< Psalms 147 >

1 Praise JAH, for it is good to sing praises to our God; for it is pleasant and fitting to praise him.
Yabi Ubangiji. Yana da kyau a rera yabai ga Allahnmu, abu mai daɗi ne daidai ne kuma a yabe shi!
2 YHWH builds up Jerusalem. He gathers together the outcasts of Israel.
Ubangiji ya gina Urushalima; ya tattara kamammu na Isra’ilan da aka kai bauta.
3 He heals the broken in heart, and binds up their wounds.
Ya warkar da masu raunanar zuciya ya ɗaɗɗaura miyakunsu.
4 He counts the number of the stars. He calls them all by their names.
Ya lissafta yawan taurari ya kuma kira kowannensu da suna.
5 Great is our Lord, and mighty in power. His understanding is infinite.
Shugabanmu mai girma ne mai iko duka; ganewarsa ba shi da iyaka.
6 YHWH upholds the humble. He brings the wicked down to the ground.
Ubangiji yana kula da masu sauƙinkai yakan yar da mugaye a ƙasa.
7 Sing to YHWH with thanksgiving. Sing praises on the harp to our God,
Rera wa Ubangiji waƙar godiya; ku kada garaya ga Allahnmu.
8 who covers the sky with clouds, who prepares rain for the earth, who makes grass grow on the mountains.
Ya rufe sararin sama da gizagizai; yana tanada wa duniya ruwan sama yana kuma sa ciyawa tă yi girma a kan tuddai.
9 He provides food for the livestock, and for the young ravens when they call.
Yakan tanada wa shanu abinci da kuma saboda’ya’yan hankaki sa’ad da suka yi kira.
10 He doesn't delight in the strength of the horse. He takes no pleasure in the legs of a man.
Jin daɗinsa ba ya a ƙarfin doki, balle farin cikinsa yă kasance a ƙafafun mutum;
11 YHWH takes pleasure in those who fear him, in those who hope in his loving kindness.
Ubangiji yakan yi farin ciki a waɗanda suke tsoronsa, waɗanda suke sa zuciya a ƙaunarsa marar ƙarewa.
12 Praise YHWH, Jerusalem. Praise your God, Zion.
Ki ɗaukaka Ubangiji, ya Urushalima; ki yabi Allahnki, ya Sihiyona.
13 For he has strengthened the bars of your gates. He has blessed your children within you.
Gama yana ƙarfafa ƙyamaren ƙofofinki yana kuma albarkace mutanenki a cikinki.
14 He makes peace in your borders. He fills you with the finest of the wheat.
Yana ba da salama ga iyakokinki yana kuma ƙosar da ke da alkama mafi kyau.
15 He sends out his commandment to the earth. His word runs very swiftly.
Yana ba da umarninsa ga duniya; maganarsa tana tafiya da sauri.
16 He gives snow like wool, and scatters frost like ashes.
Yana shimfiɗa ƙanƙara kamar ulu yă kuma watsar da hazo kamar toka.
17 He hurls down his hail like pebbles. Who can stand before his cold?
Yana zuba ƙanƙara kamar ƙananan duwatsu. Wa zai iya jure wa sanyin da ya aiko?
18 He sends out his word, and melts them. He causes his wind to blow, and the waters flow.
Yakan aiki maganarsa ta kuwa narkar da su; yakan tā da iskarsa, ruwaye kuwa su gudu.
19 He shows his word to Jacob; his statutes and his ordinances to Israel.
Ya bayyana maganarsa ga Yaƙub, dokokinsa da ƙa’idodinsa ga Isra’ila.
20 He has not done this for just any nation. They do not know his ordinances. Praise JAH.
Bai yi wannan ga wata al’umma ba; ba su san dokokinsa ba. Yabi Ubangiji.

< Psalms 147 >