< Proverbs 8 >

1 Doesn't wisdom cry out? Doesn't understanding raise her voice?
Hikima ba ta yin kira ne? Fahimi ba ya tā da muryarsa ne?
2 On the top of high places by the way, where the paths meet, she stands.
A ƙwanƙoli a kan hanya, inda hanyoyi suka haɗu, ta ɗauki matsayinta;
3 Beside the gates, at the entry of the city, at the entry doors, she cries aloud:
kusa da ƙofofin shiga cikin birni, a mashigai, ta tā da murya,
4 "To you men, I call. I send my voice to the sons of humankind.
“Gare ku, ya mutane, nake kira; na tā da muryata ga dukan’yan adam.
5 You simple, understand prudence. You fools, be of an understanding heart.
Ku da kuke marasa azanci, ku yi hankali; ku da kuke wawaye, ku nemi fahimi.
6 Hear, for I will speak excellent things. The opening of my lips is for right things.
Ku saurara, gama ina da abubuwa masu darajan da zan faɗa; na buɗe leɓunana don in faɗa abin da yake daidai.
7 For my mouth speaks truth. Wickedness is an abomination to my lips.
Bakina yana magana abin da yake gaskiya, gama leɓunana sun ƙi mugunta.
8 All the words of my mouth are in righteousness. There is nothing crooked or perverse in them.
Dukan kalmomin bakina suna da adalci; babu waninsu da ya karkace ko kuwa ƙarya ne.
9 They are all plain to him who understands, right to those who find knowledge.
Ga mai tunani dukansu daidai ne; ba su da laifi ga waɗanda suke da sani.
10 Receive my instruction rather than silver; knowledge rather than choice gold.
Ku zaɓi umarnina a maimakon azurfa, sani a maimakon zinariya zalla,
11 For wisdom is better than rubies. All the things that may be desired can't be compared to it.
gama hikima ta fi lu’ulu’ai daraja, kuma ba abin da kake sha’awa da za a kwatanta da ita.
12 "I, wisdom, have made prudence my dwelling. Find out knowledge and discretion.
“Ni, hikima, ina zama tare da hankali; ina da sani da iya rarrabewa.
13 The fear of YHWH is to hate evil. I hate pride, arrogance, the evil way, and the perverse mouth.
Jin tsoron Ubangiji shi ne ƙin mugunta; ina ƙin girman kai da fariya, halin mugunta da kuma muguwar magana.
14 Counsel and sound knowledge are mine. I have understanding and power.
Shawara da yin tunani mai kyau nawa ne; ina da fahimi da kuma iko.
15 By me kings reign, and rulers decree justice.
Ta wurina sarakuna suke mulki masu mulki kuma suke yin dokokin da suke da adalci;
16 By me princes rule; nobles, and all the righteous rulers of the earth.
ta wurina sarakuna suke mulki, da kuma dukan manyan mutanen da suke mulkin duniya.
17 I love those who love me. Those who seek me diligently will find me.
Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata, kuma waɗanda suke nemana sukan same ni.
18 With me are riches, honor, enduring wealth, and prosperity.
Tare da ni akwai wadata da girmamawa, dukiya da wadata masu dawwama.
19 My fruit is better than gold, yes, than fine gold; my yield than choice silver.
’Ya’yan itacena sun fi zinariya zalla; amfanin gonar da nake bayar ya fi azurfa mafi kyau.
20 I walk in the way of righteousness, in the midst of the paths of justice;
Ina tafiya a hanyar adalci, a kan hanyoyin gaskiya,
21 That I may give wealth to those who love me. I fill their treasuries.
ina ba da wadata ga waɗanda suke ƙaunata ina sa wuraren ajiyarsu su cika.
22 "YHWH created me in the beginning of his way, before his works of old.
“Ubangiji ya kawo ni a matsayi na farko na ayyukansa, kafin ayyukansa na tuntuni;
23 I was set up from everlasting, from the beginning, before the earth existed.
an naɗa ni tun fil azal, daga farko, kafin duniya ta kasance.
24 When there were no depths, I was brought forth, when there were no springs abounding with water.
Sa’ad da babu tekuna, aka haife ni, sa’ad da babu maɓulɓulai masu ruwa;
25 Before the mountains were settled in place, before the hills, I was brought forth;
kafin a kafa duwatsu a wurarensu, kafin tuddai ma, an haife ni,
26 while as yet he had not made the earth, nor the fields, nor the beginning of the dust of the world.
kafin ya yi duniya ko gonaki ko wata ƙurar duniya.
27 When he established the heavens, I was there; when he set a circle on the surface of the deep,
Ina nan sa’ad da ya kafa sammai a wurarensu, sa’ad da ya shata sararin sama a kan fuskar zurfafa,
28 when he established the clouds above, when the springs of the deep became strong,
sa’ad da ya kafa gizagizai a bisa ya kuma kafa maɓulɓulan zurfafa daram,
29 when he gave to the sea its boundary, that the waters should not violate his commandment, when he marked out the foundations of the earth;
sa’ad da ya ba wa teku iyakarsa domin kada ruwaye su zarce umarninsa, da kuma sa’ad da ya shata tussan duniya.
30 then I was the craftsman by his side. I was a delight day by day, always rejoicing before him,
A lokacin ni ne mai tsara abubuwa a gefensa. Na cika da murna kowace rana, kullum ina farin ciki a gabansa,
31 Rejoicing in his whole world. My delight was with the sons of men.
ina farin ciki da dukan duniyarsa ina murna da’yan adam.
32 "Now therefore, son, listen to me, for blessed are those who keep my ways.
“Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; masu albarka ne waɗanda suke kiyaye hanyoyina.
33 Hear instruction, and be wise. Do not refuse it.
Ku saurari umarnina ku kuma zama masu hikima; kada ku ƙyale ta.
34 Blessed is the man who hears me, watching daily at my gates, waiting at my door posts.
Mai albarka ne wanda ya saurare ni; yana tsaro kullum a ƙofofina, yana jira a ƙofar shigata.
35 For whoever finds me, finds life, and will obtain favor from YHWH.
Gama duk wanda ya same ni ya sami rai zai kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
36 But he who sins against me wrongs his own soul. All those who hate me love death."
Amma duk wanda ya kāsa samuna ya cuci kansa; dukan waɗanda suke ƙina suna ƙaunar mutuwa ke nan.”

< Proverbs 8 >