< 2 Timothy 1 >
1 Paul, an apostle of Christ Jesus by the will of God, according to the promise of life which is in Christ Jesus,
Bulus, manzon Kiristi Yesu ta wurin nufin Allah, bisa ga alkawarin rai wanda yake cikin Kiristi Yesu,
2 to Timothy, my beloved child: Grace, mercy, peace, from God the Father and Christ Jesus our Lord.
Zuwa ga Timoti, ƙaunataccen ɗana. Alheri, jinƙai da salama daga Allah Uba da kuma Kiristi Yesu Ubangijinmu, su kasance tare da kai.
3 I thank God, whom I serve from my forefathers with pure conscience, as without ceasing I have remembrance of thee in my prayers night and day,
Na gode wa Allah wanda nake bauta wa, kamar yadda kakanni-kakannina suka yi da lamiri mai tsabta, yadda kullum dare da rana ina tuna da ku a cikin addu’o’ina.
4 longing to see thee, being mindful of thy tears, that I may be filled with joy;
Sa’ad da na tuna da hawayenka, nakan yi marmarin ganinka, don in cika da farin ciki.
5 when I call to remembrance the unfeigned faith that is in thee, which dwelt first in thy grandmother Lois, and thy mother Eunice; and I am persuaded that it dwelleth in thee also.
An tunashe ni da sahihiyar bangaskiyarka, wadda a farko ta kasance a cikin kakarka Loyis da kuma mahaifiyarka Yunis yanzu kuwa na tabbata tana cikinka.
6 For which cause I remind thee to stir up the gift of God, which is in thee by the laying on of my hands;
Saboda haka, ina so in faɗakar da kai, ka lura baiwan nan ta Allah, wadda take tare da kai ta wurin ɗibiya maka hannuwana.
7 for God gave us not the spirit of cowardice, but of power, and of love, and of admonition.
Gama Allah bai ba mu ruhun tsoro ba, sai dai ruhun iko, na ƙauna da kuma na kamunkai.
8 Be not then ashamed of the testimony of our Lord, nor of me his prisoner; but endure hardship with me for the gospel through the power of God,
Saboda haka kada ka ji kunyar ba da shaida game da Ubangijinmu, ko kuwa ka ji kunyata, ni da nake ɗan sarƙa saboda shi. Sai dai ka haɗa kai tare da ni cikin shan wahala saboda bishara ta wurin ikon Allah,
9 who saved us, and called us with a holy calling, not according to our works, but according to his own purpose and the grace which was given us in Christ Jesus before the world began, (aiōnios )
wanda ya cece mu ya kuma kira mu ga rayuwar tsarki ba saboda wani abin da muka yi ba sai dai saboda nufinsa da kuma alherinsa. An ba mu wannan alheri cikin Kiristi Yesu tun fil azal, (aiōnios )
10 but is now made manifest by the appearing of our Saviour Christ Jesus, who abolished death, and brought life and incorruption to light through the gospel,
amma yanzu an bayyana ta ta wurin bayyanuwar Mai Cetonmu, Kiristi Yesu, wanda ya hallaka mutuwa ya kuma kawo rai da rashin mutuwa a sarari ta wurin bishara.
11 for which I was appointed a herald, and an apostle, and a teacher of the gentiles.
A wannan bishara ce, aka naɗa ni mai shela da manzo da kuma malami.
12 For which cause I suffer also these things. But I am not ashamed; for I know whom I have believed, and am persuaded that he is able to keep that which he hath committed to me unto that day.
Shi ya sa nake shan wahalar da nake sha. Duk da haka ba na jin kunya, domin na san wanda na gaskata da shi, na kuma tabbata cewa yana iya kiyaye abin da na danƙa masa amana don wancan rana.
13 Hold the pattern of sound words, which thou heardest from me, in faith and love which is in Christ Jesus;
Abin da ka ji daga gare ni, ka kiyaye shi kamar tsarin sahihiyar koyarwa, cikin bangaskiya da ƙauna cikin Kiristi Yesu.
14 the good trust committed to thee keep through the Holy Spirit which dwelleth in us.
Ka kiyaye kyakkyawar ajiyan nan da aka danƙa maka amana, ka lura da ita da taimakon Ruhu Mai Tsarki wanda yake raye a cikinmu.
15 Thou knowest this, that all those in Asia turned away from me, of whom are Phygelus and Hermogenes.
Ka san cewa kowa a lardin Asiya ya juya mini baya, har da Figelus da Hermogenes.
16 The Lord give mercy to the house of Onesiphorus, because he often refreshed me, and was not ashamed of my chain; but on the contrary,
Bari Ubangiji yă yi wa iyalin Onesiforus jinƙai, domin sau da dama yakan wartsakar da ni, bai kuma ji kunyar sarƙoƙina ba.
17 when he arrived at Rome, he sought me out very diligently, and found me.
A maimakon haka ma, sa’ad da yake a Roma, ya neme ni ido a rufe sai da ya same ni.
18 The Lord grant to him that he may find mercy from the Lord in that day: and what services he rendered me at Ephesus, thou knowest very well.
Bari Ubangiji yă sa yă sami jinƙai daga Ubangiji a wancan ranar! Ka sani sarai yadda ya taimake ni a hanyoyi dabam-dabam a Afisa.