< John 6 >

1 After these things, Jesus went away to the other side of the sea of Galilee, which is also called the Sea of Tiberias.
Ɗan lokaci bayan wannan, sai Yesu ya ƙetare zuwa gaɓar mai nesa na Tekun Galili (wato, Tekun Tibariya),
2 A large crowd followed him, because they saw the signs which he did on those who were sick.
sai taro mai yawa na mutane suka bi shi domin sun ga abubuwan banmamakin da ya yi ga marasa lafiya.
3 Jesus went up into the mountain, and he sat there with his disciples.
Sa’an nan Yesu ya hau gefen dutse ya zauna tare da almajiransa.
4 Now the Passover, the Jewish festival, was near.
Bikin Ƙetarewan Yahudawa ya yi kusa.
5 Jesus therefore lifting up his eyes, and seeing that a large crowd was coming to him, said to Philip, "Where are we to buy bread, that these may eat?"
Sa’ad da Yesu ya ɗaga kai ya ga taro mai yawa suna zuwa wajensa, sai ya ce wa Filibus, “Ina za mu sayi burodi saboda mutanen nan su ci?”
6 This he said to test him, for he himself knew what he would do.
Ya yi wannan tambayar don yă gwada shi ne kawai, gama ya riga ya san abin da zai yi.
7 Philip answered him, "Two hundred denarii worth of bread is not sufficient for them, that everyone of them may receive a little."
Sai Filibus ya amsa ya ce, “Kai, ko albashin wata takwas ba zai iya sayan isashen burodin da kowa zai ɗan samu kaɗan ba!”
8 One of his disciples, Andrew, Simon Peter's brother, said to him,
Sai wani daga cikin almajiransa Andarawus, ɗan’uwan Bitrus, ya yi magana,
9 "There is a boy here who has five barley loaves and two fish, but what are these among so many?"
“Ga wani yaro da ƙananan burodin sha’ir guda biyar da ƙananan kifi biyu, amma me wannan zai yi wa yawan mutanen nan.”
10 Jesus said, "Have the people sit down." Now there was much grass in that place. So the men sat down, in number about five thousand.
Yesu ya ce, “Ku sa mutanen su zauna.” Wurin kuwa akwai ciyawa da sosai, sai maza suka zazzauna, sun kai wajen dubu biyar.
11 Jesus took the loaves; and having given thanks, he distributed to the disciples, and the disciples to those who were sitting down; likewise also of the fish as much as they desired.
Sa’an nan Yesu ya ɗauki burodin, ya yi godiya, ya kuma rarraba wa waɗanda suke zaune gwargwadon abin da ya ishe su. Haka kuma ya yi da kifin.
12 When they were filled, he said to his disciples, "Gather up the broken pieces which are left over, that nothing be lost."
Sa’ad da duk suka ci suka ƙoshi, sai ya ce wa almajiransa, “Ku tattara gutsattsarin da suka rage. Kada kome yă lalace.”
13 So they gathered them up, and filled twelve baskets with broken pieces from the five barley loaves, which were left over by those who had eaten.
Saboda haka suka tattara su suka kuma cika kwanduna goma sha biyu na gutsattsarin burodin sha’ir biyar nan da suka ragu bayan kowa ya ci.
14 When therefore the people saw the sign which he did, they said, "This is truly the Prophet who comes into the world."
Bayan mutanen suka ga abin banmamakin da Yesu ya yi, sai suka fara cewa, “Lalle, wannan shi ne Annabin nan mai zuwa duniya.”
15 Jesus therefore, perceiving that they were about to come and take him by force, to make him king, withdrew again to the mountain by himself.
Da Yesu ya gane suna shirin su ɗauke shi ƙarfi da yaji su naɗa shi sarki, sai ya sāke komawa kan dutsen shi kaɗai.
16 When evening came, his disciples went down to the sea,
Da yamma ta yi, sai almajiransa suka gangara zuwa tafki,
17 and they entered into the boat, and were going over the sea to Capernaum. It was now dark, and Jesus had not yet come to them.
inda suka shiga jirgin ruwa suka tasar wa haye tafkin zuwa Kafarnahum. A lokacin kuwa duhu ya yi, Yesu kuma bai riga ya zo wurinsu ba tukuna.
