< Judges 17 >

1 There was a man of the hill country of Ephraim, whose name was Micah.
To, wani mutum mai suna Mika daga ƙasar tudu ta Efraim
2 And he said to his mother, "The eleven hundred pieces of silver that were taken from you, about which you uttered a curse, and also spoke it in my ears, look, the silver is with me; I took it, but now I will restore it to you." And his mother said, "Blessed be my son by YHWH."
ya ce wa mahaifiyarsa, “Shekel dubu ɗaya da ɗari ɗaya na azurfa da aka ɗauka daga gare ki wanda kuma ji kin furta la’ana a kai, azurfan yana wurina; ni ne na ɗauka.” Sa’an nan mahaifiyarsa ta ce, “Ubangiji yă albarkace ka ɗana!”
3 And he restored the eleven hundred pieces of silver to his mother; and his mother said, "I most certainly dedicate the silver to YHWH from my hand for my son, to make an engraved image and a molten image."
Sa’ad da ya mayar da azurfa dubu ɗaya da ɗari ɗaya na shekel wa mahaifiyarsa, sai ta ce, “Na ba da azurfata ga Ubangiji don ɗana yă sassaƙa sura yă kuma yi zubin gunki. Zan mayar maka.”
4 When he restored the money to his mother, his mother took two hundred pieces of silver, and gave them to the founder, who made of it an engraved image and a molten image: and it was in the house of Micah.
Saboda haka ya mayar da azurfan wa mahaifiyarsa, ita kuwa ta ɗauki azurfa ɗari biyu na shekel ta ba wa maƙeri, wanda ya mai da su sura da kuma gunki. Aka kuwa sa su a gidan Mika.
5 The man Micah had a house of God, and he made an ephod, and teraphim, and consecrated one of his sons, who became his priest.
To, wannan mutum Mika yana da ɗakin gumaka, ya yi efod da waɗansu gumaka, ya kuma naɗa ɗaya daga cikin’ya’yansa firist nasa.
6 In those days there was no king in Israel: every man did that which was right in his own eyes.
A kwanakin Isra’ila ba ta da sarki; kowa yana yin abin da ya ga dama.
7 There was a young man out of Bethlehem Judah, of the family of Judah, who was a Levite; and he lived there.
Wani saurayi Balawe daga Betlehem a Yahuda, wanda yake zama cikin zuriyar Yahuda,
8 The man departed out of the city, out of Bethlehem Judah, to live where he could find a place, and he came to the hill country of Ephraim to the house of Micah, as he traveled.
ya bar garin ya tafi neman inda zai zauna. A hanyarsa ya zo gidan Mika a ƙasar tudu ta Efraim.
9 Micah said to him, "Where did you come from?" He said to him, "I am a Levite of Bethlehem Judah, and I am going to settle wherever I may find a place."
Mika ya ce masa, “Daga ina kake?” Ya ce, “Ni Balawe ne daga Betlehem a Yahuda, ina kuwa neman wurin zauna ne.”
10 Micah said to him, "Dwell with me, and be to me a father and a priest, and I will give you ten pieces of silver by the year, and a suit of clothing, and your food." So the Levite went in.
Sa’an nan Mika ya ce masa, “Ka zauna tare da ni ka zama mini mahaifi da firist, zan kuwa ba ka azurfa goma na shekel a shekara, tufafinka da kuma abincinka.” Sai Balawen ya tafi.
11 The Levite was content to dwell with the man; and the young man was to him as one of his sons.
Saboda haka Balawen ya yarda ya zauna tare da shi, ɗan saurayin kuwa ya zama kamar ɗaya daga cikin’ya’yansa.
12 Micah consecrated the Levite, and the young man became his priest, and was in the house of Micah.
Sa’an nan Mika ya naɗa Balawen, saurayin kuwa ya zama masa firist ya kuma zauna a gidansa.
13 Then Micah said, "Now I know that YHWH will do good to me, seeing I have a Levite as my priest."
Mika ya ce, “Yanzu na san cewa Ubangiji zai yi mini alheri, da yake Balawen nan ya zama firist nawa.”

< Judges 17 >