< Hosea 13 >

1 When Ephraim spoke, there was trembling. He exalted himself in Israel, but when he became guilty in Baal, he died.
Sa’ad da Efraim ya yi magana, mutane sun yi rawan jiki; an girmama shi a cikin Isra’ila. Amma sai ya zama mai laifi na yin wa Ba’al sujada, ya kuwa mutu.
2 Now they sin more and more, and have made themselves molten images of their silver, even idols according to their own understanding, all of them the work of the craftsmen. They say of them, 'They offer human sacrifice and kiss the calves.'
Yanzu sai yin zunubi a kai a kai suke; suna yin gumaka wa kansu daga azurfansu, da wayo suna sarrafa siffofi, dukansu aikin masu aikin hannu ne. Ana magana waɗannan mutane cewa, “Suna miƙa hadayar mutum su kuma sumbaci gumakan maruƙa.”
3 Therefore they will be like the morning mist, and like the dew that passes away early, like the chaff that is driven with the whirlwind out of the threshing floor, and like the smoke out of the chimney.
Saboda haka za su zama kamar hazon safiya, kamar raɓar safen da yakan kakkaɓe, kamar ƙaiƙayin da ake tankaɗe daga masussuka, kamar hayaƙin da yake fita daga taga.
4 "Yet I am the LORD your God from the land of Egypt; and you shall acknowledge no god but me, and besides me there is no savior.
“Amma ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar. Ba za ku yarda da wani Allah ba sai ni, ba wani Mai Ceto in ban da ni.
5 I fed you in the wilderness, in the land of great drought.
Na lura da ku a hamada, cikin ƙasar mai ƙunar zafi.
6 According to their pasture, so were they filled; they were filled, and their heart was exalted. Therefore they have forgotten me.
Sa’ad da na ciyar da su sun ƙoshi; sa’ad da suka ƙoshi, sai suka fara taƙama; sai suka manta da ni.
7 Therefore I am like a lion to them. Like a leopard, I will lurk by the path.
Saboda haka zan hau kansu kamar zaki, zan ɓuya a bakin hanya kamar damisa.
8 I will meet them like a bear that is bereaved of her cubs, and will tear the covering of their heart. There I will devour them like a lioness. The wild animal will tear them.
Kamar beyar da aka ƙwace mata’ya’yanta, zan fāɗa musu in ɓarke su. Kamar zaki zan cinye su; kamar naman jeji zan yayyage su.
9 You are destroyed, Israel, because you are against me, against your help.
“An hallaka ku, ya Isra’ila, domin kun tayar mini, kun tayar wa mai taimakonku.
10 Where is your king now, that he may save you in all your cities? And your judges, of whom you said, 'Give me a king and princes?'
Ina sarkinku, da zai cece ku? Ina masu mulkinku cikin dukan garuruwanku, waɗanda kuka ce, ‘Ba mu sarki da shugabanni’?
11 I have given you a king in my anger, and have taken him away in my wrath.
Saboda haka cikin fushina na ba ku sarki, kuma cikin hasalata na ɗauke shi.
12 The guilt of Ephraim is stored up. His sin is stored up.
An yi ajiyar laifin Efraim, aka lissafta zunubansa.
13 The sorrows of a travailing woman will come on him. He is an unwise son; for when it is time, he doesn't come to the opening of the womb.
Naƙuda ta zo masa kamar a mace mai haihuwa, amma shi yaro ne marar hikima; sa’ad da lokaci ya kai, ba ya zuwa inda mahaifa ta buɗe.
14 I will ransom them from the power of Sheol. I will redeem them from death. Death, where is your victory? Sheol, where is your sting? "Compassion will be hidden from my eyes. (Sheol h7585)
“Zan fanshe su daga ikon kabari; zan cece su daga mutuwa. Ina annobanki, ya mutuwa? Ina hallakarka, ya kabari? “Ba zan ji tausayi ba, (Sheol h7585)
15 Though he is fruitful among his brothers, an east wind will come, the breath of the LORD coming up from the wilderness; and his spring will become dry, and his fountain will be dried up. He will plunder the storehouse of treasure.
ko da ma ya ci gaba cikin’yan’uwansa. Iskar gabas daga Ubangiji za tă zo, tana hurawa daga hamada; maɓulɓularsa za tă kafe rijiyarsa kuma ta bushe. Za a kwashi kaya masu daraja na ɗakin ajiyarsa ganima.
16 Samaria will bear her guilt; for she has rebelled against her God. They will fall by the sword. Their infants will be dashed in pieces, and their pregnant women will be ripped open."
Dole mutanen Samariya su ɗauki laifinsu, domin sun tayar wa Allahnsu. Za a kashe su da takobi; za a fyaɗa ƙananansu da ƙasa, za a ɓarke matansu masu ciki.”

< Hosea 13 >