18 The sea was tossed by a great wind blowing.
Iska mai ƙarfi kuwa tana bugowa, ruwaye kuma suka fara hauka.
19 When therefore they had rowed about three or four miles, they saw Jesus walking on the sea, and drawing near to the boat; and they were afraid.
Bayan sun yi tuƙi wajen mil uku ko uku da rabi, sai suka ga Yesu ya kusato jirgin ruwan, yana takawa a kan ruwan; sai suka tsorata.
20 But he said to them, "It is I. Do not be afraid."
Amma ya ce musu, “Ni ne; kada ku ji tsoro.”
21 They were willing therefore to receive him into the boat. Immediately the boat was at the land where they were going.
Sa’an nan suka yarda suka karɓe shi a cikin jirgin ruwan, nan da nan kuwa jirgin ya kai gaɓar da za su.
22 On the next day, the crowd that stood on the other side of the sea saw that there was no other boat there, except one, and that Jesus had not entered with his disciples into the boat, but his disciples had gone away alone.
Kashegari taron da suka tsaya a wancan ƙetaren tafkin suka lura cewa jirgin ruwa ɗaya ne yake a can dā ma, kuma sun lura cewa Yesu bai shiga ciki tare da almajiransa ba, gama sun tashi su kaɗai.
23 Other boats from Tiberias came near to the place where they ate the bread after the Lord had given thanks.
Sai ga waɗansu jiragen ruwa daga Tibariya suka iso kusa da wurin da mutanen suka ci burodi bayan Ubangiji ya yi godiya.
24 When the crowd therefore saw that Jesus was not there, nor his disciples, they themselves got into the boats, and came to Capernaum, seeking Jesus.
Da taron suka lura cewa Yesu da almajiransa ba sa can, sai suka shiga jiragen ruwa suka tafi Kafarnahum neman Yesu.
25 When they found him on the other side of the sea, they asked him, "Rabbi, when did you come here?"
Da suka same shi a wancan ƙetaren tafkin, sai suka tambaye shi suka ce, “Rabbi, yaushe ka kai nan?”
26 Jesus answered them, "Truly, truly, I tell you, you seek me, not because you saw signs, but because you ate of the loaves, and were filled.
Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, kuna nemana ne ba don kun ga abubuwan banmamaki ba, sai dai domin kun ci burodi kun ƙoshi.
27 Do not work for the food which perishes, but for the food which remains to everlasting life, which the Son of Man will give to you. For God the Father has sealed him." (aiōnios g166)
Kada ku yi aiki saboda abincin da yake lalacewa, sai dai saboda abinci mai dawwama har yă zuwa rai madawwami, wanda Ɗan Mutum zai ba ku. A kansa ne Allah Uba ya sa hatimin amincewarsa.” (aiōnios g166)
28 They said therefore to him, "What must we do, that we may work the works of God?"
Sai suka tambaye shi suka ce, “Me za mu yi don mu aikata ayyukan da Allah yake so?”
29 Jesus answered them, "This is the work of God, that you believe in him whom he has sent."
Yesu ya amsa, “Aikin Allah shi ne, a gaskata da wanda ya aiko.”
30 They said therefore to him, "What then do you do for a sign, that we may see, and believe you? What work do you do?
Sai suka tambaye shi, “Wace abin banmamaki ce za ka yi don mu gani mu kuwa gaskata ka? Me za ka yi?
31 Our fathers ate the manna in the wilderness. As it is written, 'He gave them bread out of heaven to eat.'"
Kakannin-kakanninmu sun ci Manna a hamada; kamar yadda yake a rubuce, ‘Ya ba su burodi daga sama su ci.’”
32 Jesus therefore said to them, "Truly, truly, I tell you, it was not Moses who gave you the bread out of heaven, but my Father gives you the true bread out of heaven.
Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, ba Musa ne ya ba ku burodi daga sama ba, sai dai Ubana ne yake ba ku burodi na gaskiya daga sama.
33 For the bread of God is that which comes down out of heaven, and gives life to the world."
Gama burodin Allah shi ne wanda yake saukowa daga sama, yana kuma ba wa duniya rai.”
34 They said therefore to him, "Lord, always give us this bread."
Sai suka ce, “Ranka yă daɗe, daga yanzu ka dinga ba mu wannan burodi.”
35 Jesus said to them, "I am the bread of life. He who comes to me will not be hungry, and he who believes in me will never be thirsty.
