< Yochanan 9 >

1 And as he passed by, he saw a man blind from birth.
Da Yesu yana tafiya, sai ya ga wani mutum wanda aka haifa makaho.
2 And his disciples asked him, "Rabbi, who sinned, this man or his parents, that he was born blind?"
Sai almajiransa suka tambaye shi suka ce, “Rabbi, wane ne ya yi zunubi, mutumin ne, ko iyayensa, da ya sa aka haife shi makaho?”
3 Jesus answered, "Neither did this man sin, nor his parents; but, that the works of God might be revealed in him.
Sai Yesu ya ce, “Ba don mutumin ko iyayensa sun yi zunubi ne ba, sai dai don a bayyana aikin Allah ne a rayuwarsa.
4 We must work the works of him who sent me, while it is day. The night is coming, when no one can work.
Muddin da sauran rana, dole mu yi aikin wanda ya aiko ni. Dare yana zuwa, sa’ad da ba wanda zai iya yin aiki.
5 While I am in the world, I am the light of the world."
Yayinda ina a cikin duniya, ni ne hasken duniya.”
6 When he had said this, he spat on the ground, made mud with the saliva, anointed the blind man's eyes with the mud,
Bayan ya faɗi haka, sai ya tofa miyau a ƙasa, ya kwaɓa laka da miyau ɗin, ya kuma shafa a idanun mutumin.
7 and said to him, "Go, wash in the pool of Siloam" (which means "Sent"). So he went away, washed, and came back seeing.
Ya ce masa, “Je ka, ka wanke a Tafkin Silowam” (kalman nan tana nufin “Aikakke”). Saboda haka mutumin ya tafi ya wanke, ya kuma dawo gida yana gani.
8 The neighbors therefore, and those who saw that he was a beggar before, said, "Is this not the one who used to sit and beg?"
Maƙwabta da waɗanda suka saba ganinsa dā yana bara, suka ce, “Kai, ba wannan mutum ne ya saba zama yana bara ba?”
9 Some said, "It is he." Others said, "He looks like him." He said, "I am he."
Waɗansu suka ce shi mana. Waɗansu kuwa suka ce, “A’a, ya dai yi kama da shi.” Amma shi ɗin ya ce, “Ƙwarai kuwa ni ne.”
10 They therefore were asking him, "How were your eyes opened?"
Sai suka ce, “To, yaya aka yi idanunka suka buɗe?”
11 He answered, "A man called Jesus made mud, anointed my eyes, and said to me, 'Go to Siloam, and wash.' So I went away and washed, and I received sight."
Ya amsa ya ce, “Mutumin da ake kira Yesu ne ya kwaɓa laka ya shafa mini a idanu. Ya ce mini in je Silowam in wanke. Na kuwa tafi, na wanke, sai na sami ganin gari.”
12 Then they asked him, "Where is he?" He said, "I do not know."
Suka tambaye shi suka ce, “Ina mutumin yake?” Ya ce, “Ban sani ba.”
13 They brought him who had been blind to the Pharisees.
Sai suka kawo mutumin da dā yake makaho wurin Farisiyawa.
14 Now it was a Sabbath on the day when Jesus made the mud and opened his eyes.
To, a ranar da Yesu ya kwaɓa laka ya buɗe idanun mutumin ranar Asabbaci ce.
15 Again therefore the Pharisees also asked him how he received his sight. He said to them, "He put mud on my eyes, I washed, and I see."
Saboda haka Farisiyawa suka tambaye shi yadda ya sami ganin gari. Mutumin ya amsa, “Ya shafa laka a idanuna, sai na wanke, ina kuwa gani.”
16 Some therefore of the Pharisees said, "This man is not from God, because he does not keep the Sabbath." Others said, "How can a man who is a sinner do such signs?" There was division among them.
Sai waɗansu daga cikin Farisiyawa suka ce, “Mutumin nan ba daga Allah yake ba, don ba ya kiyaye ranar Asabbaci.” Amma waɗansu suka yi tambaya suka ce, “Yaya mutum mai zunubi zai yi irin abubuwan banmamaki haka?” Sai ra’ayinsu ya sha bamban.
17 Therefore they asked the blind man again, "What do you say about him, because he opened your eyes?" He said, "He is a prophet."
A ƙarshe suka sāke koma ga makahon suka ce, “Kai fa, me ka gani game da shi? Idanunka ne fa ya buɗe.” Sai mutumin ya ce, “Tab, ai, shi annabi ne.”
18 The Jewish leaders therefore did not believe concerning him, that he had been blind, and had received his sight, until they called the parents of him who had received his sight,
Yahudawa dai ba su yarda cewa dā shi makaho ne ya kuma sami ganin gari ba, sai da suka kira iyayen mutumin.
19 and asked them, "Is this your son, who you say was born blind? How then does he now see?"
Suka tambaye su, “Wannan ɗanku ne? Shi ne wanda kuka ce an haife shi makaho? To, ta yaya yake gani yanzu?”
20 His parents answered them, "We know that this is our son, and that he was born blind;
Iyayen suka amsa suka ce, “Mun dai san shi ɗanmu ne, mun kuma san cewa an haife shi makaho.
