< Matthew 14 >
1 At that time, Herod the tetrarch heard the report concerning Jesus,
A lokacin nan ne, Hiridus mai mulki ya ji labarin Yesu.
2 and said to his servants, "This is John the Baptist. He is risen from the dead. That is why these powers work in him."
Ya ce wa barorinsa, “Wannan Yahaya mai baftisma ne; ya tashi daga matattu. Saboda haka wadannan ikoki na aiki a cikinsa”.
3 For Herod had arrested John, and bound him, and put him in prison for the sake of Herodias, his brother Philip's wife.
Domin Hiridus ya kama Yahaya, ya daure shi, kuma ya jefa shi a kurkuku saboda Hirudiya, matar dan'uwansa Filibus.
4 For John said to him, "It is not lawful for you to have her."
Ya ce masa, “Bai kamata ka dauke ta a matsayin matarka ba.”
5 And though he wanted to kill him, he feared the crowd because they regarded him as a prophet.
Da Hirudus ya kashe shi, amma yana tsoron jama'a, domin sun dauke shi a matsayin annabi.
6 But when Herod's birthday came, the daughter of Herodias danced among them and pleased Herod.
Amma da ranar bikin haihuwar Hirudus ta kewayo, diyar Hirudiya tayi rawa a lokacin har ta burge Hirudus.
7 Whereupon he promised with an oath to give her whatever she should ask.
Sai ya yi mata alkawari har da rantsuwa cewa ta roki komenene ta ke so, zai ba ta.
8 And she, being prompted by her mother, said, "Give me here on a platter the head of John the Baptist."
Bayan ta amshi umurni daga wurin mahaifiyarta, ta ce, “Ka bani kan Yahaya mai baptisma a kan tire.
9 And the king was grieved, but for the sake of his oaths, and of those who sat at the table with him, he commanded it to be given,
Sarki ya husata da rokonta, amma domin rantsuwar da ya yi kuma domin mutanen da ke a wurin bukin tare da shi, sai ya umurta a yi haka.
10 and he sent and beheaded John in the prison.
Ya aika aka yanke kan Yahaya acikin kurkuku.
11 And his head was brought on a platter, and given to the young woman: and she brought it to her mother.
Sai aka kawo kansa bisa tire, aka mika wa yarinyar, ta kuwa kai wa mahaifiyarta.
12 Then his disciples came, and took the dead body, and buried him; and they went and told Jesus.
Sai almajiransa suka zo, su ka dauki gawar su ka je su ka yi jana'iza. Bayan haka, su ka je su ka fada wa Yesu.
13 Now when Jesus heard this, he withdrew from there in a boat, to a secluded place to be alone. When the crowds heard it, they followed him on foot from the cities.
Sa'adda da Yesu ya ji haka, ya fita daga cikin kwale-kwale zuwa wani kebabben wuri. Da taron suka ji haka, suka bi shi da kafa daga biranen.
14 And he went out, and he saw a large crowd, and he had compassion on them, and healed their sick.
Sai Yesu ya zo gabansu, ya kuma ga babban taron. Ya tausaya masu ya kuwa warkar da marasa lafiya dake cikinsu.
15 Now when evening had come, the disciples came to him, saying, "This place is desolate, and the hour is already late. Send the crowds away, that they may go into the villages, and buy themselves food."
Da maraice ya yi, almajiransa su ka zo su ka ce masa, “Wannan wuri jeji ne, dare kuwa ya riga ya yi. Ka sallami taron domin su je cikin kauyukan nan, su sayo wa kansu abinci.”
16 But Jesus said to them, "They do not need to go away. You give them something to eat."
Amma Yesu ya ce masu, “Babu amfanin tafiyar su, ku basu abin da za su ci.”
17 And they told him, "We only have here five loaves and two fish."
Suka ce masa, “Muna da gurasa guda biyar da kifi biyu ne kawai.”
18 So he said, "Bring them here to me."
Yesu ya ce, “Ku kawo mani su.”
19 Then he commanded the crowds to sit down on the grass; and he took the five loaves and the two fish, and looking up to heaven, he blessed, broke and gave the loaves to the disciples, and the disciples gave to the crowds.
