< 1 Chronicles 11 >

1 Then all Israel gathered together to David at Hebron, saying, "Look, we are your bone and your flesh.
Dukan Isra’ila fa suka taru wurin Dawuda a Hebron suka ce, “Mu jiki da jininka ne.
2 In times past, even when Saul was king, it was you who led out and brought in Israel. YHWH your God said to you, 'You shall be shepherd of my people Israel, and you shall rule over my people Israel.'"
A dā, ko a lokacin da Shawulu yake sarki, ai, kai ne kake shugabantar Isra’ila a yaƙe-yaƙe. Kuma Ubangiji Allahnka ya ce maka, ‘Za ka zama makiyayin mutanena Isra’ila, za ka kuma zama mai mulkinsu.’”
3 So all the elders of Israel came to the king to Hebron; and David made a covenant with them in Hebron before YHWH; and they anointed David king over Israel, according to the word of YHWH by Samuel.
Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka zo wurin Sarki Dawuda a Hebron, suka yi yarjejjeniya da shi a gaban Ubangiji, suka kuwa shafe Dawuda ya zama sarki a bisa Isra’ila, yadda Ubangiji ya yi alkawari ta wurin Sama’ila.
4 David and all Israel went to Jerusalem (that is, Jebus); and the Jebusites, the inhabitants of the land, were there.
Dawuda tare da dukan Isra’ilawa suka taka zuwa Urushalima (wato, Yebus). Yebusiyawan da suke zama a wurin
5 The inhabitants of Jebus said to David, "You shall not come in here." Nevertheless David took the stronghold of Zion, that is, the City of David.
suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba.” Duk da haka, Dawuda ya ci kagarar Sihiyona, Birnin Dawuda.
6 David said, "Whoever strikes the Jebusites first shall be chief and captain." Joab the son of Zeruiah went up first, and was made chief.
Dawuda ya ce, “Duk wanda ya jagoranci yaƙi a kan Yebusiyawa zai zama babban shugaban mayaƙa.” Yowab ɗan Zeruhiya ya fara haurawa, ta haka ya zama shugaba.
7 David lived in the stronghold; therefore they called it the City of David.
Dawuda zauna a kagarar, ta haka aka kira ta Birnin Dawuda.
8 He built the city all around, from the Millo even around; and Joab repaired the rest of the city.
Sai ya gina birni kewaye da shi, daga madogaran gini zuwa katangar da take kewaye, yayinda Yowab ya maido da sauran birnin.
9 David grew greater and greater; for YHWH of hosts was with him.
Dawuda kuwa ya ƙara ƙarfi, domin Ubangiji Maɗaukaki yana tare da shi.
10 Now these are the chief of the warriors whom David had, who gave him strong support in his kingdom, together with all Israel, to make him king, according to the word of YHWH concerning Israel.
Waɗannan su ne manyan jarumawan Dawuda, su ne, tare da dukan Isra’ila, suka ba wa mulkinsa goyon baya mai ƙarfi da ya kai bisa dukan ƙasar, yadda Ubangiji ya yi alkawari.
11 This is the number of the warriors whom David had: Jeshbaal the son of Hachmoni, leader of the Three. And he wielded his spear against eight hundred and killed them at one time.
Ga jerin sunayen jarumawan Dawuda. Yashobeyam wani ɗan Hakmoni, shi ne babban shugaba; ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe a ƙarawa guda kawai.
12 After him was Eleazar the son of Dodo, the Ahohite, who was one of the Three warriors.
Biye da shi, shi ne Eleyazar ɗan Dodo mutumin Aho, ɗaya daga cikin jarumawa uku.
13 He was with David at Pas Dammim, and there the Philistines were gathered together to battle, where there was a plot of ground full of barley; and the people fled from before the Philistines.
Yana tare da Dawuda a Fas Dammim sa’ad da Filistiyawa suka taru can don yaƙi. A wani wuri inda akwai gona cike da sha’ir, sojoji suka gudu daga Filistiyawa.