Sa’an nan Yesu ya furta cewa, “Ni ne burodin rai. Wanda ya zo wurina ba zai taɓa jin yunwa ba, wanda kuma ya gaskata da ni ba zai taɓa jin ƙishirwa ba.
36 But I told you that you have seen me, and yet you do not believe.
Amma kamar yadda na faɗa muku, kun gan ni duk da haka ba ku gaskata ba.
37 All those whom the Father gives me will come to me. Him who comes to me I will in no way throw out.
Duk waɗanda Uba ya ba ni za su zo wurina, kuma duk wanda ya zo wurina ba zan kore shi ba ko kaɗan.
38 For I have come down from heaven, not to do my own will, but the will of him who sent me.
Gama na sauko daga sama ba don in cika nufin kaina ba sai dai don in cika nufin shi wanda ya aiko ni.
39 This is the will of him who sent me, that of all he has given to me I should lose nothing, but should raise him up at the last day.
Nufin wanda ya aiko ni kuwa shi ne, kada in yar da ko ɗaya daga cikin duk waɗanda ya ba ni, sai dai in tashe su a rana ta ƙarshe.
40 This is the will of my Father, that everyone who sees the Son, and believes in him, should have everlasting life; and I will raise him up at the last day." (aiōnios g166)
Gama nufin Ubana shi ne, duk wanda yake duban Ɗan, ya kuma gaskata shi zai sami rai madawwami, ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe.” (aiōnios g166)
41 The Jewish people therefore murmured concerning him, because he said, "I am the bread which came down out of heaven."
Da jin haka, Yahudawa suka fara gunaguni a kansa, domin ya ce, “Ni ne burodin da ya sauka daga sama.”
42 They said, "Is not this Jesus, the son of Joseph, whose father and mother we know? How then does he say, 'I have come down out of heaven?'"
Suka ce, “Kai, wannan ba Yesu ba ne, ɗan Yusuf, wanda mahaifinsa da mahaifiyarsa duk mun san su? Yaya yanzu zai ce, ‘Na sauko daga sama?’”
43 Therefore Jesus answered them, "Do not murmur among yourselves.
Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ku daina gunaguni a junanku.
44 No one can come to me unless the Father who sent me draws him, and I will raise him up in the last day.
Ba mai iya zuwa wurina, sai dai in Uban da ya aiko ni ya jawo shi, ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe.
45 It is written in the Prophets, 'And they will all be taught by God.' Therefore everyone who hears and learns from the Father comes to me.
A rubuce yake a cikin Annabawa cewa, ‘Allah zai koyar da dukansu.’Duk wanda ya saurari Uba, ya kuma koyi daga wurinsa, zai zo wurina.
46 Not that anyone has seen the Father, except he who is from God. He has seen the Father.
Ba wanda ya taɓa ganin Uban, sai shi wanda ya zo daga Allah; shi ne kaɗai ya taɓa ganin Uban.
47 Truly, truly, I tell you, he who believes has everlasting life. (aiōnios g166)
Gaskiya nake gaya muku, wanda ya gaskata yana da rai madawwami. (aiōnios g166)
48 I am the bread of life.
Ni ne burodin rai.
49 Your fathers ate the manna in the wilderness, and they died.
Kakannin-kakanninku sun ci Manna a hamada, duk da haka suka mutu.
50 This is the bread which comes down out of heaven, that anyone may eat of it and not die.
Amma ga burodin da ya sauko daga sama, wanda mutum zai iya ci, ba zai kuma mutu ba.
51 I am the living bread which came down out of heaven. If anyone eats of this bread, he will live forever; and the bread which I will give for the life of the world is my flesh." (aiōn g165)
Ni ne burodin rai mai saukowa daga sama. Duk wanda ya ci wannan burodi, zai rayu har abada. Wannan burodin shi ne jikina, da zan bayar don duniya ta sami rai.” (aiōn g165)
52 The Jews therefore argued with one another, saying, "How can this one give us flesh to eat?"
Sai Yahudawa suka fara gardama mai tsanani a junansu suna cewa, “Yaya wannan mutum zai ba mu naman jikinsa mu ci?”
53 Jesus therefore said to them, "Truly I tell you, unless you eat the flesh of the Son of Man and drink his blood, you do not have life in yourselves.
