< 1 Kings 4 >

1 King Solomon was king over all Israel.
Sai Sarki Solomon ya yi mulki a bisa dukan Isra’ila.
2 These were the officials whom he had: Azariah the son of Zadok, the cohen;
Waɗannan su ne manyan shugabanninsa. Azariya ɗan Zadok shi ne firist;
3 Elihoreph and Ahijah, the sons of Shisha, scribes; Jehoshaphat the son of Ahilud, the recorder;
Elihoref da Ahiya,’ya’yan Shisha maza, su ne marubuta. Yehoshafat ɗan Ahilud, shi ne mai lura da takardu.
4 and Benaiah the son of Jehoiada was over the army; and Zadok and Abiathar were cohanim;
Benahiya ɗan Yehohiyada, shi ne shugaban mayaƙa. Zadok da Abiyatar, su ne firistoci.
5 and Azariah the son of Nathan was over the officers; and Zabud the son of Nathan was chief minister, the king's friend;
Azariya ɗan Natan, shi ne mai lura da shugabannin yanki. Zabud ɗan Natan, shi ne firist da kuma mai wa sarki shawara.
6 and Ahishar was over the palace; and Eliab son of Joab was over the army; and Adoniram the son of Abda was over the men subject to forced labor.
Ahishar, shi ne sarkin fada. Adoniram ɗan Abda, shi ne mai lura da aikin gandu.
7 Solomon had twelve officers over all Israel, who provided food for the king and his household: each man had to make provision for a month in the year.
Solomon yana da gwamnoni yankuna goma sha biyu a bisa dukan Isra’ila, waɗanda suke tanaji abinci domin sarki da kuma gidan sarauta. Kowanne yakan tanada abinci na wata ɗaya a shekara.
8 These are their names: Ben Hur, in the hill country of Ephraim;
Ga sunayensu, Ben-Hur, shi ne a ƙasar tudun Efraim;
9 Ben Deker, in Makaz, and in Shaalbim, and Beth Shemesh, and Elon Beth Hanan;
Ben-Deker, shi ne a Makaz, Sha’albim, Bet-Shemesh da Elon Bet-Hanan;
10 Ben Hesed, in Arubboth (to him belonged Socoh, and all the land of Hepher);
Ben-Hesed, shi ne a Arubbot (Soko da dukan ƙasar Hefer);
11 Ben Abinadab, in all the height of Dor (he had Taphath the daughter of Solomon as wife);
Ben-Abinadab, shi ne a Nafot Dor (ya auri Tafat’yar Solomon);
12 Baana the son of Ahilud, in Taanach and Megiddo, and all Beth Shean which is beside Zarethan, beneath Jezreel, from Beth Shean to Abel Meholah, as far as beyond Jokmeam;
Ba’ana ɗan Ahilud, shi ne a Ta’anak da Megiddo, da kuma dukan Bet-Sheyan biye da Zaretan ƙasa da Yezireyel, daga Bet-Sheyan zuwa Abel-Mehola a ƙetaren Yokmeyam;
13 Ben Geber, in Ramoth Gilead (to him belonged the towns of Jair the son of Manasseh, which are in Gilead; to him belonged the region of Argob, which is in Bashan, sixty great cities with walls and bronze bars);
Ben-Geber, shi ne a Ramot Gileyad (Mazaunan Yayir ɗan Manasse a Gileyad suna a ƙarƙashinsa, haka ma yankin Argob a Bashan tare da manyan biranen sittin masu katanga da suke da ƙyamare na tagulla);
14 Ahinadab the son of Iddo, in Mahanaim;
Ahinadab ɗan Iddo, shi ne a Mahanayim;
15 Ahimaaz, in Naphtali (he also took Basemath the daughter of Solomon as wife);
Ahimawaz, shi ne a Naftali (ya auri Basemat’yar Solomon);
16 Baana the son of Hushai, in Asher and in Aloth;
Ba’ana ɗan Hushai, shi ne a Asher da Bayelot;
17 Jehoshaphat the son of Paruah, in Issachar;
Yehoshafat ɗan Faruwa, shi ne a Issakar;
18 Shimei the son of Ela, in Benjamin;
Shimeyi ɗan Ela, shi ne a Benyamin;
19 Geber the son of Uri, in the land of Gilead, the country of Sihon king of the Amorites and of Og king of Bashan; and he was the only prefect in the land of Judah.
Geber ɗan Uri, shi ne a Gileyad (ƙasar Sihon sarkin Amoriyawa da kuma Og sarkin Bashan). Shi ne kaɗai gwamna a bisa yankin.
