Anas babban firist, yana nan, da Kayafa, da Yahaya da Iskandari, da dukan dangin babban firist
7 And when they had set them in the midst, they asked, By what power, or by what name, did ye do this?
Da suka kawo Bitrus da Yahaya a tsakiyarsu sai suka tambaye su, “Da wanne iko, ko cikin wanne suna k ka yi haka?”
8 Then Peter, filled with the Holy Spirit, said to them, Rulers of the people, and elders of Israel!
Sai Bitrus, cike da Ruhu Mai Tsarki, ya ce, “Ku shugabanni da dattawan jama'a,
9 If we are this day examined in respect to a good deed done to a cripple, by what means he hath been restored,
idan mu yau ana tuhumarmu saboda aikin kirki da aka yi ga wannan mara lafiya - ta yaya wannan mutum ya sami lafiya?
10 be it known to you all, and to all the people of Israel, that by the name of Jesus Christ the Nazarene, whom ye crucified, whom God raised from the dead, —by him doth this man stand here before you sound.
Bari ku da dukan mutanen Isra'ila, ku san wannan, cikin sunan Yesu Almasihu Banazare, wanda kuka giciye, wanda Allah ya tayar daga matattu ta dalilinsa ne wannan mutumin yake tsaye a gaban ku lafiyayye.
11 This is the stone which was set at nought by you the builders, which is become a cornerstone.
Yesu Almasihu ne dutsen da ku magina kuka ki, amma an mai da shi kan gini.
12 And there is salvation in no other; for there is not another name under heaven, that hath been given among men, by which we must be saved.
Babu ceto daga kowanne mutum, domin babu wani suna da aka bayar karkashin sama, a cikin mutane wanda ta wurinsa za a iya samu ceto.''
13 And when they beheld the boldness of Peter and John, and perceived that they were unlearned and common men, they wondered; and they recognized them as having been with Jesus.
Sa'adda, suka ga karfin halin Bitrus da Yahaya, suka gane mutane ne talakawa marasa ilimi, sai suka yi mamaki, suka kuma lura suka gane Bitrus da Yahaya sun kasance tare da Yesu.
14 And seeing the man that had been cured standing with them, they could say nothing in reply.
Da yake suna ganin mutumin nan da aka warkar tare da su, sai suka rasa abin yi.
15 But when they had commanded them to go aside out of the council, they conferred among themselves,
Amma bayan sun fitar da manzannin daga majalisa sai suka tattauna a tsakaninsu.
16 saying, What shall we do to these men? for that indeed a remarkable sign hath been wrought by them is manifest to all that dwell in Jerusalem; and we cannot deny it.
Suka ce, “Yaya za mu yi da wadannan mutane? Babu shakka aikin al'ajibi ya faru ta wurinsu, kuma sananne ne ga dukan mazauna Urushalima, kuma ba mu da iko mu musanci haka.
17 But that it spread no further among the people, let us strictly forbid them with threats to speak any longer in this name to any one.
Amma saboda kada ya cigaba da yaduwa cikin mutane, bari mu yi masu kashedi kada su kara magana da kowa cikin wannan suna.''
18 And they called them, and commanded them not to speak at all, nor teach, in the name of Jesus.
Suka kira Bitrus da Yahaya suka dokace su kada su kara magana ko kuma koyarwa ko kadan a cikin sunan Yesu.
19 But Peter and John answered and said to them, Whether it is right in the sight of God to hearken to you rather than to God, judge ye.
Amma Bitrus da Yahaya suka amsa suka ce, ''Ko ya yi daidai a gaban Allah mu yi maku biyayya fiye da shi, ku hukunta.
20 For we cannot but speak the things which we saw and heard.
Baza mu iya daina magana game da abubuwan da muka ji kuma muka gani ba.''
21 So, having further threatened them, they let them go, finding no way to punish them, on account of the people; because all were glorifying God for that which had been done.
Bayan sun sake yi wa Bitrus da yahaya kashedi, sai suka sake su, su tafi. Domin ba su iya samu wata hujja da za su hore su a kai ba, domin dukan mutane suna yabon Allah saboda abin da ya faru.
