< Genesis 45 >

1 Then Joseph could no longer control himself before all those who stood before him, so he cried out, "Send everyone away from me." So no one stood with him while Joseph made himself known to his brothers.
Yusuf bai ƙara iya daurewa a gaban dukan masu yi masa hidima ba, sai ya yi kuka da ƙarfi ya ce, “Kowa yă tashi daga gabana!” Saboda haka ba kowa a wurin sa’ad da Yusuf ya sanar da kansa ga’yan’uwansa.
2 And he wept so loudly that the Egyptians heard it, and the house of Pharaoh heard about it.
Sai ya yi kuka da ƙarfi har Masarawa suka ji, har labarin ya kai gidan Fir’auna.
3 Then Joseph said to his brothers, "I am Joseph. Is my father still alive?" But his brothers couldn't answer him, for they were terrified at his presence.
Yusuf kuwa ya ce wa’yan’uwansa, “Ni ne Yusuf! Mahaifina yana nan da rai har yanzu?” Amma’yan’uwansa ba su iya amsa masa ba, gama sun firgita ƙwarai a gabansa.
4 Then Joseph said to his brothers, "Come near to me, please." So they moved closer. And he said, "I am Joseph, your brother, whom you sold into Egypt.
Sa’an nan Yusuf ya ce wa’yan’uwansa, “Ku zo kusa da ni.” Da suka yi haka, sai ya ce, “Ni ne ɗan’uwanku Yusuf, wannan da kuka sayar zuwa Masar!
5 Now do not be upset or angry with yourselves that you sold me here, for God sent me before you to preserve life.
Yanzu dai, kada ku damu, kada kuma ku yi fushi da kanku saboda kun sayar da ni a nan, gama Allah ya aiko ni gabanku ne don in ceci rayuka.
6 For the famine has been in the land these two years, and there will be five more years in which there will be neither plowing nor harvest.
Ga shi shekaru biyu ke nan ake yunwa a ƙasar, kuma da sauran shekara biyar masu zuwa da ba za a yi noma ko girbi ba.
7 God sent me ahead of you to preserve for you a remnant on the earth, and to save your lives by a great deliverance.
Amma Allah ya aiko ni gabanku ne don in adana muku raguwa a duniya, in kuma ceci rayukanku ta wurin ceto mai girma.
8 So now, it wasn't you who sent me here, but God, and he has made me a father to Pharaoh, lord of all his house, and ruler over all the land of Egypt.
“Saboda haka fa, ba ku ba ne kuka aiko ni nan, Allah ne. Ya mai da ni mahaifi ga Fir’auna, shugaban dukan gidansa da kuma mai mulkin dukan Masar.
9 Now hurry and go up to my father and tell him, 'This is what your son Joseph says, "God has made me lord of all Egypt. Come down to me. Do not delay.
Yanzu sai ku gaggauta zuwa wurin mahaifina ku faɗa masa, ‘Abin da ɗanka Yusuf ya ce; Allah ya mai da ni shugaban dukan Masar. Gangaro wurina; kada ka jinkirta.
10 You shall dwell in the land of Gesen, and you will be near to me, you, your children, and your children's children, and your flocks, and your herds, and everything that you have.
Za ka yi zama a yankin Goshen, ka kasance kusa da ni. Kai,’ya’yanka da kuma jikokinka, garkunanka da shanunka, da kuma dukan abin da kake da shi.
11 There I will provide for you, for there are still five years of famine to come, otherwise you and your household and all that you have would become destitute.
Zan tanada maka a nan, domin akwai saura shekaru biyar na yunwa masu zuwa. In ba haka ba, kai da gidanka da dukan mallakarka za ku zama gajiyayyu.’
12 Look, your eyes see, and the eyes of my brother Benjamin, that it is my mouth which is speaking to you.
“Ku kanku kun gani, haka ma ɗan’uwana Benyamin, cewa tabbatacce ni ne nake magana da ku.
13 So you must tell my father about all my glory in Egypt, and of all that you have seen. But you must hurry and bring my father down here."
Faɗa wa mahaifina game da dukan girman da aka ba ni a Masar, da kuma game da kome da kuka gani. Ku kuma kawo mahaifina a nan da sauri.”
