< Mark 15 >

1 Immediately in the morning the chief priests, with the elders and scribes, and the whole council, held a consultation, and bound Jesus, and carried him away, and delivered him to Pilate.
Da sassafe, sai manyan firistoci suka hadu da dattawa da manyan malamai, da majalisa suka daure Yesu, suka sa shi gaba suka mika shi ga Bilatus.
2 Pilate asked him, "Are you the King of the Jews?" He answered, "You say so."
Bilatus ya tambaye shi, kaine sarkin Yahudawa? ya amsa ya ce “haka ka ce”
3 The chief priests accused him of many things.
Sai manyan firistochi suka kawo zargi iri iri a kan Yesu.
4 Pilate again asked him, "Have you no answer? See how many things they testify against you."
Bilatus ya sake tambayarsa, ba ka da abin cewa? ka lura da yawan zargi da ake yi maka.
5 But Jesus made no further answer, and Pilate was amazed.
Amma Yesu baya sake yi masa magana ba. wannan ya ba shi mamaki.
6 Now at the feast he used to release to them one prisoner, whom they requested.
A lokacin idi, Bilatus ya kan sakar masu da dan bursuna wanda jama'a suka bukaci a saka,
7 There was one called Barabbas, bound with those who had made insurrection, who in the insurrection had committed murder.
A cikin gidan yari, in da aka tsare wadansu yan tawaye, da masu kisan kai, akwai wani mai kisan kai, ana ce da shi Barrabbas.
8 And the crowd went up and began to ask him to do for them according to his custom.
Sai Jama'a suka zo wurin Bilatus ya yi masu kamar yadda ya saba yi.
9 Pilate answered them, saying, "Do you want me to release to you the King of the Jews?"
Bilatus ya amsa masu ya ce, kuna so in sakar maku sarkin Yahudawa?
10 For he perceived that for envy the chief priests had delivered him up.
Yayi wannan domin ya sani cewa Firistoci sun bada shi ne domin suna kishin sa,
11 But the chief priests stirred up the crowd, that he should release Barabbas to them instead.
Sai Firistochi suka zuga jama'a, sai suka yi kuwwa suna cewa, a sakar masu Barrabbas amaimakon Yesu.
12 Pilate again asked them, "What then should I do to him whom you call the King of the Jews?"
Bilatus ya sake yi masu tambaya “Yaya zan yi da Sarkin Yahudawa?”
13 They shouted again, "Crucify him."
sai suka amsa da kuwwa” a “giciye shi!”
14 Pilate said to them, "Why, what evil has he done?" But they shouted all the louder, "Crucify him."
Bilatus ya ce masu menene laifinsa sai suka kara ihu, “a giciye shi.”
15 Pilate, wishing to please the crowd, released Barabbas to them, and handed over Jesus, when he had flogged him, to be crucified.
Bilatus don yana son ya farantawa jama'a zuciya sai ya sakar masu da Barrabbas sai ya yi wa Yesu bulala, sannan ya mika shi a giciye shi.
16 The soldiers led him away within the court, which is the Praetorium; and they called together the whole cohort.
Sojoji suka kai shi cikin kagara, suka tara rundunan soja,
17 They clothed him with purple, and weaving a crown of thorns, they put it on him.
Suka sa masa tufafin shulaiya suka nada masa rawanin kaya,
18 They began to salute him, "Greetings, King of the Jews."
Suna masa kirari na ba'a suna cewa, “A gaida sarkin Yahudawa!”
19 They struck his head with a reed, and spat on him, and bowing their knees, did homage to him.
Sai suka buge shi a kai da kulki suka kuma tofa masa yau a fuska, suka kuma durkusa suna yi masa sujadar ba'a.
20 When they had mocked him, they took the purple off of him, and put his own garments on him. They led him out to crucify him.
Bayan sun gama yi masa ba'a sai suka cire masa tufafin shunnaiya, sai suka maida masa tasa tufafinsa, sai suka fitar dashi don su giciye shi.
21 And they forced one passing by, Simon of Cyrene, coming from the country, the father of Alexander and Rufus, to go with them, that he might carry his cross.
Suna cikin tafiya sai suka hadu da wani, mai suna Saminu Bakairawani (wato uban Alizanda da Rufus); suka tillasta shi ya dauki gijiyen Yesu.
22 And they brought him to the place called Golgotha, which is translated, "The place of a skull."
Sojojin suka kawo Yesu wurin da ake kira Golgota (wato kokon kai)
23 They offered him wine mixed with myrrh to drink, but he did not take it.
Suka bashi ruwan inabi hade da mur, amma ya ki ya sha.
24 Crucifying him, they parted his garments among them, casting lots on them, what each should take.
Sai suka giciye shi, suka kuma raba tufafinsa suka kuma jefa kuri'a domin kowanne soja ya sami rabonsa.
25 It was nine in the morning, and they crucified him.
A sa'a ta uku aka giciye shi.
26 The superscription of his accusation was written over him, "THE KING OF THE JEWS."
Sai aka rubuta alamar zargi da take cewa “Ga Sarkin Yahudawa”
27 With him they crucified two robbers; one on his right hand, and one on his left.
Suka kuma giciye shi tare da wadansu yan fashi guda biyu.
