< Daniel 5 >

1 Belshazzar the king made a great feast to a thousand of his lords, and drank wine before the thousand.
Sarki Belshazar ya yi babban biki domin dubban hakimansa ya kuma sha ruwan inabi tare da su.
2 Belshazzar, while he tasted the wine, commanded to bring the golden and silver vessels which Nebuchadnezzar his father had taken out of the temple which was in Jerusalem; that the king and his lords, his wives and his secondary wives, might drink from them.
Yayinda Belshazar yake shan ruwan inabi, sai ya umarta a kawo zinariya da azurfan da Nebukadnezzar mahaifinsa ya kwaso daga haikali a Urushalima, saboda sarki da hakimansa, da matansa da ƙwarƙwaransa su sha da su.
3 Then they brought the gold and silver vessels that were taken out of the temple of the house of God which was at Jerusalem; and the king and his lords, his wives and his secondary wives, drank from them.
Sai suka kawo kayan zinariyan nan da aka kwaso daga haikalin Allah a Urushalima, sarki kuwa da hakimansa, da matansa, da ƙwarƙwaransa suka yi ta sha da su.
4 They drank wine, and praised the gods of gold, and of silver, of bronze, of iron, of wood, and of stone.
Yayinda suke shan ruwan inabin, sai suka yabi allolin zinariya da azurfa, da na tagulla, da na ƙarfe, da na itace da kuma na dutse.
5 In the same hour came forth the fingers of a man's hand, and wrote over against the lampstand on the plaster of the wall of the king's palace: and the king saw the part of the hand that wrote.
Nan da nan sai ga yatsotsin hannun mutum sun bayyana, suna yin rubutu a kan shafen bangon, kusa da wurin da ake ajiye fitilar fadar sarki. Sarki kuwa yana ganin hannun yayinda yake rubutu.
6 Then the king's face was turned pale, and his thoughts troubled him; and the joints of his thighs gave way, and his knees began knocking together.
Sai fuskarsa ta ruɗe, ya kuma ji tsoro ƙwarai har gwiwoyinsa suka yi ta bugun juna, ƙafafunsa kuma suka rasa ƙarfi.
7 The king cried aloud to bring in the enchanters, the Chaldeans, and the diviners. The king spoke and said to the wise men of Babylon, "Whoever shall read this writing, and show me its interpretation, shall be clothed with purple, and have a chain of gold about his neck, and shall be the third ruler in the kingdom."
Sai sarki ya kira masu dabo, masanan taurari da masu duba, a kawo su, ya kuma ce wa masu hikima na Babilon, “Duk wanda ya karanta wannan rubutu ya kuma faɗa mini abin da yake nufi, za a sa masa rigar shunayya, a kuma sa masa sarƙar zinariya a wuyansa, zai zama na uku a cikin masu mulkin ƙasar.”
8 Then came in all the king's wise men; but they could not read the writing, nor make known to the king the interpretation.
Sa’an nan sai dukan masu hikima suka zo ciki, amma ba su iya karanta rubutun ba ko su faɗa wa sarki abin da yake nufi.
9 Then was king Belshazzar greatly troubled, and his face turned pale, and his lords were perplexed.
Saboda haka Sarki Belshazar ya firgita ƙwarai kuma fuskarsa ta ƙara ruɗewa. Hakimansa kuma suka rikice.
10 Now the queen by reason of the words of the king and his lords came into the banquet house. The queen spoke and said, "O king, live forever; do not let your thoughts trouble you, nor let your face be changed.
Sai sarauniya, da jin muryoyi na sarki da na hakimansa, ta shiga babban ɗakin liyafar. Ta ce, “Ya sarki, ranka yă daɗe! Kada ka firgita! Kada fuskarka ta ruɗe!
11 There is a man in your kingdom, in whom is the spirit of the holy gods; and in the days of your father light and understanding and wisdom, like the wisdom of the gods, were found in him; and king Nebuchadnezzar your father, your father the king, made him chief of the magicians, enchanters, Chaldeans, and diviners;
Akwai wani mutum a masarautarka wanda yake da ruhun alloli masu tsarki a cikinsa. A zamanin mahaifinka an gane cewa yana da basira da hazaka da hikima kamar na alloli. Sarki Nebukadnezzar mahaifinka, mahaifinka sarki, na ce, ya naɗa shugaban masu dabo, da masu sihiri, masanan taurari da kuma masu duba.
12 because an extraordinary spirit, and knowledge, and understanding to interpret dreams, explain riddles, and solve knotty problems were found in this Daniel, whom the king named Belteshazzar. Now let Daniel be called, and he will show the interpretation."
Wannan mutum Daniyel, wanda sarki ya kira Belteshazar, an gane yana da ruhu nagari, da ilimi, da ganewa don yin fassarar mafarkai, da bayyana ma’anar kacici-kacici, da warware al’amura masu wuya. Ka kira Daniyel shi kuwa zai faɗa maka abin da rubutun nan yake nufi.”
13 Then was Daniel brought in before the king. The king spoke and said to Daniel, "Are you that Daniel, who are of the children of the captivity of Judah, whom the king my father brought out of Judah?
Saboda haka aka kawo Daniyel a gaban sarki, sai sarki ya ce masa, “Kai ne Daniyel ɗin nan, ɗaya daga cikin kamammu waɗanda mahaifina sarki ya kawo daga Yahuda?
14 I have heard of you, that the spirit of the gods is in you, and that light and understanding and extraordinary wisdom are found in you.
Na sami labari cewa kana da ruhun alloli a cikinka da kuma basira, da hazaka da kuma fitacciyar hikima.
15 Now the wise men, the enchanters, have been brought in before me, that they should read this writing, and make known to me its interpretation; but they could not show the interpretation of the thing.