14 Then he threw his arms around his brother Benjamin's neck and wept, and Benjamin wept on his shoulder.
Sa’an nan ya rungume ɗan’uwansa Benyamin ya yi kuka, sai Benyamin ya rungume shi yana kuka.
15 And he kissed all his brothers and wept on them, and after that his brothers talked with him.
Ya sumbaci dukan’yan’uwansa, ya kuma yi kuka a kansu. Bayan haka sai’yan’uwansa suka yi masa magana.
16 Now the report of it was heard in Pharaoh's house, saying, "Joseph's brothers have come." It pleased Pharaoh and his servants.
Sa’ad da labarin ya kai fadan Fir’auna cewa’yan’uwan Yusuf sun zo, sai Fir’auna da dukan hafsoshin suka ji daɗi.
17 And Pharaoh said to Joseph, "Tell your brothers, 'Do this: Load your animals and go. Enter the land of Canaan.
Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Faɗa wa’yan’uwanka, ‘Yi wannan; ku jibge dabbobinku ku koma zuwa ƙasar Kan’ana,
18 Take your father and your families and come to me, and I will give you the best of the land of Egypt, and you will eat the richness of the land.'
Ku kawo mahaifinku da iyalanku zuwa wurina. Zan ba ku mafi kyau na ƙasar Masar, za ku kuwa ci moriyar ƙasar.’
19 Now you are commanded, 'Do this: Take wagons from the land of Egypt for your little ones, and for your wives, and bring your father and come.
“An kuma umarce ka, ka faɗa musu, ‘Ku yi wannan, ku ɗauki wagonu daga Masar domin’ya’yanku da matanku, ku ɗauki mahaifinku ku zo.
20 Also, do not worry about your possessions, for the best of all of the land of Egypt is yours."
Kada ku damu da mallakarku, gama mafi kyau na Masar za su zama naku.’”
21 So the sons of Israel did that. And Joseph gave them wagons, according to the commandment of Pharaoh, and gave them provisions for the journey.
Sai’ya’yan Isra’ila maza suka yi haka. Yusuf ya ba su wagonu kamar yadda Fir’auna ya umarta, ya kuma ba su guzuri don tafiyarsu.
22 He gave to all of them, to each one, a change of clothing. But to Benjamin he gave three hundred pieces of silver and five changes of clothing.
Ya ba da sababbin riguna ga kowannensu amma ga Benyamin ya ba shi shekel ɗari uku na azurfa da riguna kashi biyar.
23 To his father he sent the following: ten donkeys loaded with the best things of Egypt, and ten female donkeys loaded with grain and food and provision for his father on the journey.
Ga kuma abin da ya aika wa mahaifinsa, jakuna goma da aka jibge da abubuwa mafi kyau na Masar, da jakuna mata guda goma ɗauke da hatsi da burodi da waɗansu tanade-tanade don tafiyarsa.
24 So he sent his brothers off, and as they departed he said to them, "Do not be fearful on the journey."
Sa’an nan ya sallami’yan’uwansa, yayinda suke barin wurin ya ce musu, “Kada ku yi faɗa a hanya!”
25 So they went up out of Egypt and came into the land of Canaan to their father Jacob.
Saboda haka suka haura, suka fita daga Masar, suka zo wurin maihaifinsu Yaƙub a ƙasar Kan’ana.
26 And they told him, saying, "Joseph is still alive, and he is ruler over all the land of Egypt." But he was unmoved, because he did not believe them.
Suka faɗa masa, “Yusuf yana da rai! Gaskiya, shi ne mai mulkin dukan Masar.” Gaban Yaƙub ya fāɗi, domin bai gaskata su ba.
27 But when they told him all the words of Joseph, which he had said to them, and when he saw the wagons which Joseph had sent to transport him, the spirit of their father Jacob revived.
Amma sa’ad da suka faɗa masa kome da Yusuf ya faɗa musu, da kuma sa’ad da ya ga wagonun da Yusuf ya aika don a ɗauke shi a kai da shi can, sai ya farfaɗo, ya dawo cikin hankalinsa.
28 Then Israel said, "I'm convinced. My son Joseph is still alive. I will go and see him before I die."
Sai Yaƙub ya ce, “Na yarda! Ɗana Yusuf yana da rai har yanzu. Zan tafi in gan shi kafin in mutu.”

< Genesis 45 >