< Mark 4 >
1 And again he began to teach by the seaside. And a large crowd was gathered to him, so that he entered into a boat in the sea, and sat down. And the whole crowd was on the land by the sea.
Ya kuma fara koyarwa a bakin teku. Akwai babban taro kewaye da shi, sai ya shiga cikin jirgin ruwa a cikin tekun, ya kuwa zauna. Duk taron kuwa na kan tudu a bakin tekun.
2 And then he taught them many things in parables, and told them in his teaching,
Ya koya masu abubuwa da yawa da misalai, a cikin koyawarsa ya ce masu,
3 "Listen. Look, the sower who went out to sow.
“ku saurara! wani mai shuka ya tafi shuka.
4 And it happened, as he sowed, some seed fell by the road, and the birds came and devoured it.
Yana cikin yafa iri, sai wadansu iri suka fadi a kan hanya, tsuntsaye kuma suka zo suka tsince su.
5 And others fell on the rocky ground, where it had little soil, and immediately it sprang up, because it had no depth of soil.
Wadansu kuma suka fadi a kan dutse inda ba kasa dayawa. Nan da nan kuwa suka tsiro saboda rashin zurfin kasa.
6 And when the sun came up, it was scorched; and because it had no root, it withered away.
Da rana fa ta daga, sai suka yankwane da yake ba su da saiwa sosai, sai suka bushe.
7 And others fell among the thorns, and the thorns grew up, and choked it, and it yielded no fruit.
Wadansu kuma suka fadi cikin kayayuwa su ka yi girma sai kayayuwan suka shake su, ba su yi tsaba ba.
8 And others fell into the good ground, and yielded fruit, growing up and increasing; and brought forth thirty times, and sixty times, and one hundred times."
Wadansu kuma suka fadi a kasa mai kyau, suka yi yabanya, suka yi tsaba, suka yi girma, wadansu ribi talattin wadansu sittin, wadansu kuma dari”.
9 And he said, "Whoever has ears to hear, let him hear."
Sai ya ce, Duk mai kunnen ji, ya ji,”
10 And when he was alone, those who were around him with the twelve asked him about the parables.
Sa'adda Yesu yake shi kadai, wadanda suke kusa dashi tare da sha biyun suka tambaye shi ma'anar misalan.
11 And he said to them, "To you has been given the mystery of the Kingdom of God, but to those who are outside, all things are done in parables,
Sai ya ce masu, “ku an yardar maku, ku san asirin mulkin Allah, amma ga wadanda ba su cikinku, komai sai a cikin Misalai,
12 that 'seeing they may see, and not perceive; and hearing they may hear, and not understand; lest perhaps they should turn and be forgiven.'"
don gani da ido sun gani, amma ba su gane ba. ji kuma, sun ji, amma ba su fahimta ba, don kada su juyo a gafarta masu,”
13 And he said to them, "Do you not understand this parable? And how will you understand all of the parables?
Ya ce masu, “Ashe, ba ku fahimci wannan misalin ba? yaushe za ku fahimci sauran?
14 The farmer sows the word.
Mai shukan nan fa maganar Allah yake shukawa.
15 And these are the ones by the road where the word is sown; and when they have heard, immediately Satan comes, and takes away the word which has been sown in them.
Wadanda suka fadi a hanyar kuwa, su ne kwatancin wadanda. a aka shuka mganar a zuciyarsu, Da suka ji, nan da nan sai shaidan ya zo ya dauke Maganar da aka shuka a zuciyarsu.
16 And these in a similar way are those who are sown on the rocky places, who, when they have heard the word, immediately receive it with joy.
Haka kuma wadanda aka shuka a wuri mai duwatsu, sune wadanda da zarar sun ji Maganar sai su karba da farin ciki.
17 And they have no root in themselves, but are short-lived. Then, when oppression or persecution arises because of the word, immediately they stumble.
Su kuwa basu da tushe, ba su da karfi, idan kunci ko tsanani ya zo saboda kalmar, nan da nan sai su yi tuntube.
18 And others are those who are sown among the thorns; these are the ones who have heard the word,
Wadansu kuma su ne kwatacin wadanda suka fadi cikin kayayuwa, sune wadanda suka ji Maganar,
19 and the cares of the age, and the deceitfulness of riches, and the lusts of other things entering in choke the word, and it becomes unfruitful. (aiōn )
amma abubuwan duniya, da rudin dukiya da kuma kwadayin wadansu abubuwa, sukan shiga su shake Maganar, har ta zama marar amfani. (aiōn )
20 And those which were sown on the good ground are those who hear the word, and accept it, and bear fruit, some thirty times, some sixty times, and some one hundred times."
Wadanda aka shuka a kasa mai kyau kuwa, sune kwatancin wadanda suke jin Maganar, su karba, su kuma yin amfani da ita wadansu ribi talatin, wadansu sittin, wadansu dari.”
