< Mark 16 >

1 When the Sabbath was past, Miriam from Magdala, and Miriam the mother of Jacob, and Salome, bought spices, that they might come and anoint him.
Da Asabbaci ya wuce, sai Maryamu Magdalin, Maryamu mahaifiyar Yaƙub, da kuma Salome suka sayi kayan ƙanshi domin su je su shafa wa jikin Yesu.
2 Very early on the first day of the week, they came to the tomb when the sun had risen.
A ranar farko ta mako, da sassafe, bayan fitowar rana, suna kan hanyarsu zuwa kabarin ke nan,
3 They were saying among themselves, "Who will roll away the stone from the door of the tomb for us?"
sai suka tambaye juna suka ce, “Wane ne zai gungura mana dutsen daga bakin kabarin?”
4 for it was very big. Looking up, they saw that the stone was rolled back.
Amma da suka ɗaga kai, sai suka ga cewa, an riga an gungura dutsen. Dutsen kuwa babba ne.
5 Entering into the tomb, they saw a young man sitting on the right side, dressed in a white robe, and they were amazed.
Da suna shiga cikin kabarin, sai suka ga wani saurayi sanye da farar riga, yana zaune a hannun dama, sai suka firgita.
6 He said to them, "Do not be amazed. You seek Yeshua of Natzeret, who has been crucified. He has risen. He is not here. Look, the place where they put him.
Ya ce, “Kada ku firgita. Kuna neman Yesu Banazare wanda aka gicciye ne. Ya tashi! Ba ya nan. Ku dubi inda aka kwantar da shi.
7 But go, tell his talmidim and Peter, 'He goes before you into Galil. There you will see him, as he said to you.'"
Amma ku tafi ku gaya wa almajiransa da kuma Bitrus cewa, ‘Ya sha gabanku zuwa Galili. Can za ku gan shi, kamar yadda ya faɗa muku.’”
8 They went out, and fled from the tomb, for trembling and astonishment had come on them. They said nothing to anyone; for they were afraid.
Da rawan jiki da kuma ruɗewa, matan suka fita a guje daga kabarin. Ba su kuwa gaya wa kowa ba, don suna tsoro.
9 (note: The most reliable and earliest manuscripts do not include Mark 16:9-20.) Now when he had risen early on the first day of the week, he appeared first to Miriam from Magdala, from whom he had cast out seven demons.
(note: The most reliable and earliest manuscripts do not include Mark 16:9-20.) Da Yesu ya tashi daga matattu da safe, a ranar farko ta mako, ya fara bayyana ga Maryamu Magdalin, wadda ya fitar da aljanu bakwai daga cikinta.
10 She went and told those who had been with him, as they mourned and wept.
Ta je ta gaya wa waɗanda dā suke tare da shi, waɗanda kuma suke makoki da kuka.
11 When they heard that he was alive, and had been seen by her, they disbelieved.
Da suka ji cewa Yesu yana da rai, har ma ta gan shi, ba su gaskata ba.
12 And after these things he appeared in another form to two of them, as they walked on their way into the country.
Daga baya Yesu ya bayyana a wani kamanni dabam ga biyunsu, yayinda suke tafiya ƙauye.
13 And they went away and told it to the rest. They did not believe them, either.
Waɗannan kuwa suka koma suka shaida wa sauran, amma su ma ba su gaskata ba.
14 Afterward he was revealed to the eleven themselves as they were reclining, and he rebuked them for their unbelief and hardness of heart, because they did not believe those who had seen him after he had risen.
Bayan haka, Yesu ya bayyana ga Sha Ɗayan, yayinda suke cin abinci. Ya tsawata musu a kan rashin bangaskiyarsu, da yadda suka ƙi gaskata waɗanda suka gan shi bayan ya tashi.
15 And he said to them, "Go into all the world, and proclaim the Good News to the whole creation.
Ya ce, musu, “Ku tafi cikin dukan duniya, ku yi wa’azin bishara ga dukan halitta.
16 He who believes and is immersed will be saved; but he who disbelieves will be condemned.
Duk wanda ya gaskata, aka kuma yi masa baftisma, zai sami ceto. Amma duk wanda bai gaskata ba kuwa, zai hallaka.
17 And these signs will accompany those who believe: in my name they will cast out demons; they will speak with new tongues;
Waɗannan alamu za su kasance tare da waɗanda suka gaskata. A cikin sunana za su fitar da aljanu, za su yi magana da sababbin harsuna.
18 they will pick up serpents; and if they drink any deadly thing, it will not harm them; they will place their hands on the sick, and they will be made well."
Za su ɗauki macizai da hannuwansu. In kuwa suka sha mugun dafi, ba zai cuce su ba ko kaɗan. Za su ɗibiya hannuwansu a kan marasa lafiya, su kuwa warke.”
19 So then the Lord Yeshua, after he had spoken to them, was taken up into heaven, and sat down at the right hand of God.
Bayan Ubangiji Yesu ya yi musu magana, sai aka ɗauke shi zuwa sama, ya kuma zauna a hannun dama na Allah.
20 And they went out and preached everywhere, the Lord working with them and confirming the message by the signs that followed.
Sai almajiran suka fita, suka yi wa’azi ko’ina. Ubangiji kuwa ya yi aiki tare da su, ya tabbatar da maganarsa ta wurin alamu da suke biye da maganar.

< Mark 16 >