22 For the man was above forty years old, on whom this sign of the healing had been wrought.
Mutumin da ya sami wannan al'ajibi na warkarwa yana sama da shekara arba'in.
23 And being released they went to their own company, and reported all that the chief priests and elders had said to them.
Bayan an sake su, Bitrus da Yahaya suka zo cikin mutanensu suka ba da rahoton duk abin da manyan firistoci da dattawa suka fada masu.
24 And on hearing it, they lifted up their voice to God with one accord, and said, Lord, thou art he that made heaven and earth and sea, and all things that are in them;
Da suka ji haka, suka daga muryarsu tare ga Allah suka ce, ''Ubangiji, kai da ka yi sama da duniya da teku da duk abin da ke cikinsu,
25 who by the mouth of thy servant David said, “Why did the heathen rage, and the peoples meditate vain things?
kai wanda ta wurin Ruhu Mai Tsarki ta bakin ubanmu Dauda bawanka, ya ce, 'Me ya sa al'ummai suka tunzura, kuma mutane suke tunanin abubuwan banza?
26 The kings of the earth came up, and the rulers assembled together, against the Lord, and against his Anointed.”
Sarakunan duniya sun hada kansu tare, kuma shugabanninsu sun taru don su yi gaba da Ubangiji, da kuma Almasihunsa.'
27 For in truth against thy holy servant Jesus, whom thou didst anoint, did both Herod and Pontius Pilate, with the gentiles, and the peoples of Israel, assemble in this city,
Hakika, Hiridus da Buntus Bilatus, tare da al'ummai da mutanen Isra'ila, sun taru a wannan birni domin su yi jayayya da bawanka mai tsarki Yesu, shafaffe.
28 to do whatever thy hand and thy will before determined to be done.
Sun taru domin su aiwatar da dukan abin da hannunka da nufinka ya shirya zai faru.
29 And now, Lord, look upon their threatenings, and grant to thy servants that with all boldness they may speak thy word,
Yanzu, Ya Ubangiji ka dubi kashedin su, ka ba bayin ka ikon furta maganar ka gabagadi.
30 while thou stretchest forth thy hand to heal, and signs and wonders are wrought through the name of thy holy servant Jesus.
Sa'adda ka mika hannunka domin warkarwa, alamu da al'ajibai su faru ta wurin sunan bawanka mai tsarki Yesu.”
31 And when they had prayed, the place was shaken where they were assembled; and they were all filled with the Holy Spirit, and they spoke the word of God with boldness.
Bayan sun gama addu'a, wurin da suka taru ya girgiza, suka cika da Ruhu Mai Tsarki, suka furta maganar Allah gabagadi.
32 And the multitude of those who believed were of one heart, and of one soul; and not one of them said that aught of the things which he possessed was his own; but they had all things common.
Babban taron da suka ba da gaskiya kansu hade yake; kuma ba wanda ya ce da abinda ya mallaka nasa ne; maimakon haka, komai na su daya ne.
33 And with great power did the apostles give their testimony to the resurrection of the Lord Jesus; and great grace was upon them all.
Da iko mai karfi manzannin suka yi shelar shaidarsu game da tashin Yesu Ubangiji daga matattu, babban alheri kuma na bisansu.
34 For there was no one among them that was in want; for as many as were possessors of lands or houses sold them, and brought the prices of the things that were sold,
Babu wani a cikinsu wanda ya rasa komai, domin masu filaye da gidaje suka sayar suka kawo kudin abin da suka sayar
35 and laid them at the feet of the apostles; and distribution was made to every one, according as he had need.
sai suka kawo kudin gaban manzanni. Aka rarraba wa kowanne mutum bisa ga bukatarsa.
36 And Joseph, who by the apostles was surnamed Barnabas, (which is, when interpreted, Son of consolation, ) a Levite, born in Cyprus,
Yusufu, Balawi, mutumin tsibirin Kubrus, wanda manzannisu ka yi wa lakani da suna Barnaba. (wato, mai karfafa zuciya).
37 having land, sold it, and brought the money, and laid it at the feet of the apostles.
Yana da fili sai ya sayar da shi ya kawo kudin gaban manzanni.