Sai Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, sai kun ci naman jikin Ɗan Mutum kuka kuma sha jininsa, ba za ku kasance da rai a cikinku ba.
54 He who eats my flesh and drinks my blood has everlasting life, and I will raise him up at the last day. (aiōnios g166)
Duk wanda ya ci naman jikina ya kuma sha jinina, yana da rai madawwami. Ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe. (aiōnios g166)
55 For my flesh is food indeed, and my blood is drink indeed.
Gama naman jikina abinci ne na gaskiya jinina kuma abin sha ne na gaskiya.
56 He who eats my flesh and drinks my blood lives in me, and I in him.
Duk wanda ya ci naman jikina ya kuma sha jinina, yana cikina, ni kuma ina cikinsa.
57 As the living Father sent me, and I live because of the Father; so he who feeds on me, he will also live because of me.
Kamar dai yadda Uba mai rai ya aiko ni, ina kuma rayuwa ta saboda shi, haka ma wanda yake ni ne abincinsa zai rayu saboda ni.
58 This is the bread which came down out of heaven—not as the fathers ate, and died. He who eats this bread will live forever." (aiōn g165)
Wannan shi ne burodin da ya sauko daga sama. Kakannin-kakanninku sun ci Manna suka kuma mutu, amma duk wanda yake cin wannan burodi zai rayu har abada.” (aiōn g165)
59 He said these things in the synagogue, as he taught in Capernaum.
Ya faɗi wannan ne lokacin da yake koyarwa a cikin majami’a a Kafarnahum.
60 Therefore many of his disciples, when they heard this, said, "This is a hard saying. Who can listen to it?"
Da jin haka, da yawa daga cikin almajiransa suka ce, “Wannan koyarwa tana da wuya. Wa zai iya yarda da ita?”
61 But Jesus knowing in himself that his disciples murmured at this, said to them, "Does this cause you to stumble?
Da yake ya san almajiransa suna gunaguni game da wannan, sai Yesu ya ce musu, “Wannan ya ɓata muku rai ne?
62 Then what if you would see the Son of Man ascending to where he was before?
Me za ku ce ke nan, in kuka gan Ɗan Mutum yana hawa zuwa inda yake dā!
63 It is the Spirit who gives life. The flesh profits nothing. The words that I speak to you are spirit, and are life.
Ruhu ne yake ba da rai; jikin kam, ba ya amfana kome. Kalmomin da na faɗa muku, Ruhu ne, da kuma rai.
64 But there are some of you who do not believe." For Jesus knew from the beginning who they were who did not believe, and who it was who would betray him.
Duk da haka akwai waɗansunku da ba su gaskata ba.” Gama Yesu ya sani tun farko, waɗanda ba su gaskata ba, da kuma wanda zai bashe shi.
65 He said, "For this cause have I said to you that no one can come to me, unless it is given to him by the Father."
Ya ci gaba da cewa, “Shi ya sa na faɗa muku cewa ba mai iya zuwa wurina, sai dai Uba ya yardar masa.”
66 At this, many of his disciples went back, and walked no more with him.
Daga wannan lokaci da yawa daga cikin almajiransa suka ja da baya, suka daina bin sa.
67 Jesus said therefore to the twelve, "You do not also want to go away, do you?"
Sai Yesu ya tambayi Sha Biyun, “Ku ma za ku tafi ne?”
68 Simon Peter answered him, "Lord, to whom would we go? You have the words of everlasting life. (aiōnios g166)
Sai Siman Bitrus ya amsa ya ce, “Ubangiji wajen wa za mu tafi? Kai ne da kalmomin rai madawwami. (aiōnios g166)
69 We have come to believe and know that you are the Holy One of God."
Mun gaskata mun kuma san cewa kai ne Mai Tsarkin nan na Allah.”
70 Jesus answered them, "Did I not choose you, the twelve, and one of you is a devil?"
Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ba ni na zaɓe ku Sha Biyu ba? Amma ɗayanku Iblis ne!”
71 Now he spoke of Judas, the son of Simon Iscariot, for it was he who would betray him, being one of the twelve.
(Yana nufin Yahuda, ɗan Siman Iskariyot, wanda, ko da yake ɗaya ne cikin Sha Biyun, zai bashe shi daga baya.)

< John 6 >