< 2 Corinthians 11 >
1 I wish that you would bear with me in a little foolishness, but indeed you do bear with me.
Ina fata za ku yi haƙuri da’yar wautata. Amma, ai, kun riga kun yi haƙuri.
2 For I am jealous over you with a godly jealousy. For I married you to one husband, that I might present you as a pure virgin to Christ.
Ina kishinku da kishi irin na Allah. Na yi muku alkawarin aure ga miji ɗaya, Kiristi, domin in miƙa ku a gare shi kamar budurwa zalla.
3 But I am afraid that somehow, as the serpent deceived Eve in his craftiness, so your minds might be corrupted from the sincerity and purity that is in Christ.
Sai dai ina tsoro kada yă zama, kamar yadda maciji ya yaudari Hawwa’u da makircinsa, ku ma a bauɗar da hankalinku daga sahihiyar biyayya amintacciya ga Kiristi.
4 For if he who comes preaches another Jesus, whom we did not preach, or if you receive a different spirit, which you did not receive, or a different "good news", which you did not accept, you put up with that well enough.
Gama in wani ya zo wurinku yana wa’azin wani Yesu dabam da wanda muka yi wa’azinsa, ko kuma in kun karɓi wani ruhu dabam da wanda kuka karɓa, ko wata bishara dabam da wadda kuka karɓa, ya nuna kun yarda da su ke nan cikin sauƙinkai.
5 For I reckon that I am not at all behind the very best apostles.
Amma a ganina waɗancan da kuke ce da su “manyan manzanni” ba su fi ni da wani abu ba.
6 Even though I am unskilled in speech, I am not unskilled in knowledge. But in every way we have made this known to you in all things.
Mai yiwuwa ni ba horarre ba ne a magana, amma ina da sani. Mun kuwa bayyana muku wannan a sarari, ta kowace hanya.
7 Or did I commit a sin in humbling myself that you might be exalted, because I preached to you God's Good News free of charge?
Laifi ke nan ne na yi da na ƙasƙantar da kaina, don a ɗaga ku zuwa babban matsayi ta wurin yin muku wa’azin bisharar Allah kyauta?
8 I robbed other churches, taking wages from them that I might serve you.
Na yi wa waɗansu ikkilisiyoyi ƙwace ta wurin karɓar taimako daga wurinsu, domin in yi muku hidima.
9 When I was present with you and was in need, I was not a burden on anyone, for the brothers, when they came from Macedonia, supplied the measure of my need. In everything I kept myself from being burdensome to you, and I will continue to do so.
Sa’ad da nake tare da ku kuma nake zaman rashi, ban nawaita wa kowa ba, gama’yan’uwan da suka zo daga Makidoniya sun biya bukata. Na kiyaye kaina daga nawaita muku ta kowace hanya, zan kuma ci gaba da yin haka.
10 As the truth of Christ is in me, no one will stop me from this boasting in the regions of Achaia.
Ba shakka, kamar yadda gaskiyar Kiristi take a cikina, babu wani a yankunan Akayya da zai iya hana yin taƙaman nan tawa.
11 Why? Because I do not love you? God knows.
Don me? Don ba na ƙaunar ku ne? Allah dai ya sani ina ƙaunarku!
12 But what I do, that I will do, that I may cut off occasion from them that desire an occasion, that in which they boast, they may be found even as we.
Zan kuma ci gaba da yin abin da nake yi, domin in toshe kafar mutanen nan da suke fariya, suna nema mu daidaita da su.
13 For such people are false apostles, deceitful workers, masquerading as Christ's apostles.
Gama irin waɗannan mutane manzannin ƙarya ne, ma’aikata ne masu ruɗi, sun ɓad da kamanni kamar su manzannin Kiristi ne.
14 And no wonder, for even Satan masquerades as an angel of light.
Ba abin mamaki ba ne, gama Shaiɗan kansa ma yana ɓad da kamanni kamar shi mala’ikan haske ne.
15 It is no great thing therefore if his servants also masquerade as servants of righteousness, whose end will be according to their works.
Don haka, ba abin mamaki ba ne, in bayin Shaiɗan sun ɓad da kamanni kamar su bayin adalci ne. A ƙarshe, za a sāka musu gwargwadon ayyukansu.
16 I say again, let no one think me foolish. But if so, yet receive me as foolish, that I also may boast a little.
Ina sāke faɗa, kada wani yă ɗauka ni wawa ne. Amma in kun ɗauke ni haka, to, sai ku karɓe ni kamar yadda kuke karɓan wawa, domin in ɗan in yi taƙama.