21 And he said to them, "Is the lamp brought to be put under a basket or under a bed? Is it not put on a stand?
ya ce masu, “Shin, ana kawo fitila a cikin gida don a rufe ta da kwando ko a ajiye ta a karkashin gado? ku kan kawo ta ne don ku dora ta a kan madorinta.
22 For there is nothing hidden, except that it should be made known; neither was anything made secret, but that it should come to light.
Ba abin da yake boye, da baza a sani ba ko kuma ba abinda ke asirce da bazaya bayyana a fili ba.
23 If anyone has ears to hear, let him hear."
Bari mai kunnen ji, ya ji!''
24 And he said to them, "Consider carefully what you hear. With whatever measure you measure, it will be measured to you, and more will be given to you.
Sai ya ce masu, ku mai da hankali a kan abin da kuka ji, Mudun da ka auna, da shi za a auna maka, har ma a kara maka.
25 For whoever has, more will be given, and he who does not have, even that which he has will be taken away from him."
Domin mai abu akan karawa, marar abu kuma za a karba daga wurinsa a kuma karawa mai shi.”
26 And he said, "The Kingdom of God is like someone who scatters seed on the earth,
Sai ya ce, “Mulkin Allah kamar mutum yake mai yafa iri a kasa.
27 and he sleeps and rises night and day, and the seed springs up and grows; he doesn't know how.
A kwana a tashi har irin ya tsiro, ya girma bai kuwa san ta yaya aka yi ba.
28 The earth bears fruit, first the blade, then the ear, then the full grain in the ear.
Kasa da kanta, takan ba da amfani, tsiro shine ne na farko,
29 But when the fruit is ripe, immediately he puts forth the sickle, because the harvest has come."
Sai kai, sa'anan sai kwaya mai kwari. Sa, adda amfani ya nuna, sai ya sa lauje ya yanke nan da nan, wato kaka ta yi kenan.”
30 And he said, "To what will we liken the Kingdom of God? Or with what parable will we use for it?
Ya kuma ce, “Da me za mu kwatanta Mulki Allah? ko kuwa da wane misali za mu misalta shi?
31 It's like a mustard seed, which, when it is sown upon the soil, though it is less than all the seeds that are upon the soil,
Kamar kwayar zarra yake wadda, in an shuka ta, ko da yake ita ce mafi kankanta cikin kwayoyi a duniya.
32 And when it is sown, grows up, and becomes greater than all the garden plants, and puts out large branches, so that the birds of the sky can lodge under its shadow."
Duk da haka in an shuka ta, sai ta yi girma fiye da duk sauran ita-tuwan da ke a jeji tayi manyan rassa, har tsuntsaye su iya yin sheka arassanta.”
33 And with many such parables he spoke the word to them, as they were able to hear it.
Da misalai da yawa, irin wadannan ya yi masu Magana, dadai gwargwadon ganewarsu,
34 And he did not speak to them without a parable; but privately to his own disciples he explained everything.
ba ya fada masu kome sai da misali, amma a kebe, yakan bayyana wa almajiransa dukan abu.
35 And on that day, when evening had come, he said to them, "Let us go over to the other side."
A ranan nan da yama ta yi yace masu “Mu haye wancan ketaren.”
36 And leaving the crowd, they took him with them, even as he was, in the boat. And other boats were with him.
Sai suka bar taron, suka tafi tare da shi acikin cikin jirgin. wadansu jirage kuma na tare da shi.
37 And a big wind storm arose, and the waves beat into the boat, so much that the boat was already filled.
Sai babban hadari da iska mai karfi ya taso, rakuman ruwa kuma na ta girgizawa cikin jirgin, har jirgin ya cika.
38 And he himself was in the stern, asleep on the cushion, and they woke him up, and told him, "Teacher, do you not care that we are dying?"
Yesu kuwa na daga karshen bayan jirgin a kan kujera, yana barci, sai suka tashe shi, suka ce masa “Malam za mu hallaka ba ka kula ba?”
39 And he awoke, and rebuked the wind, and said to the sea, "Peace. Be still." And the wind ceased, and there was a great calm.
Sai ya farka, ya tsawata wa Iskar. Ya kuma ce wa ruwan tekun, “Ka natsu! ka yi shiru!” Sai Iskar ta kwanta, wurin duk ya yi shiru.
40 And he said to them, "Why are you so afraid? Do you still have no faith?"
Ya ce masu, “Don me kuka firgita haka? Har yanzu baku da bangaskiya ne?”
41 And they were greatly afraid, and said to one another, "Who then is this, that even the wind and the sea obey him?"
Sai suka tsorata kwarai suka ce wa juna, “wanene wannan kuma, wanda har Iska da teku ma suke yi masa biyayya?”