< Jeremiah 5 >

1 "Run back and forth through the streets of Jerusalem, and see now, and know, and seek in the broad places of it, if you can find a man, if there are any who does justly, who seeks truth; and I will pardon her.
“Ku yi ta kai da kawowa a titunan Urushalima, ku dudduba ko’ina ku kuma lura, ku bincika cikin dandalinta. Ko za ku sami mutum guda wanda yake aikata adalci wanda yake kuma son bin gaskiya, sai in gafarta wa wannan birni.
2 Though they say, 'As YHWH lives;' surely they swear falsely."
Ko da yake suna cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye,’ duk da haka suna rantsuwar ƙarya.”
3 YHWH, do your eyes not look on truth? You have stricken them, but they were not grieved. You have consumed them, but they have refused to receive correction. They have made their faces harder than a rock. They have refused to return.
Ya Ubangiji, idanunka ba sa ganin gaskiya? Ka buge su, amma ba su ji zafi ba; ka ragargaza su, amma suka ƙi su gyara. Fuskarsu ta ƙeƙashe fiye da dutse suka ƙi su tuba.
4 Then I said, "Surely these are poor. They are foolish; for they do not know the way of YHWH, nor the law of their God.
Na yi tunani, “Waɗannan ne kawai matalauta; su wawaye ne, gama ba su san hanyar Ubangiji ba, ko abubuwan da Allahnsu yake bukata ba.
5 I will go to the great men, and will speak to them; for they know the way of YHWH, and the law of their God." But these with one accord have broken the yoke, and burst the bonds.
Saboda haka zan tafi wurin shugabanni in yi musu magana; tabbatacce sun san hanyar Ubangiji, da abubuwan da Allahnsu yake bukata.” Amma da nufi guda su ma suka karye karkiyar suka tsintsinke sarƙoƙin.
6 Therefore a lion out of the forest shall kill them, a wolf of the evenings shall destroy them, a leopard shall watch against their cities; everyone who goes out there shall be torn in pieces; because their transgressions are many, and their backsliding is increased.
Saboda haka zaki daga kurmi zai fāɗa musu, kyarkeci kuma daga hamada zai cinye su, damisa za tă yi musu ƙawanya kusa da garuruwansu yă yayyage duk wanda ya kuskura ya fita, gama tawayensu da girma yake jan bayansu kuma yana da yawa.
7 "How can I pardon you? Your children have forsaken me, and sworn by what are no gods. When I had fed them to the full, they committed adultery, and assembled themselves in troops at the prostitutes' houses.
“Me zai sa in gafarta muku?’Ya’yanku sun yashe ni sun yi rantsuwa da allolin da ba alloli ba ne. Na biya musu dukan bukatunsu, duk da haka suka yi zina suka tattaru a gidajen karuwai.
8 They were as fed horses roaming at large: everyone neighed after his neighbor's wife.
An ciyar da su sosai, kamar ƙosassun ingarmu, masu jaraba, kowanne yana haniniya, yana neman matar maƙwabcinsa.
9 Shouldn't I punish them for these things?" says YHWH; "and shouldn't my soul be avenged on such a nation as this?
Ba zan hukunta su saboda wannan ba?” In ji Ubangiji. “Bai kamata in yi ramuwa a kan irin al’ummar nan ba?
10 "Go up on her walls, and destroy; but do not make a full end. Take away her branches; for they are not YHWH's.
“Ku ratsa cikin gonakin inabinta ku cinye su, amma kada ku hallaka su gaba ɗaya. Ku kakkaɓe rassanta, gama waɗannan mutane ba na Ubangiji ba ne.
11 For the house of Israel and the house of Judah have dealt very treacherously against me," says YHWH.
Gidan Isra’ila da gidan Yahuda sun zama marasa aminci gaba ɗaya gare ni” in ji Ubangiji.
12 They have denied YHWH, and said, "It is not he; neither shall evil come on us; neither shall we see sword nor famine.
Sun yi ƙarya a kan Ubangiji; sun ce, “Ba zai yi kome ba! Ba wata masifar da za tă same mu; ba za mu taɓa ganin takobi ko yunwa ba.
13 The prophets shall become wind, and the word is not in them. Thus shall it be done to them."
Annabawa holoƙo ne kawai maganar kuwa ba ta cikinsu; saboda haka bari abin da suke faɗi ya koma kansu.”
14 Therefore thus says YHWH, the God of hosts, "Because you speak this word, look, I will make my words in your mouth fire, and this people wood, and it shall devour them.
Saboda haka ga abin Ubangiji Allah Maɗaukaki yana cewa, “Domin mutanen sun yi waɗannan maganganu, zan mai da maganata a bakinku wuta waɗannan mutane kuwa su zama itacen da za tă ci.
15 Look, I will bring a nation on you from far, house of Israel," says YHWH. "It is a mighty nation. It is an ancient nation, a nation whose language you do not know, neither understand what they say.
