< Mark 8 >
1 In those days, when there was a large crowd, and they had nothing to eat, he called the talmidim to himself, and said to them,
A kwanakin nan, akwai wani gagaruman taron mutane, kuma basu da abincin ci. Yesu ya kirawo almajiransa yace masu,
2 "I have compassion on the crowd, because they have stayed with me now three days, and have nothing to eat.
“Ina tausayin taron mutanen nan domin kwana uku kenan suna nan tare da ni babu abinci.
3 If I send them away fasting to their home, they will faint on the way, and some of them have come a long way."
Idan na salame su su koma gidajensu ba tare da sun ci abinci ba, za su galabaita a hanya domin gidajensu na da nisa.”
4 His talmidim answered him, "From where could one satisfy these people with bread here in a deserted place?"
Almajiransa suka amsa masa cewa, “A ina za mu iya samu gurasa a wannan jeji da zai ishi wadannan mutane haka?”
5 He asked them, "How many loaves do you have?" They said, "Seven."
Ya tambaye su, “gurasa nawa kuke da su?” Sai suka ce, “Bakwai.”
6 He commanded the crowd to sit down on the ground, and he took the seven loaves. Having given thanks, he broke them, and gave them to his talmidim to serve, and they served the crowd.
Ya umarci mutanen da su zauna. Ya dauki gurasar bakwai, bayan da ya yi godiya, ya kakarya gurasar, sa'annan ya umarci almajiransa da su raba wa mutanen. Su kuwa suka raba masu.
7 They had a few small fish. Having blessed them, he said to serve these also.
Suna kuma da kananan kifaye kadan. Bayan da ya yi godiya akan su, ya umurci almajiran su rabawa mutanen.
8 They ate, and were filled. They took up seven baskets of broken pieces that were left over.
Sun ci sun koshi. Suka tattara ragowar, har sun cika kwanduna bakwai.
9 Now they were about four thousand. Then he sent them away.
Akwai maza kimanin dubu hudu a wurin. Yesu ya sallame su.
10 Immediately he entered into the boat with his talmidim, and came into the region of Dalmanutha.
Nan take, ya shiga jirgin ruwa da almajiransa zuwa shiyyar Dalmanuta.
11 The Pharisees came out and began to question him, seeking from him a sign from heaven, and testing him.
Sai Farisawa suka zo suka fara gardama da shi. Suna nema ya nuna masu alama daga sama, domin su gwada shi.
12 He sighed deeply in his spirit, and said, "Why does this generation seek a sign? Truly I tell you, no sign will be given to this generation."
Ya ja numfashi a ruhunsa yana cewa, “Don me wannan tsarar tana neman alama. Hakika ina gaya maku, babu wata alama da za a ba wannan tsarar.”
13 And he left them, and got into the boat again, and went to the other side.
Sai ya bar su ya sake shiga jirgin zuwa hayin tafkin.
14 Now they forgot to take bread; and they did not have more than one loaf in the boat with them.
A lokacin nan, almajiransa sun manta su dauki gurasa. Domin gurasa daya ce tak a garesu cikin jirgin ruwan.
15 He warned them, saying, "Watch out; guard yourselves against the hametz of the Pharisees and the hametz of Herod."
Ya gargade su, “ku yi hattara da yisti na Farisawa da Yisti na Hirudus.”
16 And they began discussing among themselves that they had no bread.
Almajiran suka fara tattaunawa a tsakaninsu, “Saboda ba mu da gurasa ne.”
17 He, perceiving it, said to them, "Why do you reason that it's because you have no bread? Do you not perceive yet, neither understand? Are your hearts hardened?
Yesu yana sane da wannan, sa'annan ya ce masu, “Don me kuke tattaunawa akan rashin gurasa? Har yanzu baku gane ba? Har yanzu ba ku da sane? Ko zuciyar ku ta duhunta ne?”
18 Having eyes, do you not see? Having ears, do you not hear? Do you not remember?
Kuna da idanu, ba ku gani? Kuna da kunnuwa, ba ku ji? Ba ku tuna ba?
19 When I broke the five loaves among the five thousand, how many baskets full of broken pieces did you take up?" They told him, "Twelve."
Da na kakkarya gurasar a cikin mutane dubu biyar, kwanduna nawa kuka samu ragowa? Suka ce masa, “Goma sha biyu.”
20 "When the seven loaves fed the four thousand, how many baskets full of broken pieces did you take up?" And they said, "Seven."
