< Joshua 9 >

1 It happened, when all the kings who were beyond the Jordan, in the hill country, and in the lowland, and on all the shore of the Great Sea in front of Lebanon, the Hethite, the Amorite, the Canaanite, the Perizzite, the Hivite, and the Jebusite, heard of it
To, sa’ad da dukan sarakunan yammancin Urdun suka ji waɗannan abubuwa, sai waɗanda suke kan tudu, da na cikin kwari a yammanci, da dukan waɗanda suke gefen Bahar Rum har zuwa Lebanon (sarakunan Hittiyawa, Amoriyawa, Kan’aniyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa)
2 that they gathered themselves together to fight with Joshua and with Israel, with one accord.
suka haɗa kansu don su yaƙi Yoshuwa da Isra’ila.
3 But when the inhabitants of Gibeon heard what Joshua had done to Jericho and to Ai,
Amma da mutanen Gibeyon suka ji abin da Yoshuwa ya yi wa Yeriko da Ai,
4 they also resorted to a ruse, and went and made as if they had been ambassadors, and took old sacks on their donkeys, and wineskins, old and torn and bound up,
sai suka shirya wata dabara ta ruɗu, suka shirya ɗan abinci don tafiya, suka ɗauki tsofaffin buhuna a kan jakunansu da tsofaffin salkuna na ruwan inabi, yagaggu da suka sha ɗinki.
5 and old and patched shoes on their feet, and wore old garments. All the bread of their provision was dry and moldy.
Suka sa tsofaffin takalman da suka sha gyara, suka sa tsofaffin tufafi. Dukan abincinsu na tafiya ya bushe ya yi fumfuna.
6 They went to Joshua to the camp at Gilgal, and said to him, and to the men of Israel, "We have come from a far country. Now therefore make a covenant with us."
Sai suka je wurin Yoshuwa a sansanin Gilgal suka ce masa da mutanen Isra’ila, “Daga ƙasa mai nisa muka fito, yanzu fa, sai ku yi alkawari da mu.”
7 The men of Israel said to the Hivites, "What if you live among us. How could we make a covenant with you?"
Mutanen Isra’ila kuwa suka ce wa Hiwiyawa, “Wataƙila kuna kusa da mu, ta yaya za mu yi alkawari da ku?”
8 They said to Joshua, "We are your servants." Joshua said to them, "Who are you? Where do you come from?"
Suka ce wa Yoshuwa, “Mu bayinku ne.” Amma Yoshuwa ya tambaye su ya ce, “Ku wane ne, kuma daga ina kuka zo?”
9 They said to him, "Your servants have come from a very far country because of the name of YHWH your God; for we have heard of his fame, all that he did in Egypt,
Suka amsa suka ce, “Bayinka sun zo ne daga ƙasa mai nisa gama Ubangiji Allahnka ya yi suna sosai. Gama mun ji labarin abubuwan da ya yi. Dukan abubuwan da ya yi a Masar
10 and all that he did to the two kings of the Amorites who were beyond the Jordan, to Sihon king of Heshbon and to Og king of Bashan, who was at Ashtaroth.
da kuma duk abubuwan da ya yi wa sarakuna biyu na Amoriyawa gabas da Urdun, Sihon sarkin Heshbon, da Og sarkin Bashan wanda ya yi mulki a Ashtarot.
11 Our elders and all the inhabitants of our country spoke to us, saying, 'Take provision in your hand for the journey, and go to meet them, and tell them, "We are your servants. Now make a covenant with us."'
Dattawanmu da duk mazaunan ƙasar, suka ce mana, ‘Ku ɗauki abincin tafiyar da za ku riƙe; ku je ku same su ku ce musu, “Mu bayinku ne, ku yi alkawari da mu.”’
12 This our bread we took hot for our provision out of our houses on the day we went out to go to you; but now, look, it is dry, and has become moldy.
Abincin tafiyan nan namu yana da ɗumi lokacin da muka kintsa tashi daga gida a ranar da za mu kama hanya zuwa wurinku. Amma yanzu duba yadda ya bushe, ya yi fumfuna.
13 These wineskins, which we filled, were new; and look, they are torn. These our garments and our shoes have become old because of the very long journey."
Waɗannan salkuna kuma da muka cika ruwan inabi, sababbi ne amma duba yadda suka yayyage. Tufafinmu da takalmanmu duk sun yayyage don doguwar tafiya.”
