< John 21 >
1 After these things, Jesus revealed himself again to the disciples at the sea of Tiberias. He revealed himself this way.
Daga baya Yesu ya sāke bayyana kansa ga almajiransa, a bakin Tekun Tibariya. Ga yadda ya faru.
2 Simon Peter, Thomas called Didymus, Nathanael of Cana in Galilee, and the sons of Zebedee, and two others of his disciples were together.
Siman Bitrus, Toma (wanda ake kira Didaimus), Natanayel daga Kana ta Galili,’ya’yan Zebedi maza, da kuma waɗansu almajirai guda biyu suna tare.
3 Simon Peter said to them, "I'm going fishing." They told him, "We are also coming with you." They went out, and entered into the boat. That night, they caught nothing.
Sai Siman Bitrus ya ce musu, “Za ni kamun kifi,” suka ce, “Za mu tafi tare da kai.” Saboda haka suka fita suka shiga jirgin ruwa, amma a daren nan ba su kama kome ba.
4 But when day had already come, Jesus stood on the beach, yet the disciples did not know that it was Jesus.
Da sassafe, sai ga Yesu tsaye a gaci, amma almajiran ba su gane cewa Yesu ne ba.
5 Jesus therefore said to them, "Children, have you anything to eat?" They answered him, "No."
Sai ya ce musu, “Abokai, kuna da kifi kuwa?” Suka amsa suka ce, “A’a.”
6 He said to them, "Cast the net on the right side of the boat, and you will find some." They cast it therefore, and now they weren't able to draw it in for the multitude of fish.
Ya ce musu, “Ku jefa abin kamun kifinku dama da jirgin ruwan, za ku samu.” Da suka yi haka, sai suka kāsa jawo abin kamun kifin saboda yawan kifi.
7 That disciple therefore whom Jesus loved said to Peter, "It's the Lord." So when Simon Peter heard that it was the Lord, he wrapped his coat around him (for he was naked), and threw himself into the sea.
Sai almajirin da Yesu yake ƙauna ya ce wa Bitrus, “Ai, Ubangiji ne!” Nan da nan da Siman Bitrus ya ji ya ce, “Ai, Ubangiji ne,” sai ya yafa mayafinsa (don dā ma ya tuɓe shi), ya fāɗa cikin ruwan.
8 But the other disciples came in the little boat (for they were not far from the land, but about one hundred yards away), dragging the net full of fish.
Sauran almajiran kuwa suka bi shi cikin jirgin ruwan, janye da abin kamun kifin cike da kifi, don ba su da nisa daga gaci, wajen yadi ɗari ne.
9 So when they got out on the land, they saw a fire of coals there, and fish placed on it, and bread.
Da suka sauka, sai suka ga garwashin wuta a can da kifi a kai, da kuma’yan burodi.
10 Jesus said to them, "Bring some of the fish which you have just caught."
Yesu ya ce musu, “Ku kawo waɗansu kifin da kuka kama yanzu.”
11 Simon Peter went up, and drew the net to land, full of great fish, one hundred fifty-three; and even though there were so many, the net was not torn.
Sai Siman Bitrus ya hau ya jawo abin kamun kifin gaci. Ya cika da manyan kifi, 153, amma duk da yawansun nan abin kamun kifin bai tsintsinke ba.
12 Jesus said to them, "Come and eat breakfast." None of the disciples dared inquire of him, "Who are you?" knowing that it was the Lord.
Yesu ya ce musu, “Ku zo ku karya kumallo.” Ba wani daga cikin almajiran da ya yi karambanin tambayarsa, “Wane ne kai?” Sun san cewa Ubangiji ne.
13 Then Jesus came and took the bread, gave it to them, and the fish likewise.
Yesu ya zo, ya ɗauki burodin ya ba su, haka kuma kifin.
14 This is now the third time that Jesus was revealed to his disciples, after he had risen from the dead.
Wannan fa shi ne sau na uku da Yesu ya bayyana kansa ga almajiransa bayan an tashe shi daga matattu.
