< Acts 3 >
1 And Peter and John were going up together to the temple, at the hour of prayer, which is the ninth hour.
Wata rana, Bitrus da Yohanna suna haurawa zuwa haikali a lokacin addu’a da ƙarfe uku na rana.
2 And a certain man lame from his birth was carried along, whom they laid daily at the gate of the temple which is called Beautiful, to ask alms of those who entered the temple;
To, sai ga wani da aka haifa gurgu ana ɗauke da shi zuwa ƙofar haikalin da ake kira Kyakkyawa, inda akan ajiye kowace rana, don yă yi bara daga masu shigowa cikin filayen haikali.
3 who, seeing Peter and John about to go into the temple, asked alms.
Da ya ga Bitrus da Yohanna suna gab da shiga, sai ya roƙe su kuɗi.
4 And Peter fixing his eyes upon him, with John, said, Look upon us.
Bitrus kuwa ya kafa masa ido, haka ma Yohanna. Sai Bitrus ya ce, “Dube mu!”
5 And he gave heed to them, expecting to receive something from them.
Saboda haka mutumin ya mai da hankalinsa a kansu, yana fata samun wani abu daga gare su.
6 Then Peter said, Silver and gold have I none; but what I have I give thee. In the name of Jesus Christ the Nazarene, rise up and walk.
Sai Bitrus ya ce, “Azurfa ko zinariya ba ni da su, amma abin da nake da shi, shi zan ba ka. A cikin sunan Yesu Kiristi Banazare, ka yi tafiya.”
7 And grasping him by the right hand, he raised him up; and immediately his feet and ankles received strength.
Ta wurin kama hannunsa na dama, ya taimake shi ya miƙe, nan take ƙafafu da idon sawun mutumin suka yi ƙarfi.
8 And leaping forth he stood, and walked, and entered with them into the temple, walking and leaping, praising God.
Sai ya yi wuf da ƙafafunsa ya fara tafiya. Ya tafi tare da su ya shiga cikin filin haikali yana tafiya yana tsalle, yana kuma yabon Allah.
9 And all the people saw him walking, and praising God;
Sa’ad da dukan mutane suka gan shi yana tafiya yana yabon Allah,
10 and they recognized him as the man that sat for alms at the Beautiful Gate of the temple; and they were filled with wonder and amazement at that which had happened to him.
sai suka gane cewa shi ne mutumin nan wanda dā yake zama yana bara a bakin ƙofar haikalin da ake kira Kyakkyawa, suka kuwa cika da mamaki da tsoro a kan abin da ya faru gare shi.
11 And as he held fast to Peter and John, all the people ran together to them in the porch that is called Solomon's greatly wondering.
Tun mai bawan yana riƙe da Bitrus da Yohanna, dukan mutanen suka yi mamaki, suka zo wurinsu a guje a inda ake kira Shirayin Solomon.
12 But Peter seeing it, answered the people: Men of Israel, why wonder ye at this? Or why look ye earnestly on us, as though by our own power or godliness we had made this man to walk?
Da Bitrus ya ga haka, sai ya ce musu, “Mutanen Isra’ila, don me wannan ya ba ku mamaki? Don me kuke kallonmu sai ka ce da ikon kanmu ne ko kuwa don ibadarmu ne muka sa wannan mutum ya yi tafiya?
13 The God of Abraham and Isaac and Jacob, the God of our fathers, hath glorified his servant Jesus, whom ye indeed delivered up, and denied him in the presence of Pilate, when he had decided to release him.
Allah na Ibrahim, Ishaku, da Yaƙub, Allah na kakanninmu, ya ɗaukaka bawansa Yesu. Ku kuka ba da shi domin a kashe, kuka yi mūsun saninsa a gaban Bilatus, ko da yake ya yi niyya ya sake shi.
14 But ye denied the holy and righteous one, and asked that a murderer should be granted to you.
Kuka yi mūsun sanin Mai Tsarki da Mai Adalci kuka roƙa a sakar muku mai kisankai.
15 But the author of life ye killed; whom God raised from the dead, whereof we are witnesses.
Kuka kashe tushen rai, amma Allah ya tashe shi daga matattu. Mu shaidu ne ga wannan.
16 And his name, through faith in his name, made this man strong, whom ye see and know; yea, the faith which is through him gave him this perfect soundness in the presence of you all.
Ta wurin bangaskiya cikin sunan Yesu ne wannan mutum da kuke gani kuka kuma sani ya sami ƙarfi. Da sunan Yesu, da kuma bangaskiyar da take samuwa ta wurinsa ne ya ba shi cikakkiyar warkarwa, yadda dukanku kuke gani.
17 And now, brethren, I know that ye acted in ignorance, as did also your rulers.
“To,’yan’uwa, na san cewa, kun aikata wannan cikin jahilci ne, yadda shugabanninku suka yi.
18 But God thus fulfilled what he had before announced by the mouth of all the prophets, that his Christ should suffer.
Amma ta haka ne Allah ya cika abin da ya rigyafaɗi ta bakin dukan annabawa cewa, Kiristinsa zai sha wahala.
19 Repent therefore and turn from your ways, that your sins may be blotted out, in order that the times of refreshing may come from the presence of the Lord,
Saboda haka ku tuba, ku juyo ga Allah, don a shafe zunubanku, don lokutan wartsakewa su zo daga wurin Ubangiji,
20 and that he may send forth Christ Jesus, who was before appointed for you;
don kuma ya iya aika da Kiristi, wanda aka naɗa tun dā saboda ku, Yesu ke nan.
21 whom heaven indeed must receive until the times of a restoration of all things; of which times God spoke by the mouth of his holy prophets from the days of old. (aiōn )
Dole yă kasance a sama, sai lokaci ya yi da Allah zai mai da kome sabo, yadda ya yi alkawari tun dā ta wurin annabawansa masu tsarki. (aiōn )
22 Moses indeed said, “A prophet will the Lord your God raise up to you from among your brethren, as be raised up me; him shall ye hear in all things, whatever he shall speak to you.
Gama Musa ya ce, ‘Ubangiji Allahnku zai tasar muku wani annabi kamar ni daga cikin mutanenku; dole ku saurari duk abin da ya faɗa muku.
23 And it shall come to pass, that every soul which doth not hear that prophet shall be utterly destroyed from among the people.”
Duk wanda bai saurare shi ba za a ware shi gaba ɗaya daga mutanensa.’
24 And all the prophets also, Samuel and those who followed, as many as spoke, announced these days.
“Tabbatacce, dukan annabawa daga Sama’ila zuwa gaba, dukansu da suka yi magana, sun rigya faɗin waɗannan kwanaki.
25 Ye are the sons of the prophets, and of the covenant which God made with our fathers, saying to Abraham, “And in thy posterity shall all the families of the earth be blessed.”
Ku kuwa magādan annabawan ne da kuma na alkawarin da Allah ya yi da kakanninku. Ya ce wa Ibrahim, ‘Ta wurin zuriyarka, dukan kabilan duniya za su sami albarka.’
26 To you first, God, having raised up his servant, sent him to bless you in turning away every one of you from your iniquities.
Da Allah ya tashe bawansa, ya aike shi da fari zuwa gare ku don yă albarkace ku ta wurin juye kowannenku daga mugayen hanyoyinku.”