< Genesis 24 >

1 Now Abraham was old, well advanced in days, and the LORD had blessed Abraham in all things.
Yanzu fa Ibrahim ya tsufa, yana da shekaru masu yawa, Ubangiji kuma ya albarkace shi a kowace hanya.
2 And Abraham said to his servant, the elder of his household, who was in charge over all that he had, "Please put your hand under my thigh,
Sai Ibrahim ya ce wa babban bawan gidansa, wanda yake lura da duk abin da yake da shi, “Sa hannunka a ƙarƙashin cinyata.
3 and I will make you swear by the God of heaven and earth, that you must not take a wife for my son from the daughters of the Canaanites, among whom I am living,
Ina so ka rantse da sunan Ubangiji Allah na sama da ƙasa, cewa ba za ka samo wa ɗana mata daga’yan matan Kan’aniyawa, waɗanda nake zama cikinsu ba.
4 but you must go to my country and to my relatives, and get a wife for my son Isaac."
Amma za ka tafi ƙasata da kuma cikin’yan’uwana, ka samo mata saboda ɗana Ishaku.”
5 And the servant asked him, "What if the woman isn't willing to follow me to this land? Must I then bring your son back to the land from which you came?"
Bawan ya ce masa, “Me zai faru in matar ba tă yarda tă zo tare da ni zuwa wannan ƙasa ba? In komar da ɗanka a ƙasar da ka fito ne ke nan?”
6 Then Abraham told him, "Be careful that you do not take my son back there.
Ibrahim ya ce, “Ka tabbata ba ka komar da ɗana can ba.”
7 Now the God of heaven, who took me from my father's household and from the land of my birth, who spoke to me and promised me on oath, saying, 'I will give this land to your offspring' -- he will send his angel before you, and you will get a wife for my son from there.
Ubangiji Allah na sama, wanda ya fitar da ni daga gidan mahaifina, da kuma ƙasar asalina wanda kuma ya yi magana da ni, ya yi mini alkawari da rantsuwa cewa, “Ga zuriyarka zan ba da wannan ƙasa, zai aika mala’ikansa yă sha gabanka domin ka samo wa ɗana mata daga can.
8 But if the woman isn't willing to follow you, then you will be free from this oath to me. Only you must not bring my son back there."
In matar ba tă yarda tă zo tare da kai ba, za a kuɓutar da kai daga wannan rantsuwa. Sai dai kada ka kai ɗana a can.”
9 So the servant put his hand under the thigh of his master Abraham and gave his oath to him concerning this matter.
Saboda haka bawan ya sa hannunsa a ƙarƙashin cinyar maigidansa Ibrahim, ya kuma rantse masa game da wannan al’amari.
10 Then the servant took ten camels from his master's camels and departed, having a variety of good things from his master at his disposal, and he set out and went to Aram Naharaim, to the city of Nahor.
Sai bawan ya ɗibi raƙuma goma na maigidansa ya tafi, ɗauke da kowane irin abubuwa masu kyau daga wurin maigidansa. Ya fita don yă tafi Aram-Naharayim, ya kama hanyarsa zuwa garin Nahor.
11 And he made the camels kneel down outside the city by the well of water at the time of evening, the time when women go out to draw water.
Ya sa raƙuman suka durƙusa kusa da rijiya a bayan gari; wajen yamma ne, lokacin da mata sukan fita ɗiban ruwa.
12 Then he said, "God of my master Abraham, please grant me success today and show kindness to my master Abraham.
Sai ya yi addu’a ya ce, “Ya Ubangiji Allah na maigidana Ibrahim, ka ba ni nasara yau, ka kuma nuna alheri ga maigidana Ibrahim.
13 Look, I am standing by the spring of water, and the daughters of the men of the city are coming out to draw water.
Duba, ina tsaye a bakin rijiyar ruwa,’ya’ya matan mutanen gari kuma suna fitowa domin ɗiban ruwa.
14 Now may it happen that the young woman to whom I will say, 'Please lower your jug that I may drink,' and she answers, 'Drink, and I will also give your camels a drink,'—her you have chosen for your servant Isaac. By this I will know that you have shown kindness to my master."
Bari yă zama sa’ad da na ce wa wata yarinya, ‘Ina roƙonki ki saukar da tulunki domin in sha,’ in ta ce, ‘Ka sha, zan kuma ba wa raƙumanka ma’; bari tă zama ita ce ka zaɓa wa bawanka Ishaku. Ta haka zan san cewa ka nuna wa maigidana alheri.”