15 So when they had eaten their breakfast, Jesus said to Simon Peter, "Simon, son of John, do you love me more than these?" He said to him, "Yes, Lord; you know that I love you." He said to him, "Feed my lambs."
Da suka gama ci, sai Yesu ya ce wa Siman Bitrus, “Siman ɗan Yohanna, kana ƙaunata da gaske fiye da waɗannan?” Ya ce, “I, Ubangiji, ka san cewa ina sonka.” Yesu ya ce, “Ciyar da’ya’yan tumakina.”
16 He said to him again a second time, "Simon, son of John, do you love me?" He said to him, "Yes, Lord; you know that I love you." He said to him, "Tend my sheep."
Har wa yau Yesu ya ce, “Siman ɗan Yohanna, kana ƙaunata da gaske?” Ya amsa ya ce, “I, Ubangiji, ka san cewa ina sonka.” Yesu ya ce, “Lura da tumakina.”
17 He said to him the third time, "Simon, son of John, do you love me?" Peter was grieved because he asked him the third time, "Do you love me?" And he said to him, "Lord, you know everything. You know that I love you." Jesus said to him, "Feed my sheep.
Sau na uku ya ce masa, “Siman ɗan Yohanna, kana ƙaunata?” Sai Bitrus ya ɓata rai saboda Yesu ya tambaye shi sau na uku, “Kana ƙaunata?” Ya ce, “Ubangiji ka san kome duka; ka san cewa, ina ƙaunarka.” Yesu ya ce, “Ciyar da tumakina.
18 Truly I tell you, when you were young, you dressed yourself, and walked where you wanted to. But when you are old, you will stretch out your hands, and another will dress you, and carry you where you do not want to go."
Gaskiya nake faɗa maka, sa’ad da kake saurayi kakan yi wa kanka sutura ka tafi inda ka so; amma sa’ad da ka tsufa za ka miƙa hannuwanka, wani dabam yă yi maka sutura yă kai ka inda ba ka so.”
19 Now he said this, signifying by what kind of death he would glorify God. When he had said this, he said to him, "Follow me."
Yesu ya faɗi wannan ne, don yă nuna irin mutuwar da Bitrus zai yi yă ɗaukaka Allah. Sa’an nan ya ce masa, “Bi ni!”
20 Then Peter, turning around, saw a disciple following. This was the disciple whom Jesus sincerely loved, the one who had also leaned on Jesus' chest at the evening meal and asked, "Lord, who is going to betray You?"
Bitrus ya juya ya ga cewa almajirin nan da Yesu yake ƙauna yana binsu. (Wannan ne ya jingina a jikin Yesu sa’ad da suke cin abincin yamman nan da ya ce, “Ubangiji wane ne zai bashe ka?”)
21 Peter seeing him, said to Jesus, "Lord, what about this man?"
Da Bitrus ya gan shi sai ya ce, “Ubangiji, wannan fa?”
22 Jesus said to him, "If I desire that he stay until I come, what is that to you? You follow me."
Yesu ya amsa ya ce, “Idan na so yă kasance da rai har in dawo, mene ne naka a ciki? Kai dai bi ni.”
23 This saying therefore went out among the brothers, that this disciple would not die. Yet Jesus did not say to him that he would not die, but, "If I desire that he stay until I come, what is that to you?"
Saboda wannan, jita-jita ta bazu a cikin’yan’uwa cewa wannan almajirin ba zai mutu ba. Amma fa Yesu bai ce ba zai mutu ba; shi dai ya ce, “In na so yă kasance da rai har in dawo, mene ne naka a ciki?”
24 This is the disciple who testifies about these things, and wrote these things. We know that his witness is true.
Wannan shi ne almajirin da ya ba da shaida a kan waɗannan abubuwa ya kuma rubuta su. Mun san cewa shaidarsa gaskiya ce.
25 There are also many other things which Jesus did, which if they would all be written, I suppose that even the world itself would not have room for the books that would be written.
Yesu ya yi waɗansu abubuwa da yawa kuma. Da a ce an rubuta kowannensu, na tabbata ko duniya duka ba za tă sami wuri saboda littattafan da za a rubuta ba.