28 And the Scripture was fulfilled which says, "And he was numbered with transgressors."
Daya a hannun damansa daya a hannun hagunsa. Domin a cika abinda nassi ya fada.
29 Those who passed by blasphemed him, wagging their heads, and saying, "Ha. You who destroy the temple, and build it in three days,
suke wucewa suna zaginsa suna kada kai suna cewa, “Aha! kai da zaka rushe haikali ka kuma gina shi cikin kwana uku,
30 save yourself and come down from the cross."
ka ceci kanka mana, ka sauka daga giciye!”
31 Likewise, also the chief priests mocking among themselves with the scribes said, "He saved others. He cannot save himself.
Haka ma manyan firistoci da malamai, suka yi masa ba'a suna cewa “Ya ceci wadansu amma bai iya ceci kansa ba”
32 Let the Christ, the King of Israel, now come down from the cross, that we may see and believe him." Those who were crucified with him insulted him.
Bari Almasihu Sarkin Yahudawa ya sauka daga giciye. Domin mu gaskata shi, sai wadanda aka giciye shi tare dasu, suma suka yi masa ba'a.
33 Now when it was noon, there was darkness over the whole land until three in the afternoon.
sa'a ta shida zuwa sa'a ta tara, duhu ya rufe ko'ina,
34 Then at three in the afternoon Jesus called out with a loud voice, saying, "Elohi, Elohi, lema shabachthani?" which is translated, "My God, my God, why have you forsaken me?"
A sa'a ta tara, Yesu ya tada murya da karfi ya ce Eloi, Eloi lamathsabathani?” Ma'ana Ya Allahna Ya Allahna, me ya sa ka yashe ni?”
35 Some of those who stood by, when they heard it, said, "Look, he is calling for Elijah."
Wasu daga cikin na tsaye, da suka ji shi, sai suka ce, “Duba, yana kiran Iliya.”
36 One ran, and filling a sponge full of vinegar, put it on a reed, and gave it to him to drink, saying, "Let him be. Let us see whether Elijah comes to take him down."
Sai wani ya hanzarta, ya dauki soso ya tsoma a ruwan inabi mai tsami, ya soka agora ya mika masa don yasha. Mutumin yace bari mu gani ko Iliya zai zo ya saukar da shi.
37 Jesus gave a loud cry, and gave up the spirit.
Sai Yesu yayi kuka da babban murya da karfi sannan ya rasu.
38 The veil of the temple was torn in two from the top to the bottom.
Sai labulen haikalin ya rabu kashi biyu daga sama har kasa.
39 And when the centurion, who stood by opposite him, saw that he cried out like this and breathed his last, he said, "Truly this man was the Son of God."
Sa'adda da jarumin sojan da ke tsaye yana fuskantar Yesu ya ga yadda ya mutum, Sai ya ce “hakika, wannan mutum Dan Allah ne.”
40 There were also women watching from afar, among whom were both Mary Magdalene, and Mary the mother of James the younger and of Josi, and Salome;
Akwai kuma mata wadanda ke dubawa daga nesa. Daga cikinsu akwai Maryamu Magadala, da Maryamu( Uwar Yakubu da Yusufu) da Salome.
41 who, when he was in Galilee, followed him, and served him; and many other women who came up with him to Jerusalem.
Wadannan matan sune suka bishi sa'adda da yake Galilee suna yi masa hidima. Da wadansu mata da yawa suka zo Urushalima tare da shi.
42 When evening had now come, because it was the Preparation Day, that is, the day before the Sabbath,
Da maraice an shiga shirye shirye domin kashe gari asabbaci ce.
43 Joseph of Arimathea, a prominent council member who also himself was looking for the Kingdom of God, came. He boldly went in to Pilate, and asked for the body of Jesus.
Sai Yusufu daga garin Arimatiya ya zo, mutumin kirki, mai girma kuma dan majalisar dattawa, mai sauraron mulkin Allah, da gaba gadi ya tafi wurin Bilatus ya bukaci a bashi jikin Yesu.
44 Pilate was surprised that he was already dead; and summoning the centurion, he asked him whether he had been dead long.
Bilatus ya yi mamakin mutuwar Yesu cikin lokaci kadan, sai ya kira jarumin ya tabbattar koYesu ya mutu.
45 When he found out from the centurion, he granted the body to Joseph.
Bayan ya tabbattar daga wurin jarumin soja cewa Yesu ya mutu, sai ya bada jikin ga Yusufu.
46 He bought a linen cloth, and taking him down, wound him in the linen cloth, and placed him in a tomb which had been cut out of a rock. He rolled a stone against the door of the tomb.
Yusufu ya sayo likafani. ya saukar da shi daga giciye, ya kawo likafanin nan ya lulube jikin Yesu dashi. Ya kai shi kabarin da aka sassaka da dutse, wadda ya shirya shi domin kansa. Ya kawo dutse ya rufe bakin kabarin da shi.
47 Mary Magdalene and Mary, the mother of Josi, saw where he was placed.
Maryamu Magadaliya da Maryamu Uwar Yusufu sun ga wurin da aka yi jana'izar Yesu.

< Mark 15 >