< Psalms 34 >

1 [By David; when he pretended to be insane before Abimelech, who drove him away, and he departed.] I will bless the LORD at all times. His praise will always be in my mouth.
Ta Dawuda. Sa’ad da ya yi kamar ya haukace a gaban Abimelek, Wanda ya kore shi, ya kuwa tafi. Zan gode wa Ubangiji kullayaumi; yabonsa kullum za su kasance a leɓunana.
2 My soul shall boast in the LORD. The humble shall hear of it, and be glad.
Raina zai yi fariya a cikin Ubangiji; bari waɗanda suke wahala su ji su kuma yi farin ciki.
3 Oh magnify the LORD with me. Let us exalt his name together.
Ku ɗaukaka Ubangiji tare da ni; bari mu ɗaukaka sunansa tare.
4 I sought the LORD, and he answered me, and delivered me from all my fears.
Na nemi Ubangiji, ya kuwa amsa mini; ya cece ni daga dukan tsoro.
5 They looked to him and were radiant, and their faces are not ashamed.
Waɗanda suke dubansa sukan haskaka; fuskokinsu ba sa rufuwa da kunya.
6 This poor man cried, and the LORD heard him, and saved him out of all his troubles.
Wannan matalauci ya yi kira, Ubangiji kuwa ya ji shi; ya cece shi daga dukan wahalarsa.
7 The angel of the LORD encamps around those who fear him, and delivers them.
Mala’ikan Ubangiji ya kafa sansani kewaye da waɗanda suke tsoronsa, ya kuwa cece su.
8 Oh taste and see that the LORD is good. Blessed is the man who takes refuge in him.
Ku gwada ku gani cewa Ubangiji yana da kyau; mai albarka ne mutumin da yake neman mafaka a gare shi.
9 Oh fear the LORD, you his holy ones, for there is no lack with those who fear him.
Ku ji tsoron Ubangiji, ku tsarkakansa, gama masu tsoronsa ba sa rasa kome.
10 The young lions do lack, and suffer hunger, but those who seek the LORD shall not lack any good thing.
Zakoki za su iya rasa ƙarfi su kuma ji yunwa, amma waɗanda suke neman Ubangiji ba sa rasa abu mai kyau.
11 Come, you children, listen to me. I will teach you the fear of the LORD.
Ku zo,’ya’yana, ku saurare ni; zan koya muku tsoron Ubangiji.
12 Who is someone who desires life, and loves many days, that he may see good?
Duk waninku da yake ƙaunar rayuwa yana kuma so yă ga kwanaki masu kyau,
13 Keep your tongue from evil, and your lips from speaking lies.
ka kiyaye harshenka daga mugunta da kuma leɓunanku daga faɗar ƙarairayi.
14 Turn away from evil, and do good. Seek peace, and pursue it.
Juyo daga mugunta ku yi alheri; nemi salama ku kuma yi ƙoƙarin samunta.
15 The eyes of the LORD are toward the righteous. His ears listen to their cry.
Idanun Ubangiji suna a kan masu adalci kuma kunnuwansa suna sauraran kukansu;
16 The LORD's face is against those who do evil, to cut off the memory of them from the earth.
fuskar Ubangiji yana gāba da waɗanda suke aikata mugunta, don yă sa a manta da su a duniya.
17 The righteous cry out, and the LORD hears, and delivers them out of all their troubles.
Adalai kan yi kuka, Ubangiji kuwa yakan ji su; yakan cece su daga dukan wahalarsu.
18 The LORD is near to those who have a broken heart, and saves those who have a crushed spirit.
Ubangiji yana kusa da waɗanda suka karai ya kuma cece waɗanda aka ragargaza a ruhu.
19 Many are the afflictions of the righteous, but the LORD delivers him out of them all.
Adali zai iya kasance da wahala da yawa, amma Ubangiji yakan cece shi daga dukansu;
20 He protects all of his bones. Not one of them is broken.
yakan tsare dukan ƙasusuwansa, ba ko ɗayansu da zai karye.
21 Evil shall kill the wicked. Those who hate the righteous shall be condemned.
Mugunta zai kashe mugu; za a hukunta abokan gāban adalai.
22 The LORD redeems the soul of his servants. None of those who take refuge in him shall be condemned.
Ubangiji yakan cece bayinsa; ba wanda yake neman mafaka a wurinsa da za a hukunta.

< Psalms 34 >