14 And he took his stand in the midst of the plot, and defended it, and killed the Philistines; and YHWH saved them by a great victory.
Sai shi da Dawuda suka shiga gonar sha’ir ɗin, suka tsaya ciki don su tsare ta. Suka ragargaza Filistiyawa, Ubangiji kuma ya kawo babban nasara.
15 And three of the Thirty chief men went down to the rock to David, into the cave of Adullam; and the army of the Philistines were camped in the Valley of Rephaim.
Wata rana uku cikin manyan mutanen nan talatin suka gangara wurin Dawuda zuwa dutse a kogon Adullam, yayinda ƙungiyar Filistiyawa suke sansani a Kwarin Refayim.
16 David was then in the stronghold, and the garrison of the Philistines was then in Bethlehem.
A lokacin Dawuda yana cikin mafaka, sojojin Filistiyawa kuma suna a Betlehem.
17 And David had a craving and said, "Oh that one would give me water to drink of the well of Bethlehem, which is by the gate."
Dawuda ya ji marmarin ruwan sha sai ya ce, “Kash, a ce wani zai sami mini ruwan sha daga rijiya kusa da ƙofar Betlehem mana!”
18 The Three broke through the army of the Philistines, and drew water out of the well of Bethlehem, that was by the gate, and took it, and brought it to David: but David would not drink of it, but poured it out to YHWH,
Sai Ukun suka kutsa kai cikin sansanin Filistiyawa, suka ja ruwa daga rijiyar da take kusa da ƙofar Betlehem suka ɗauko shi suka kawo wa Dawuda. Amma ya ƙi yă sha; a maimako, sai ya zubar da shi a gaban Ubangiji.
19 and said, "My God forbid it me, that I should do this. Shall I drink the blood of these men who have put their lives in jeopardy?" For they risked their lives to bring it. Therefore he would not drink it. The Three warriors did these things.
Ya ce, “Allah yă sawwaƙe in yi haka, ya kamata in sha jinin waɗannan mutanen da suka yi kasai da rayukansu?” Domin sun yi kasai da rayukansu don su dawo da shi, Dawuda bai sha shi ba. Irin abubuwan da jarumawa ukun nan suka yi ke nan.
20 And Abishai, the brother of Joab, was leader of the Thirty. And he wielded his spear against three hundred and killed them, and had a name beside the Three.
Abishai ɗan’uwan Yowab shi ma babba ne cikin Ukun nan. Ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe, ya kuma zama sananne kamar Ukun.
21 He was the most illustrious of the Thirty, and he became their leader. However, he did not attain to the Three.
Aka ninka girmama shi bisa Ukun, sai ya zama shugaba, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
22 Benaiah the son of Jehoiada was a valiant man of Kabzeel, who performed great deeds. He killed the two of Ariel of Moab. He also went down and killed a lion in the midst of a pit in time of snow.
Benahiya ɗan Yehohiyada shi ma wani barden yaƙi ne daga Kabzeyel, wanda ya yi manyan abubuwa. Ya bugi gwanayen Mowab biyu. Ya kuma gangara zuwa cikin rami a ranar da aka yi dusar ƙanƙara ya kashe zaki.
23 He killed an Egyptian, a man of great stature, seven feet five inches tall; and in the Egyptian's hand was a spear like a weaver's beam; and he went down to him with a staff, and grabbed the spear out of the Egyptian's hand, and killed him with his own spear.
Ya kuma kashe wani mutumin Masar mai tsayi ƙafa bakwai da rabi. Ko da yake mutumin Masar yana da māshi kamar sandan masaƙa a hannunsa, Benahiya ya yaƙe shi da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannun mutumin Masar ya kuma kashe shi da māshin nan nasa.
24 Benaiah the son of Jehoiada did these things, and had a name among the Three warriors.
Irin abubuwan da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma sananne ne kamar waɗannan jarumawa uku.
25 Look, he was more honored than the Thirty, but he did not attain to the Three. And David set him over his guard.
Aka ɗauka shi da bangirma fiye da Talatin nan, amma ba a haɗa shi cikin Ukun ba. Dawuda kuwa ya sa shi yă lura da masu tsaron lafiyarsa.