Sai Yesu ya umarci taron su zauna akan ciyawa. Ya dauki gurasa biyar da kifi biyun. Ya dubi sama, ya sa albarka ya gutsuttsura ya kuma ba almajiran. Almajiran suka ba taron.
20 And they all ate and were filled, and they took up twelve baskets full of that which remained left over from the broken pieces.
Dukansu suka ci suka koshi. Sai suka dauki gutsattsarin gurasa da kifin, kwanduna goma sha biyu cike.
21 Now those who ate were about five thousand men, besides women and children.
Wadanda su ka ci kuwa kimanin maza dubu biyar ne, ban da mata da yara.
22 And immediately he made the disciples get into the boat and to go ahead of him to the other side, while he sent the crowds away.
Nan take sai ya sa almajiran suka shiga kwale-kwalen su haye zuwa dayan gefen kafin shi, domin ya sallami taron.
23 And after he had sent the crowds away, he went up into the mountain by himself to pray. When evening had come, he was there alone.
Bayan ya sallami taron sun tafi, sai ya haura kan dutse domin yayi addu'a. Da dare yayi, yana can shi kadai.
24 But the boat was now in the middle of the sea, battered by the waves, for the wind was against it.
Amma yanzu fa kwale-kwalen na tsakiyar tekun, kuma da wuyar sarrafawa saboda rakuman ruwa da iska na gaba da su.
25 And in the watch between three and six in the morning, he came to them, walking on the sea.
Da asuba (wajen karfe uku na dare) Yesu ya nufo su yana tafiya akan teku.
26 And when the disciples saw him walking on the sea, they were troubled, saying, "It's a ghost." and they screamed with fear.
Da almajiran suka ganshi yana tafiya akan tekun, sai suka firgita suna cewa, “Fatalwa ce,” suka yi kururuwa cikin tsoro.
27 But immediately Jesus spoke to them, saying "Cheer up. It is I. Do not be afraid."
Amma Yesu yayi magana da su nan da nan yace, “Ku yi karfin hali! Ni ne! Kada ku ji tsoro.”
28 Peter answered him and said, "Lord, if it is you, command me to come to you on the waters."
Bitrus ya amsa masa cewa, “Ubangiji, idan kai ne, ka umarce ni in zo wurin ka bisa ruwan.”
29 He said, "Come." Peter stepped down from the boat, and walked on the water and went toward Jesus.
Yesu yace, “Zo” Sai Bitrus ya fita daga jirgin yana tafiya akan ruwan zuwa wurin Yesu.
30 But when he saw the strong wind, he was afraid, and beginning to sink, he yelled, saying, "Lord, save me."
Amma da Bitrus ya ga iska, sai ya tsorata. Yayin da ya fara nutsewa, sai ya tada murya ya ce, “Ubangiji, ka cece ni!”
31 Immediately Jesus stretched out his hand, took hold of him, and said to him, "You of little faith, why did you doubt?"
Nan take Yesu ya mika hannunsa, ya kama Bitrus ya ce masa, “Kai mai karancin bangaskiya, meyasa ka yi shakka?”
32 When they got up into the boat, the wind ceased.
Bayan da Yesu da Bitrus suka shiga cikin kwale-kwalen, sai iska ta daina kadawa.
33 Those who were in the boat worshiped him, saying, "You are truly the Son of God."
Sai almajiran dake cikin kwale-kwalen su ka yi wa Yesu sujada suna cewa, “Hakika kai Dan Allah ne.”
34 When they had crossed over, they came to the land of Gennesaret.
Da suka haye, sun iso kasar Janisarata.
35 When the people of that place recognized him, they sent into all that surrounding region, and brought to him all who were sick,
Da mutanen wurin suka gane Yesu, sai suka aika da sako zuwa dukan yankin, kuma suka kawo masa dukan marasa lafiya.
36 and they begged him that they might just touch the fringe of his garment. And all who touched it were healed.
Suka roke shi don su taba gezar rigarsa, kuma dukan wadanda suka taba shi sun warke.