21 but how he now sees, we do not know; or who opened his eyes, we do not know. He is of age. Ask him. He will speak for himself."
Sai dai yadda yake gani yanzu, ko kuma wa ya buɗe idanunsa, ba mu sani ba. Ku tambaye shi. Ai, shi ba yaro ba ne, zai faɗa da bakinsa.”
22 His parents said these things because they feared the Jewish leaders; for the Jewish leaders had already agreed that if anyone would confess him as the Messiah, he would be put out of the synagogue.
Iyayensa sun faɗa haka ne saboda suna tsoron Yahudawa, gama Yahudawa sun riga sun yanke shawara cewa duk wanda ya yarda cewa Yesu shi ne Kiristi, za a kore shi daga majami’a.
23 Therefore his parents said, "He is of age. Ask him."
Shi ya sa iyayensa suka ce, “Ai, shi ba yaro ba ne, ku tambaye shi.”
24 So they called the man who was blind a second time, and said to him, "Give glory to God. We know that this man is a sinner."
Sai suka sāke kiran mutumin nan da yake makaho a dā, suka ce masa, “Ka ɗaukaka Allah, mu kam, mun san mutumin nan mai zunubi ne.”
25 He therefore answered, "I do not know if he is a sinner. One thing I do know: that though I was blind, now I see."
Sai ya amsa ya ce, “Ko shi mai zunubi ne ko babu, ni dai ban sani ba. Abu ɗaya fa na sani, dā ni makaho ne, amma yanzu ina gani!”
26 They said to him, "What did he do to you? How did he open your eyes?"
Sai suka tambaye suka ce, “Shin, me ya yi maka? Ta yaya ya buɗe idanunka?”
27 He answered them, "I told you already, and you did not listen. Why do you want to hear it again? You do not also want to become his disciples, do you?"
Ya amsa ya ce, “Na riga na gaya muku ba ku kuwa saurara ba. Don me kuke so ku sāke ji? Ko ku ma kuna so ku zama almajiransa ne?”
28 They insulted him and said, "You are his disciple, but we are disciples of Moses.
Sai suka hau shi da zagi suna cewa, “Kai ne dai almajirin mutumin! Mu almajiran Musa ne!
29 We know that God has spoken to Moses. But as for this man, we do not know where he comes from."
Mun dai san cewa Allah ya yi magana da Musa, amma wannan mutum ba mu san inda ya fito ba.”
30 The man answered them, "How amazing. You do not know where he comes from, yet he opened my eyes.
Sai mutumin ya ce, “Cabɗi, yau ga abin mamaki! Ba ku san inda ya fito ba, ga shi kuwa ya buɗe idanuna.
31 We know that God does not listen to sinners, but if anyone is a worshipper of God, and does his will, he listens to him.
Mun san cewa Allah ba ya sauraron masu zunubi. Yakan saurari mai tsoronsa mai aikata nufinsa.
32 Since the world began it has never been heard of that anyone opened the eyes of someone born blind. (aiōn g165)
Ba wanda ya taɓa ji cewa an buɗe idanun wanda aka haifa makaho. (aiōn g165)
33 If this man were not from God, he could do nothing."
Da mutumin nan ba daga Allah ba ne, da ba abin da zai iya yi.”
34 They answered him, "You were altogether born in sins, and do you teach us?" They threw him out.
Sai suka amsa suka ce, “Kai da aka haifa cike da zunubi; za ka yi karambanin koyarwar da mu!” Sai suka kore shi.
35 Jesus heard that they had thrown him out, and finding him, he said, "Do you believe in the Son of Man?"
Yesu ya ji labari cewa sun kore shi, da ya same shi kuwa, sai ya ce, “Ka gaskata da Ɗan Mutum?”
36 He answered, "Who is he, Lord, that I may believe in him?"
Sai mutumin ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, wane ne shi? Gaya mini, don in gaskata da shi.”
37 Jesus said to him, "You have both seen him, and it is he who speaks with you."
Yesu ya ce, “Yanzu ka gan shi; tabbatacce ma, shi ne yake magana da kai.”
38 He said, "Lord, I believe." and he worshiped him.
Sai mutumin ya ce, “Ubangiji, na gaskata,” ya kuma yi masa sujada.
39 Jesus said, "I came into this world for judgment, that those who do not see may see; and that those who see may become blind."
Yesu ya ce, “Saboda shari’a ce na zo duniya nan, saboda makafi su sami ganin gari, waɗanda suke gani kuma su makance.”
40 Those of the Pharisees who were with him heard these things, and said to him, "Are we also blind?"
Da Farisiyawan da suke tare da shi suka ji ya faɗi haka sai suka yi tambaya suka ce, “Mene? Mu ma makafi ne?”
41 Jesus said to them, "If you were blind, you would have no sin; but since you say, 'We see,' your sin remains.
Yesu ya ce, “Ai, da ku makafi ne ma, da ba ku da zunubi, amma da yake kun ce, kuna gani, zunubanku suna nan daram.

< Yochanan 9 >