< Luke 20 >
1 It happened on one of those days, as he was teaching the people in the temple and proclaiming the Good News, that the chief cohanim and scribes came to him with the elders.
Wata rana da Yesu yana koyar da mutane, yana musu wa’azin bishara a filin haikalin, sai manyan firistoci da malaman dokoki, tare da dattawan suka zo wurinsa.
2 They asked him, "Tell us: by what authority do you do these things? Or who is giving you this authority?"
Suka ce masa, “Gaya mana, da wane iko kake yin waɗannan abubuwa. Wa ya ba ka wannan ikon?”
3 He answered them, "I also will ask you one question. Tell me:
Ya amsa ya ce, “Ni ma zan yi muku wata tambaya. Ku faɗa mini,
4 the immersion of John, was it from heaven, or from man?"
baftismar Yohanna, daga sama ne ta fito, ko kuwa daga wurin mutane ne?”
5 They reasoned with themselves, saying, "If we say, 'From heaven,' he will say, 'Why did you not believe him?'
Sai suka yi shawara da junansu, suka ce, “In muka ce, ‘Daga sama ne,’ zai tambaya, ‘To, don me ba ku gaskata shi ba?’
6 But if we say, 'From man,' all the people will stone us, for they are persuaded that John was a prophet."
Amma in kuma muka ce, ‘Daga mutane ne,’ dukan mutanen za su jajjefe mu da duwatsu, domin sun tabbata cewa, Yohanna annabi ne.”
7 They answered that they did not know where it was from.
Don haka, sai suka amsa cewa, “Ba mu san inda ta fito ba.”
8 Yeshua said to them, "Neither will I tell you by what authority I do these things."
Yesu ya ce, “To, ni ma ba zan gaya muku, ko da wane iko ne, nake yin waɗannan abubuwa ba.”
9 He began to tell the people this parable. "A man planted a vineyard, and rented it out to some farmers, and went on a journey for a long time.
Sai ya ci gaba da gaya wa mutanen wannan misali ya ce, “Wani mutum ya yi gonar inabi, sai ya ba da hayarta ga waɗansu manoma, sa’an nan ya yi wata doguwar tafiya.
10 At the proper season, he sent a servant to the farmers to collect his share of the fruit of the vineyard. But the farmers beat him, and sent him away empty.
A lokacin girbi, sai ya aiki bawa zuwa wurin masu hayan, don su ba shi daga cikin’ya’yan inabin. Amma’yan hayan suka yi wa bawan nan dūka, suka kore shi hannu wofi.
11 He sent yet another servant, and they also beat him, and treated him shamefully, and sent him away empty.
Ya sāke aikan wani bawa, shi ma suka yi masa dūka, suka kunyata shi, suka kuma kore shi hannu wofi.
12 He sent yet a third, and they also wounded him, and threw him out.
Har yanzu, ya sāke aikan na uku, amma suka ji masa rauni, suka jefar da shi waje.
13 The lord of the vineyard said, 'What am I to do? I will send my beloved son. It may be that they will respect him.'
“Sai mai gonar inabin ya ce, ‘Me zan yi? Zan aiki ɗana da nake ƙauna, wataƙila za su girmama shi.’
14 "But when the farmers saw him, they reasoned among themselves, saying, 'This is the heir. Let us kill him, that the inheritance may be ours.'
“Amma da’yan hayan suka gan shi, sai suka tattauna zancen, suka ce, ‘Wannan shi ne magājin, mu kashe shi sa’an nan gādon zai zama namu!’
15 They threw him out of the vineyard, and killed him. What therefore will the lord of the vineyard do to them?
Sai suka fitar da shi waje, suka kashe shi. “To, me mai gonar inabin zai yi da su?
16 He will come and destroy these farmers, and will give the vineyard to others." When they heard it, they said, "May it never be."
Zai zo ya karkashe masu hayan nan, ya ba wa waɗansu gonar inabin.” Da mutanen suka ji wannan, sai suka ce, “Allah ya sawwaƙa!”
17 But he looked at them, and said, "Then what is this that is written, 'The stone which the builders rejected, the same was made the chief cornerstone?'
Yesu ya zura musu ido ya ce, “To, mene ne ma’anar abin da aka rubuta cewa, “‘Dutsen da magina suka ƙi, shi ne kuwa ya zama dutsen kan ginin’
18 Everyone who falls on that stone will be broken to pieces; but on whomever it falls, it will crush him."
Duk wanda ya fāɗi a kan dutsen nan, zai kakkarye. Kuma in dutsen nan ya fāɗi a kan wani, zai murƙushe shi.”
19 The chief cohanim and the scribes sought to lay hands on him that very hour, but they feared the people—for they knew he had spoken this parable against them.
Malaman dokoki da manyan firistoci, suka nemi hanyar kama shi nan da nan, domin sun san cewa, ya yi wannan misali a kansu ne, amma suna jin tsoron mutane.
20 They watched him, and sent out spies, who pretended to be righteous, that they might trap him in something he said, so as to deliver him up to the power and authority of the governor.
Sai suka sa masa ido, suka aiki’yan leƙen asiri, waɗanda suka nuna kamar su masu gaskiya ne, suna nufin su kama shi game da abin da zai faɗa, domin su ba da shi ga gwamna mai mulki, da mai iko.
21 They asked him, "Teacher, we know that you say and teach what is right, and are not partial to anyone, but truly teach the way of God.