14 The men sampled their provisions, and did not ask counsel from the mouth of YHWH.
Mutanen Isra’ila suka ɗiba daga cikin abincin tafiyar amma ba su nemi nufin Ubangiji ba.
15 Joshua made peace with them, and made a covenant with them, to let them live. The leaders of the congregation swore to them.
Sa’an nan Yoshuwa ya yi alkawari zaman salama da su, cewa ba zai kashe su ba, sai shugabannin mutanen Isra’ila kuwa suka tabbatar musu da haka ta wurin yin rantsuwa.
16 It happened at the end of three days after they had made a covenant with them, that they heard that they were their neighbors, and that they lived among them.
Kwana uku bayan sun yi alkawari da Gibeyonawa, sai Isra’ilawa suka ji cewa Gibeyonawa maƙwabtansu ne, waɗanda suke zaune kurkusa da su.
17 The children of Israel traveled and came to their cities on the third day. Now their cities were Gibeon, Chephirah, Beeroth, and Kiriath Jearim.
Saboda haka Isra’ilawa suka tashi a rana ta uku suke je biranen mutanen, wato, Gibeyon, Kefira, Beyerot da Kiriyat Yeyarim.
18 The children of Israel did not strike them, because the leaders of the congregation had sworn to them by YHWH, the God of Israel. And the whole congregation murmured against the leaders.
Amma Isra’ilawa ba su kai musu hari ba domin shugabanninsu sun rantse musu da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila. Mutane Isra’ila duka kuwa suka yi gunaguni a kan shugabannin.
19 But all the leaders said to all the congregation, "We have sworn to them by YHWH, the God of Israel; and now therefore we may not touch them.
Amma shugabanni suka amsa musu suka ce, “Mun rantse musu da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, saboda haka ba za mu taɓa su ba yanzu.
20 This we will do to them, and let them live; lest wrath be on us, because of the oath which we swore to them."
Ga abin da za mu yi musu, za mu bar su da rai don kada fushin Allah yă sauka a kanmu gama mun riga mun rantse musu.”
21 And the leaders said to them, "Let them live." So they became wood cutters and drawers of water for all the congregation, and all the congregation did as the leaders had spoken to them.
Suka ƙara da cewa, “Mu bar su da rai, amma bari su zama masu yankan itace da masu ɗibo mana ruwa.” Haka shugabannin suka cika alkawarinsu.
22 Joshua called for them, and he spoke to them, saying, "Why have you deceived us, saying, 'We are very far from you,' when you live among us?
Yoshuwa kuwa ya aika aka kira Gibeyonawa ya ce musu, “Don me kuka ruɗe mu kuka ce, ‘Mun zo ne daga wuri mai nisa,’ bayan kuwa kuna nan kurkusa da mu?
23 Now therefore you are cursed, and some of you will never fail to be bondservants, both wood cutters and drawers of water for the house of my God."
Yanzu ku la’anannu ne. Ba za ku daina zama mana masu yankan itace da kuma masu ɗebo ruwa domin haikalin Allahnmu ba.”
24 They answered Joshua, and said, "Because your servants were certainly told how YHWH your God commanded his servant Moses to give you all the land, and to destroy all the inhabitants of the land from before you. Therefore we were very afraid for our lives because of you, and have done this thing.
Suka amsa wa Yoshuwa suka ce, “An gaya wa bayinka dalla-dalla yadda Ubangiji Allahnka ya umarci bawansa Musa yă ba ka ƙasar duka, ka kuma kashe duk masu zama a cikinta, muka ji tsoro cewa za ka kashe mu shi ya sa muka yi haka.
25 Now, look, we are in your hand. Do to us as it seems good and right to you to do."
Yanzu, a hannunka muke, ka yi duk abin da ka ga ya yi maka kyau.”
26 He did so to them, and delivered them out of the hand of the children of Israel, so that they did not kill them.
Yoshuwa kuwa ya cece su daga hannun Isra’ilawa, har ba su kashe su ba.
27 That day Joshua made them wood cutters and drawers of water for the congregation and for the altar of YHWH, to this day, in the place which he should choose.
A ranar Yoshuwa ya sa Gibeyonawa suka zama masu yankan itace da ɗebo ruwa wa jama’ar Isra’ila da kuma domin haikalin Ubangiji a inda Ubangiji zai zaɓa. Abin da suke ke nan har wa yau.

< Joshua 9 >