Kuma da na kakarya gurasa bakwai a cikin mutane dubu hudu, kwanduna nawa kuka dauka cike da ragowar? Suka ce masa, “bakwai.”
21 He asked them, "Do you not yet understand?"
Ya ce masu, “har yanzu baku gane ba?”
22 He came to Beit Tzaidah. They brought a blind man to him, and begged Yeshua to touch him.
Sun zo Baitsaida. Mutanen wurin suka kawo masa wani makaho, sai suka roke shi ya taba shi.
23 He took hold of the blind man by the hand, and brought him out of the village. When he had spit on his eyes, and laid his hands on him, he asked him if he saw anything.
Yesu ya rike hanun makahon, ya jagorance shi zuwa bayan kauyen. Da ya tofa yawunsa a idon mutumin, kuma ya dora hanunsa akan mutumin, sai ya tambaye shi “kana ganin wani abu kuwa?”
24 He looked up, and said, "I see people; they look like trees walking."
Ya daga ido sai ya ce, “ina ganin mutane na tafiya kamar itatuwa.”
25 Then again he laid his hands on his eyes. He made him look up, and was restored, and saw everything clearly.
Ya sake dora masa hannu a idanuwansa, mutumin ya bude idanuwansa, sai ya fara ganin gari da kyau.
26 He sent him away to his house, saying, "Do not enter into the village."
Yesu ya sallame shi zuwa gidansa nan take, ya ce masa, “kada ka shiga cikin garin”
27 Yeshua went out, with his talmidim, into the villages of Caesarea Philippi. On the way he asked his talmidim, "Who do people say that I am?"
Yesu da almajiransa sun shiga kauyukan kaisariya ta Filibi. Da suke kan hanya, sai ya tambaye su, “Shin wanene mutane ke ce da ni?”
28 And they said to him, saying, "John the Immerser, and others say Elijah, but others: one of the prophets."
Suka amsa masa suka ce, Yahaya mai Baftisma. Wasu suka ce, “Iliya”. wadansu kuma, 'Daya daga cikin anabawa”.
29 He said to them, "But who do you say that I am?" Peter answered and said to him, "You are the Messiah."
Ya tambaye su, “Amma me ku ke ce da ni?” Bitrus ya ce, “Kai ne Almasihu.”
30 He commanded them that they should tell no one about him.
Yesu ya umarce su kada su gaya wa kowa game da shi.
31 He began to teach them that the Son of Man must suffer many things, and be rejected by the elders, the chief cohanim, and the scribes, and be killed, and after three days rise again.
Sai ya fara koya masu cewa, dole ne Dan Mutum ya sha wahala, dattawa da marubuta da manyan Firistoci zasu ki shi, a kuma kashe shi. Bayan kwana uku, zai tashi daga matattu.
32 He spoke to them openly. Peter took him, and began to rebuke him.
Ya fadi wannan afili. Sai Birus ya ja shi gefe ya fara tsauta masa.
33 But he, turning around, and seeing his talmidim, rebuked Peter, and said, "Get behind me, Satan. For you have in mind not the things of God, but the things of humans."
Amma Yesu ya juya ya dubi almajiransa sa'annan ya tsautawa Bitrus yana cewa, “Ka koma bayana Shaidan, domin kana kula da abubuwan mutane ne kawai, ba na Allah ba.”
34 He called the crowd to himself with his talmidim, and said to them, "If anyone wants to come after me, let him deny himself, and take up his cross, and follow me.
Sai ya kira taron jama'ar da almajiransa a wuri daya, ya ce masu, “Duk wanda yake so ya bini, dole ne ya musunci kansa, ya dauki giciyensa ya biyo ni.
35 For whoever wants to save his life will lose it; and whoever will lose his life for my sake and the sake of the Good News will save it.
Domin duk wanda yake so ya ceci ransa zai rasa shi, amma duk wadda ya rasa ransa domina da kuma bishara zai cece shi.
36 For what does it profit a person to gain the whole world, and forfeit his soul?
Me zai amfani mutum idan ya sami dukan duniya sannan ya rasa ransa.
37 Or what will a person give in exchange for his soul?
Me mutum zai bayar amaimakon ransa?
38 For whoever will be ashamed of me and of my words in this adulterous and sinful generation, the Son of Man also will be ashamed of him, when he comes in the glory of his Father with the holy angels."
Duk wanda ke jin kunyata ko maganata a wannan mazinaciyar tsara mai zunubi, Dan Mutum ma zai ji kunyarsa a lokacin da ya dawo cikin daukakar Ubansa da Malaiku masu tsarki.”