Sai’yan leƙen asirin suka tambaye shi, suka ce, “Malam, mun sani kana faɗin, kuma kana koyar da abin da yake daidai, ba ka kuma nuna bambanci, amma kana koyar da hanyar Allah bisa ga gaskiya.
22 Is it lawful for us to pay taxes to Caesar, or not?"
Daidai ne mu biya haraji ga Kaisar, ko babu?”
23 But he perceived their craftiness, and said to them,
Ya gane makircinsu, sai ya ce musu,
24 "Show me a denarius. Whose image and inscription are on it?" They answered, "Caesar's."
“Nuna mini dinari. Hoton wane ne, kuma rubutun wane ne a kai?” Suka amsa, “Na Kaisar.”
25 He said to them, "Then give to Caesar the things that are Caesar's, and to God the things that are God's."
Sai ya ce musu, “Ku ba wa Kaisar abin da yake na Kaisar, ku kuma ba wa Allah abin da yake na Allah.”
26 They weren't able to trap him in his words before the people. And amazed at his answer, they fell silent.
Ba su iya kama shi a kan abin da ya faɗa a fili ba. Amsarsa ya ba su mamaki, shi ya sa suka yi shiru.
27 Some of the Sadducees came to him, those who deny that there is a resurrection.
Waɗansu Sadukiyawa da suke cewa, ba tashin matattu, suka zo wurin Yesu da tambaya cewa,
28 They asked him, "Teacher, Moses wrote to us that if a man's brother dies having a wife, and he is childless, his brother should take the wife, and raise up children for his brother.
“Malam, Musa ya rubuta mana cewa, ‘In ɗan’uwan wani mutum ya mutu, ya bar mata amma ba’ya’ya, dole mutumin ya aure gwauruwar, ya samo wa ɗan’uwansa’ya’ya.’
29 There were therefore seven brothers. The first took a wife, and died childless.
To, an yi waɗansu’yan’uwa bakwai. Na fari ya auri wata mace, ya mutu ba’ya’ya.
31 the third took her, and likewise the seven all left no children, and died.
da na ukun suka aure ta. Haka nan dukansu bakwai suka mutu babu’ya’ya.
32 Afterward the woman also died.
A ƙarshe, ita macen ma ta mutu.
33 Therefore in the resurrection whose wife of them will she be? For the seven had her as a wife."
Shin, a tashin matattu, matar wa za tă zama? Tun da su bakwan nan, sun aure ta.”
34 Yeshua said to them, "The people of this age marry and are given to someone to marry. (aiōn )
Yesu ya amsa ya ce, “Mutanen zamanin nan suna aure, suna kuma ba da aure, (aiōn )
35 But those who are regarded as worthy of a place in that age and the resurrection from the dead neither marry nor are given to someone to marry. (aiōn )
amma su waɗanda aka ga sun cancantar kasancewa a zamanin can, da kuma na tashin matattu, ba za su yi aure, ko su ba da aure ba. (aiōn )
36 For they cannot die any more, for they are like the angels, and are children of God, being children of the resurrection.
Kuma ba za su sāke mutuwa ba, gama su kamar mala’iku ne. Su’ya’yan Allah ne, tun da su’ya’yan tashin matattu ne.
37 But that the dead are raised, even Moses showed at the bush, when he called the Lord 'The God of Abraham, and the God of Isaac, and the God of Jacob.'
Amma bisa ga labari na bishiya nan, mai cin wuta da Musa ya gani a jeji, ko Musa ma, ya nuna cewa, matattu suna tashi. Gama ya kira Ubangiji, ‘Allah na Ibrahim, da Allah na Ishaku, da kuma Allah na Yaƙub.’
38 Now he is not the God of the dead, but of the living, for all are alive to him."
Shi ba Allah na matattu ba ne, amma na masu rai ne, gama a gare shi, duka na da rai.”
39 Some of the scribes answered, "Teacher, you speak well."
Sai waɗansu malaman dokoki suka amsa suka ce, “Ka faɗi daidai, malam!”
40 They did not dare to ask him any more questions.
Kuma ba wanda ya sami ƙarfin halin yin masa waɗansu tambayoyi.
41 He said to them, "Why do they say that the Messiah is David's son?
Sai Yesu ya ce musu, “Yaya suke cewa, ‘Kiristi ɗan Dawuda ne?’
42 David himself says in the scroll of Psalms, 'The Lord said to my Lord, "Sit at my right hand,
Dawuda da kansa ya faɗa a cikin Zabura, “‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana,
43 until I make your enemies the footstool of your feet."'
sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”’
44 "David therefore calls him Lord, so how is he his son?"
Dawuda ya kira shi ‘Ubangiji.’ Ta, yaya zai zama ɗansa?”
45 In the hearing of all the people, he said to his talmidim,
Yayinda dukan mutane suna cikin sauraronsa, sai Yesu ya ce wa almajiransa,
46 "Beware of the scribes, who like to walk in long robes, and love greetings in the marketplaces, the best seats in the synagogues, and the best places at feasts;
“Ku yi hankali da malaman dokoki. Sukan so sa manyan riguna suna zaga, suna sha’awan karɓan gaisuwa a wuraren kasuwanci, da kuma wuraren zama mafi daraja a majami’u, da wuraren bangirma a bukukkuwa.
47 who devour widows' houses, and for a pretense make long prayers: these will receive greater condemnation."
Suna mamaye gidajen gwauraye, kuma don burga, suna dogayen addu’o’i. Ga irin waɗannan mutane, za a yi musu hukunci mai tsanani sosai.”