Ya gidan Isra’ila,” in ji Ubangiji, “Ina kawo al’umma daga nesa a kanku al’umma ce ta tun dā mai ƙarfin hali, mutane ne da ba ku san harshensu ba, waɗanda ba za ku fahimci abin da suke faɗa ba.
16 Their quiver is an open tomb, they are all mighty men.
Kwarinsu kamar buɗaɗɗen kabari ne; dukansu jarumawa ne.
17 They shall eat up your harvest, and your bread, which your sons and your daughters should eat. They shall eat up your flocks and your herds. They shall eat up your vines and your fig trees. They shall beat down your fortified cities, in which you trust, with the sword.
Za su cinye amfanin gonakinku da abincinku, za su cinye’ya’yanku maza da mata; za su cinye garkunan tumakinku da na awakinku, za su cinye’ya’yan inabinku da na ɓaurenku. Da takobi za su hallaka biranenku masu katanga.
18 "But even in those days," says YHWH, "I will not make a full end with you.
“Amma ko a cikin waɗancan kwanaki,” in ji Ubangiji, “ba zan hallaka ku gaba ɗaya ba.
19 It will happen, when you say, 'Why has YHWH our God done all these things to us?' Then you shall say to them, 'Thus says YHWH, Just like you have forsaken me, and served foreign gods in your land, so you shall serve strangers in a land that is not yours.'
Sa’ad da kuma mutanen suka yi tambaya, ‘Me ya sa Ubangiji Allahnmu ya yi dukan wannan gare mu?’ Sai ka amsa musu, ‘Yadda kuka yashe ni kuka kuma bauta wa baƙin alloli a ƙasarku, haka yanzu za ku bauta wa baƙi a ƙasar da ba taku ba.’
20 "Declare this in the house of Jacob, and publish it in Judah, saying,
“Ka sanar da wannan ga gidan Yaƙub ka yi shelarsa a Yahuda.
21 'Hear now this, foolish people, and without understanding; who have eyes, and do not see; who have ears, and do not hear:
Ku ji wannan, ku wawaye marasa azanci, waɗanda suke da idanu amma ba sa gani, waɗanda suke da kunnuwa amma ba sa ji.
22 Do you not fear me?' says YHWH 'Won't you tremble at my presence, who have placed the sand for the bound of the sea, by a perpetual decree, that it can't pass it? And though its waves toss themselves, yet they can't prevail; though they roar, yet they can't pass over it.'
Bai kamata ku ji tsorona ba?” In ji Ubangiji. “Bai kamata ku yi rawar jiki a gabana ba? Na sa yashi ya zama iyakar teku, madawwamiyar iyakar da ba zai tsallake ba. Raƙuman ruwa za su iya yin hauka, amma ba za su iya haye ta ba; za su iya yin ruri, amma ba za su iya ƙetare ta ba.
23 "But this people has a revolting and a rebellious heart; they have revolted and gone.
Amma mutanen nan suna da tauraren zukata, kuma’yan tawaye ne; sun kauce suka kuma rabu da ni.
24 Neither do they say in their heart, 'Let us now fear YHWH our God, who gives rain, both the former and the latter, in its season; who preserves to us the appointed weeks of the harvest.'
Ba sa faɗa wa kansu, ‘Bari mu ji tsoron Ubangiji Allahnmu, wanda yake ba mu ruwan sama a kan kari na kaka da na bazara, wanda kullum yake tabbatar mana da girbi.’
25 "Your iniquities have turned away these things, and your sins have withheld good from you.
Laifofinku sun raba ku da waɗannan abubuwa; zunubanku sun hana ku samun alheri.
26 For among my people are found wicked men. They watch, as fowlers lie in wait. They set a trap. They catch men.
“A cikin mutanena an sami mugaye waɗanda suke kwanton ɓauna kamar masu sa tarko wa tsuntsaye kamar waɗanda suke kafa tarko don su kama mutane.
27 As a cage is full of birds, so are their houses full of deceit. Therefore they have become great, and grew rich.
Kamar keji cike da tsuntsaye, gidajensu sun cika da ruɗu; sun yi arziki suka kuma zama masu iko
28 They have grown fat. They shine; yes, they excel in deeds of wickedness. They do not plead the cause, the cause of the fatherless, that they may prosper; and they do not judge the right of the needy.
suka kuma yi ƙiba, suka yi bul-bul. Mugayen ayyukansu ba su da iyaka; ba sa wa marayu shari’ar adalci, ba sa kāre’yancin matalauta.
29 "Shall I not punish for these things?" says YHWH. "Shall not my soul be avenged on such a nation as this?
Bai kamata in hukunta su saboda wannan ba?” In ji Ubangiji. “Bai kamata in yi ramuwa a kan irin al’umma kamar wannan ba?
30 "An astonishing and horrible thing has happened in the land.
“Abin banmamaki da bantsoro ya faru a ƙasar.
31 The prophets prophesy falsely, and the priests rule by their own authority; and my people love to have it so. What will you do in the end of it?
Annabawa suna annabcin ƙarya, firistoci suna mulki da ikon kansu, mutanena kuma suna son haka. Amma me za ku yi a ƙarshe?

< Jeremiah 5 >