< 2 Samuel 4 >

1 Now when Ishbaal, Saul's son, heard that Abner was dead in Hebron, he lost courage, and all Israel was troubled.
Sa’ad da Ish-Boshet ya ji labari cewa Abner ya mutu a Hebron, sai ya karaya, sai dukan hankalin Isra’ila ya tashi.
2 And Ishbaal, Saul's son, had two men who were captains of bands; the name of the one was Baanah, and the name of the other Rechab, the sons of Rimmon the Beerothite, of the people of Benjamin (for Beeroth was regarded as belonging to the people of Benjamin;
To, ɗan Shawulu yana da’ya’ya maza biyu da suke shugabannin’yan hari. Ana kiran ɗaya Ba’ana, ɗayan kuma Rekab. Su’ya’yan Rimmon mutumin Benyamin ne daga Beyerot, an lissafta Beyerot a ɓangaren Benyamin,
3 and the Beerothites fled to Gittaim, and have lived as foreigners there until this day).
domin mutanen Beyerot sun gudu zuwa Gittayim inda suke zaman baƙunci har wa yau.
4 Now Jonathan, Saul's son, had a son whose feet were crippled. He was five years old when the news came of Saul and Jonathan from Jezreel, and his nurse took him up and fled. And it happened as she was hurrying to get away that he fell and was injured. And his name was Mippibaal.
(Yonatan ɗan Shawulu yana da ɗa mai suna Mefiboshet wanda yake gurgu a duka ƙafafu. Yana da shekara biyar ne sa’ad da labarin mutuwar Shawulu da Yonatan ya zo daga Yezireyel. Sai mai renonsa ta ɗauke shi ta gudu, amma yayinda take hanzari tă gudu, sai ya fāɗo, ya gurgunce.)
5 The sons of Rimmon the Beerothite, Rechab and Baanah, went, and came about the heat of the day to the house of Ishbaal, as he took his rest at noon.
To, Rekab da Ba’ana,’ya’yan Rimmon mutumin Beyerot, suka tafi gidan Ish-Boshet, suka isa can da tsakar rana yayinda yake hutun tsakar rana.
6 And look, the doorkeeper of the house had been sifting wheat, and she became drowsy and fell asleep. And Rechab and his brother Baanah slipped by.
Suka shiga sashe na cikin gida sai ka ce suna so su ɗibo alkama ne, suka soke shi a ciki. Sa’an nan Rekab da Ba’ana ɗan’uwansa suka zame suka ɓace.
7 And they went into the house where he was lying on his bed in his bedchamber. And they struck him and killed him, and beheaded him. And they took his head and went by the way of the Arabah all night.
Sun shiga gidan yayinda yake kwance a gado a ɗakin barcinsa. Bayan sun soke shi sai suka kashe shi, suka kuma datse kansa. Suka ɗauke shi, suka yi tafiya dukan dare suka bi ta Araba.
8 They brought the head of Ishbaal to David at Hebron, and said to the king, "Look, the head of Ishbaal, the son of Saul, your enemy, who sought your life. The LORD has avenged my lord the king this day of Saul and his descendants."
Suka kawo kan Ish-Boshet wa Dawuda a Hebron, suka ce wa sarki, “Ga kan Ish-Boshet ɗan Shawulu, maƙiyinka, wanda ya nemi yă kashe ka. A yau Ubangiji ya rama wa ranka yă daɗe sarki, a kan Shawulu da zuriyarsa.”
9 David answered Rechab and Baanah his brother, the sons of Rimmon the Beerothite, and said to them, "As the LORD lives, who has redeemed my soul out of all adversity,
Dawuda ya ce wa Rekab da ɗan’uwansa Ba’ana,’ya’yan Rimmon mutumin Beyerot, “Muddin Ubangiji yana a raye, wanda ya kuɓutar da ni daga wahala,
10 when someone told me, 'Look, Saul is dead,' thinking to have brought good news, I took hold of him, and killed him in Ziklag, which was the reward I gave him for his news.
sa’ad da wani mutum ya ce mini, ‘Shawulu ya mutu,’ yana tsammani ya kawo labari mai daɗi ne, na kama shi na kashe a Ziklag. Ladar da na ba shi ke nan saboda labarinsa!
11 How much more, when wicked men have slain a righteous person in his own house on his bed, shall I not now require his blood of your hand, and take you away from the earth?"
Balle fa, sa’ad da mugayen mutane suka kashe marar laifi a gidansa, a bisa gadonsa, ashe, ba zan nemi jininsa daga hannunku in kawar da ku a duniya ba!”
12 David commanded his young men, and they killed them, and cut off their hands and their feet, and hanged them up beside the pool in Hebron. But they took the head of Ishbaal, and buried it in the grave of Abner son of Ner.
Saboda haka Dawuda ya umarci mutanensa, suka kuwa kashe su. Suka yayyanka hannuwansu da ƙafafunsu, suka kuma rataye jikunansu kusa da tafki a Hebron. Amma suka ɗauki kan Ish-Boshet suka binne a kabarin Abner a Hebron.

< 2 Samuel 4 >