An kawo masu hikima da masu dabo a gabana domin su karanta wannan rubutu su kuma faɗa mini abin da yake nufi, amma ba su iya ba.
16 But I have heard of you, that you can give interpretations, and solve problems. Now if you can read the writing, and make known to me its interpretation, you shall be clothed with purple, and have a chain of gold about your neck, and shall be the third ruler in the kingdom."
Na sami labari cewa kana iya ba da fassara da kuma warware matsaloli masu wuya. In har ka iya karanta wannan rubutun ka kuma faɗa mini abin da yake nufi, za a sa maka riga shunayya, a kuma sa sarƙar zinariya a wuyanka. Za ka zama na uku a cikin masu mulkin ƙasar.”
17 Then Daniel answered before the king, "Keep your gifts for yourself, and give your rewards to another; Nevertheless I will read the writing to the king, and make known to him the interpretation.
Sai Daniyel ya amsa wa sarki ya ce, “Za ka iya ajiye kyautar wa kanka ko kuma ka ba wa wani. Duk da haka, zan karanta wa sarki rubutun, in kuma faɗa abin da yake nufi.
18 You king, the Most High God gave Nebuchadnezzar your father the kingdom, and greatness, and glory, and majesty.
“Ya sarki, Allah Mafi Ɗaukaka ya ba mahaifinka Nebukadnezzar sarauta, da girma, da ɗaukaka, da martaba.
19 And because of the greatness that he gave him, all the peoples, nations, and languages trembled and feared before him. Whom he would he killed, and whom he would he kept alive; and whom he would he raised up, and whom he would he put down.
Saboda irin matsayin da ya ba shi, dukan mutane da al’ummai da kuma dukan harsuna suka ji tsoronsa suka yi rawar jiki a gabansa. Bisa ga ganin damarsa yakan kashe wani, ya bar wani da rai, haka kuma yakan ɗaukaka wani, ya ƙasƙantar da wani.
20 But when his heart was lifted up, and his spirit was hardened so that he dealt proudly, he was removed from his kingly throne, and they took his glory from him.
Amma da lokacin da zuciyarsa ta cika da girman kai ta kuma taurare, sai aka kore shi daga gadon sarautarsa, aka raba shi kuma da darajarsa.
21 And he was driven from the sons of men, and his mind was made like the animals', and his dwelling was with the wild donkeys. He was fed with grass like oxen, and his body was wet with the dew of the sky; until he knew that the Most High God rules in the kingdom of men, and that he sets up over it whomever he wants.
Aka kore shi daga cikin mutane aka kuma ba shi tunani irin na dabba; ya yi zama tare da jakunan jeji, ya kuma ci ciyawa kamar shanu; jikinsa kuma ya jiƙe da raɓa, har zuwa lokacin da ya gane, ashe, Allah Maɗaukaki ne mai iko duka a kan dukan mulkoki a duniya, yake kuma ba da mulki ga duk wanda ya ga dama.
22 You his son, Belshazzar, have not humbled your heart, though you knew all this,
“Amma kai ɗansa, Ya Belshazar, ba ka ƙasƙantar da kanka ba, ko da yake ka san wannan duka.
23 but have lifted up yourself against the Lord of heaven. And they have brought the vessels of his house before you, and you and your lords, your wives and your secondary wives, have drunk wine from them. And you have praised the gods of silver and gold, of bronze, iron, wood, and stone, which do not see, nor hear, nor know. And the God in whose hand your breath is, and whose are all your ways, you have not glorified.
A maimakon, sai ka nuna wa Ubangiji na sama girman kai. Ka sa aka kawo maka su kwaf na zinariya daga haikalinsa, da kai da hakimanka, da matanka da ƙwarƙwaranka kuka sha ruwan inabi da su. Kuka yabi allolin zinariya da na azurfa, da na tagulla, da na baƙin ƙarfe, da na itace, da na dutse waɗanda ba sa ji, ba sa gani, ba sa da gane kome. Amma ba ka girmama Allah ba, wanda ranka da dukan harkokinka suna a hannunsa.
24 Then was the part of the hand sent from before him, and this writing was inscribed.
Saboda haka ya aiko da hannun da ya yi rubutun nan.
25 This is the writing that was inscribed: MENE, MENE, TEKEL, UPHARSIN.
“Wannan shi ne rubutun da aka yi, Mene, mene, tekel, farsin
26 This is the interpretation of the thing: MENE; God has numbered your kingdom, and brought it to an end;
“Abin da kalmomin nan suke nufi shi ne, “Mene, Allah ya ƙayyade yawan kwanakin mulkinka ya kuma kawo su ga ƙarshe.
27 TEKEL; you are weighed in the balances, and are found wanting.
“Tekel, An kuma auna ka a ma’auni aka tarar ka kāsa.
28 PERES; your kingdom is divided, and given to the Medes and Persians."
“Feres, An raba mulkinka aka ba wa Medes da Farisa.”
29 Then commanded Belshazzar, and they clothed Daniel with purple, and put a chain of gold about his neck, and made proclamation concerning him, that he should be the third ruler in the kingdom.
Sai Belshazar ya umarta, aka sa wa Daniyel riga mai shunayya, aka sa sarƙar zinariya a wuyansa, aka kuma yi shela, cewa yanzu shi ne na uku a cikin masu mulkin ƙasar.
30 In that night Belshazzar the Chaldean King was slain.
A wannan dare aka kashe Belshazar, sarkin Babiloniyawa,
31 Daryavesh the Mede received the kingdom, being about sixty-two years old.
Dariyus mutumin Medes kuwa ya karɓi mulkin, yana da shekara sittin da biyu.

< Daniel 5 >