< Psalms 92 >

1 [A Psalm. A song for the Sabbath day.] It is a good thing to give thanks to the LORD, to sing praises to your name, Most High;
Zabura ce. Waƙa ce. Domin ranar Asabbaci. Yana da kyau a yabi Ubangiji a kuma yi kiɗi ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka,
2 to proclaim your loving kindness in the morning, and your faithfulness every night,
don a yi shelar ƙaunarka da safe amincinka kuma da dare,
3 with the ten-stringed lute, with the harp, and with the melody of the lyre.
da kiɗin molo mai tsirkiya goma da kuma ƙarar garaya.
4 For you, LORD, have made me glad through your work. I will triumph in the works of your hands.
Gama ka sa na yi murna ta wurin ayyukanka, ya Ubangiji; na rera don farin ciki saboda ayyukan hannuwanka.
5 How great are your works, LORD. Your thoughts are very deep.
Ina misalin ayyukanka, ya Ubangiji, tunaninka da zurfi suke ƙwarai!
6 A senseless man doesn't know, neither does a fool understand this:
Mutum marar azanci ba zai sani ba, wawa ba zai gane ba,
7 though the wicked spring up as the grass, and all the evildoers flourish, they will be destroyed forever.
cewa ko da yake mugaye suna girma kamar ciyawa kuma dukan masu aikata mugunta suna haɓaka, za a hallaka su har abada.
8 But you, LORD, are on high forevermore.
Amma kai, ya Ubangiji, za a ɗaukaka har abada.
9 For, look, your enemies, LORD, for, look, your enemies shall perish. All the evildoers will be scattered.
Gama tabbatacce abokan gābanka, ya Ubangiji, tabbatacce abokan gābanka za su hallaka; za a watsar da dukan masu aikata mugunta.
10 But you have exalted my horn like that of the wild ox. I am anointed with fresh oil.
Ka ɗaukaka ƙahona kamar na ɓauna; an zubo mai masu kyau a kaina.
11 My eye has also seen my enemies. My ears have heard of the wicked enemies who rise up against me.
Idanuna sun ga fāɗuwar maƙiyana; kunnuwana sun ji kukan mugayen maƙiyana.
12 The righteous shall flourish like the palm tree. He will grow like a cedar in Lebanon.
Adalai za su haɓaka kamar itacen dabino, za su yi girma kama al’ul na Lebanon;
13 They are planted in the LORD's house. They will flourish in our God's courts.
da aka daddasa a gidan Ubangiji, za su haɓaka a filayen gidan Allahnmu.
14 They will still bring forth fruit in old age. They will be full of sap and green,
Za su ci gaba da ba da’ya’ya a tsufansu, za su kasance ɗanye kuma kore shar,
15 to show that the LORD is upright. He is my Rock, and there is no unrighteousness in him.
suna shela cewa, “Ubangiji adali ne; shi ne Dutsena, kuma babu mugunta a cikinsa.”

< Psalms 92 >