26 Also the warriors of the armies: Asahel the brother of Joab, Elhanan the son of Dodo of Bethlehem,
Jarumawan nan su ne, Asahel ɗan’uwan Yowab, Elhanan ɗan Dodo daga Betlehem,
27 Shammah the Harodite, Elika the Harodite, Helez the Paltite,
Shammot mutumin Haror, Helez mutumin Felon,
28 Ira the son of Ikkesh the Tekoite, Abiezer the Anathothite,
Ira ɗan Ikkesh daga Tekowa, Abiyezer daga Anatot,
29 Sibbekai the Hushathite, Zalmon the Ahohite,
Sibbekai mutumin Husha, Ilai mutumin Aho,
30 Maharai the Netophathite, Heled the son of Baanah the Netophathite,
Maharai mutumin Netofa, Heled ɗan Ba’ana mutumin Netofa,
31 Ithai the son of Ribai of Gibeah of the people of Benjamin, Benaiah the Pirathonite,
Ittai ɗan Ribai daga Gibeya a Benyamin, Benahiya mutumin Firaton,
32 Hiddai of Nahale Gaash, Abiel the Arbathite,
Hurai daga kogunan Ga’ash, Abiyel mutumin Arba,
33 Azmaveth the Bahurimite, Eliahba the Shaalbinite,
Azmawet mutumin Harum, Eliyaba mutumin Sha’albo,
34 Jashen the Gizonite, Jonathan the son of Shamma the Hararite,
’ya’yan Hashem mutumin Gizon maza, Yonatan ɗan Shageye mutumin Harar,
35 Ahiam the son of Sakar the Hararite, Eliphelet the son of Ahasbai the Maacathite,
Ahiyam ɗan Sakar mutumin Harar, Elifal ɗan Ur,
36 Eliam the son of Ahithophel the Gilonite,
Hefer mutumin Mekerat, Ahiya mutumin Felon,
37 Hezrai the Carmelite, Paarai the Archite,
Hezro mutumin Karmel, Na’arai ɗan Ezbai,
38 Igal the son of Nathan, from the elite troops of the Hagrites,
Yowel ɗan’uwan Natan, Mibhar ɗan Hagiri,
39 Zelek the Ammonite, Naharai the Beerothite, the armor bearer of Joab the son of Zeruiah,
Zelek mutumin Ammon Naharai Baroti, mai ɗaukar kayan yaƙin Yowab ɗan Zeruhiya,
40 Ira the Jattirite, Gareb the Jattirite,
Ira mutumin Itra, Gareb mutumin Itra,
41 Uriah the Hethite, Zabad the son of Ahlai,
Uriya mutumin Hitti Zabad ɗan Alai,
42 Adina the son of Shiza the Reubenite, a chief of the Reubenites, and thirty with him,
Adina ɗan Shiza mutumin Ruben, wanda shi ne babba na mutanen Ruben, kuma talatin suna tare da shi,
43 Hanan the son of Maacah, and Joshaphat the Mithnite,
Hanan ɗan Ma’aka, Yoshafat mutumin Mit,
44 Uzzia the Ashterathite, Shama and Jeiel the sons of Hotham the Aroerite,
Uzziya mutumin Ashtarot, Shama da Yehiyel’ya’yan Hotam mutumin Arower maza,
45 Jediael the son of Shimri, and Joha his brother, the Tizite,
Yediyayel ɗan Shimri, ɗan’uwansa Yoha mutumin Tiz,
46 Eliel the Mahavite, and Jeribai, and Joshaviah, the sons of Elnaam, and Ithmah the Moabite,
Eliyel mutumin Ma’aha, Yeribai da Yoshawiya’ya’yan Elna’am maza, Itma mutumin Mowab,
47 Eliel, and Obed, and Jaasiel the Mezobaiah.
Eliyel, Obed da Ya’asiyel mutumin Mezob.

< 1 Chronicles 11 >