17 That which I speak, I do not speak according to the Lord, but as in foolishness, in this confidence of boasting.
A wannan taƙamata ba na magana yadda Ubangiji zai yi ba ne, sai dai magana ce irin ta wawa.
18 Seeing that many boast after the flesh, I will also boast.
Da yake mutane da yawa suna taƙama irin ta duniya, ni ma haka zan yi.
19 For you bear with the foolish gladly, being wise.
Ku kam kuna da wayo sosai, har kuna jimre wa wawaye da murna!
20 For you put up with it if someone makes slaves of you, if someone exploits you, if someone takes advantage of you, if someone exalts himself, if someone strikes you on the face.
Gaskiyar ita ce, kuna haƙuri da duk wanda ya sa ku bauta ko ya cuce ku ko ya more ku ko ya nuna muku isa ko kuma ya mare ku a fuska.
21 I speak by way of disparagement, as though we had been weak. Yet however any is bold (I speak in foolishness), I am bold also.
Ina jin kunya in ce mun nuna kāsawa da ba mu yi waɗannan abubuwan ba! Abin da wani yake da ƙarfin hali yin taƙama a kai, shi ne ni ma nake ƙarfin hali yin taƙama a kai. Ina magana kamar wawa ne.
22 Are they Hebrews? So am I. Are they Israelites? So am I. Are they descendants of Abraham? So am I.
In su Ibraniyawa ne, ni ma haka. In su Isra’ilawa ne, ni ma haka. In su zuriyar Ibrahim ne, ni ma haka.
23 Are they servants of Christ? (I speak as one beside himself) I am more so; in labors more abundantly, in prisons more abundantly, in stripes above measure, in deaths often.
In su bayin Kiristi ne, ni na fi su ma, ina magana kamar ruɗaɗɗe ne fa! Ai, na fi su shan fama ƙwarai da gaske, da shan dauri, na sha dūka marar iyaka, na sha hatsarin mutuwa iri-iri.
24 Five times from the Jews I received forty stripes minus one.
Sau biyar Yahudawa suka yi mini bulala arba’in ɗaya babu.
25 Three times I was beaten with rods. Once I was stoned. Three times I suffered shipwreck. I have been a night and a day in the deep.
Sau uku aka bulale ni da bulalar ƙarfe, sau ɗaya aka jajjefe ni da duwatsu, sau uku jirgin ruwa ya ragargaje ina ciki, na kwana na kuma yini ruwan teku yana tafiya da ni.
26 I have been in travels often, perils of rivers, perils of robbers, perils from my countrymen, perils from those who are not Jews, perils in the city, perils in the wilderness, perils in the sea, perils among false brothers;
Na yi tafiye-tafiye da yawa, na sha hatsari a koguna, na sha hatsarin’yan fashi, na sha hatsari a hannun kabilarmu, na sha hatsari a hannun al’ummai, na sha hatsari a birane, na sha hatsari a jeji, na sha hatsari a teku, na kuma sha hatsarin’yan’uwa na ƙarya.
27 in labor and travail, in watchings often, in hunger and thirst, in fastings often, and in cold and nakedness.
Na yi fama, na shan wuya, ga kuma rashin barci sau da yawa. Na san abin da ake nufin da jin yunwa da ƙishirwa, sau da yawa kuwa na kasance da rashin abinci, na sha sanyi da zaman tsirara.
28 Besides those things that are outside, there is that which presses on me daily, anxiety for all the churches.
Ban da waɗannan abubuwa, kowace rana ina ɗauke da nauyin kula da dukan ikkilisiyoyi.
29 Who is weak, and I am not weak? Who is caused to stumble, and I do not burn with indignation?
Wane ne ya rasa ƙarfi, da ban ji shi a jikina ba? Wane ne ya fāɗi cikin zunubi, da ban ji zafin wannan ba?
30 If I must boast, I will boast of the things that concern my weakness.
In ma lalle ne in yi taƙama, to, sai in yi taƙama da abubuwan da suka nuna rashin ƙarfina.
31 The God and Father of the Lord Jesus, he who is blessed forevermore, knows that I do not lie. (aiōn )
Allah Uban Ubangiji Yesu Kiristi, wanda yabo ta tabbata a gare shi har abada, ya san cewa ba ƙarya nake yi ba. (aiōn )
32 In Damascus the governor under Aretas the king guarded the city of the Damascenes, desiring to arrest me.
A Damaskus, gwamnan da yake ƙarƙashin Sarki Aretas, ya sa tsare ƙofofin birnin Damaskus, don yă kama ni.
33 Through a window I was let down in a basket by the wall, and escaped his hands.
Amma aka saukar da ni cikin kwando ta tagar katanga, na kuɓuce masa.