20 Judah and Israel were many as the sand which is by the sea in multitude, eating and drinking and making merry.
Mutanen Yahuda da na Isra’ila sun yi yawa sai ka ce yashi a bakin teku. Suka ci, suka sha, suka kuma yi farin ciki.
21 And Solomon ruled over all the kingdoms, from the River, and to the land of the Philistines, and to the border of Egypt. They brought tribute and served Solomon all the days of his life.
Solomon kuwa ya yi mulki a bisa dukan masarautai daga Kogi zuwa ƙasar Filistiyawa, har zuwa iyakar Masar. Waɗannan ƙasashe sun yi ta kawo haraji, suka kuma zama bayin Solomon dukan kwanakin ransa.
22 Solomon's provision for one day was thirty measures of fine flour, and sixty measures of meal,
Tanajin Solomon na kowace rana su ne, garwa talatin na garin abinci,
23 ten head of fat cattle, and twenty head of cattle out of the pastures, and one hundred sheep, besides deer, and gazelles, and roebucks, and fattened fowl.
shanun da aka yi kiwo a gida guda goma, shanu ashirin da suka ƙoshi daga kiwo, tumaki da awaki ɗari; ban da ƙishimai, bareyi, batsiyoyi, da kaji masu ƙiba.
24 For he had dominion over all on this side the River, from Tiphsah even to Gaza, over all the kings on this side the River: and he had peace on all sides around him.
Gama ya yi mulki a bisa dukan masarautai yamma da Kogi, daga Tifsa zuwa Gaza, aka kuwa sami zaman lafiya a kowane gefe.
25 Judah and Israel lived safely, every man under his vine and under his fig tree, from Dan even to Beersheba, all the days of Solomon.
A kwanakin da Solomon yake raye, Yahuda da Isra’ila, daga Dan zuwa Beyersheba, sun zauna lafiya, kowane mutum ya zauna a ƙarƙashin itacen inabi da na ɓaurensa.
26 And Solomon had four thousand stalls of horses for his chariots, and twelve thousand horsemen.
Solomon yana da rumfunan dawakai masu jan kekunan yaƙi, dubu huɗu, da kuma dawakai dubu goma sha biyu
27 Those officers provided food for king Solomon, and for all who came to king Solomon's table, every man in his month; they let nothing be lacking.
Shugabannin yankuna, kowanne a watansa yakan yi tanajin abinci domin Sarki Solomon da kuma duk wanda ya zo teburin sarki. Sun tabbatar ba a rasa kome ba.
28 And they also brought barley and straw for the horses and the steeds to the place where the officers were, every man according to his duty.
Kowa a cikinsu, bisa ga lokacin da aka ba shi, yakan kai hatsin sha’ir da ciyawa domin dawakan-kekunan yaƙi, da sauran dawakai a inda aka ajiye su.
29 God gave Solomon wisdom and exceptional insight, and very great understanding, even as the sand that is on the seashore.
Allah ya ba Solomon hikima da hangen nesa mai girma, da kuma fāɗin fahimta marar iyaka, kamar yashi a bakin teku.
30 Solomon's wisdom excelled the wisdom of all the people of the east, and all the wisdom of Egypt.
Hikimar Solomon ta fi hikimar mutanen Gabas, ta kuma fi dukan hikimar Masar girma.
31 For he was wiser than all men; than Ethan the Ezrahite, and Heman, and Calcol, and Darda, the sons of Mahol: and his fame was in all the nations all around.
Ya fi kowane mutum hikima, har da Etan dangin Ezra ma. Yana da hikima fiye da Heman, Kalkol da Darda,’ya’yan Mahol maza. Sunansa ya bazu ko’ina a ƙasashen da suke kewaye.
32 He spoke three thousand proverbs; and his songs were one thousand five.
Ya yi karin magana dubu uku. Waƙoƙinsa kuwa sun kai dubu ɗaya da biyar.
33 He spoke of trees, from the cedar that is in Lebanon even to the hyssop that springs out of the wall; he spoke also of animals, and of birds, and of crawling creatures, and of fish.
Ya yi magana a kan rayuwar itatuwa, daga al’ul na Lebanon zuwa hizzob da yake girma a bangaye. Ya kuma yi koyarwa game da dabbobi, da tsuntsaye, da abubuwa masu rarrafe, da kuma kifi.
34 There came of all peoples to hear the wisdom of Solomon, from all kings of the earth, who had heard of his wisdom.
Mutane suka yi ta zuwa daga ƙasashe dabam-dabam don su ji hikimar Solomon. Sarakuna daga ko’ina a duniya, sun ji labarin hikimarsa, suka kuma aika da mutane don su ji shi.

< 1 Kings 4 >