15 And it happened, before he had finished speaking, that look, Rebekah was coming out with her jug on her shoulder—who was born to Bethuel the son of Milcah, the wife of Nahor, Abraham's brother.
Kafin ya gama addu’a, sai Rebeka ta fito da tulu a kafaɗarta. Ita’yar Betuwel ɗan Milka, matar Nahor, ɗan’uwan Ibrahim.
16 Now the young woman was very beautiful in appearance, a virgin; no man had ever slept with her. And she went down to the spring and filled her jug and came up.
Yarinyar kuwa kyakkyawa ce, budurwa, ba namijin da ya taɓa kwana da ita. Ta gangara zuwa rijiyar, ta cika tulunta ta kuma hauro.
17 Then the servant ran to meet her, and said, "Please give me a little water to drink from your jug."
Bawan ya yi sauri ya same ta ya ce, “Ina roƙonki ki ba ni ɗan ruwa daga tulunki.”
18 So she said, "Drink, my lord." And she hurried and let down her jug to her hands, and gave him a drink.
Ta ce, “Ka sha, ranka yă daɗe,” ta yi sauri ta saukar da tulun a hannuwanta, ta kuma ba shi, ya sha.
19 Now when she had finished giving him a drink, she said, "I will also draw for your camels, until they have finished drinking."
Bayan ta ba shi ya sha, sai ta ce, “Zan ɗebo wa raƙumanka ruwa su ma, har sai sun gama sha.”
20 So she hurried and emptied her jug into the trough and ran again to the well to draw, and drew for all his camels.
Sai ta yi sauri ta juye ruwan da yake tulunta cikin kwami, ta koma zuwa rijiyar da gudu don ta ƙara ɗebo ruwa, ta kuma ɗebo isashe saboda dukan raƙumansa.
21 And the man watched her in silence so as to know whether God had made his journey successful or not.
Mutumin bai ce uffam ba, ya dai kalle ta sosai don yă san ko Ubangiji ya ba shi nasara a tafiyarsa ko babu.
22 And it happened, as the camels had finished drinking, that the man took a gold ring weighing a beka, which he put on her nose, and two bracelets for her hands weighing ten pieces of gold,
Sa’ad da raƙuman suka gama shan ruwa, mutumin ya fitar da zoben hanci na zinariya mai nauyin giram biyar da woroworo biyu na zinariya masu nauyin shekel goma, ya ba ta.
23 and said, "Whose daughter are you? Please tell me, is there room in your father's house for us to lodge?"
Sa’an nan ya tambaye ta ya ce, “Ke’yar wace ce? Ina roƙonki ki faɗa mini, akwai wuri a gidan mahaifinki da za mu kwana?”
24 Then she said to him, "I am the daughter of Bethuel, the son of Milcah, whom she bore to Nahor."
Sai ta ce masa, “Ni’yar Betuwel ce ɗan da Milka ta haifa wa Nahor.”
25 And she also said to him, "We have plenty of straw and fodder, and room to lodge."
Ta ƙara da cewa, “Muna da isashen ciyawa da abincin dabbobi, da kuma wuri domin ku kwana.”
26 Then the man bowed his head and worshiped God,
Sa’an nan mutumin ya rusuna ya yi wa Ubangiji sujada,
27 and said, "Blessed be the God of my master Abraham, who has not forsaken his loving kindness and his truth toward my master. As for me, he has led me on the journey to the house of my master's relatives."
yana cewa, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah na maigidana Ibrahim, wanda bai daina nuna alheri da amincinsa ga maigidana ba. Ni kam, Ubangiji ya bishe ni a tafiyata zuwa gidan’yan’uwan maigidana.”
28 Then the young woman ran, and told her mother's household about these words.
Yariyan ta gudu ta faɗa wa mutanen gidan mahaifiyarta game da abubuwan nan.
29 Now Rebekah had a brother, and his name was Laban, and he ran out to the man at the spring.
Rebeka fa tana da wani ɗan’uwa mai suna Laban, sai ya yi hanzari ya fita zuwa wurin mutumin a rijiyar.
30 And it happened, when he saw the nose ring and the bracelets on his sister's wrists, and when he heard the words of Rebekah his sister, saying, "This is what the man said to me," that he went to the man. And look, he was standing by the camels at the spring.
Nan da nan da ya ga zoben hancin da woroworo a hannuwan’yar’uwansa, ya kuma ji Rebeka ta faɗa abin da mutumin ya ce mata, sai ya fita zuwa wurin mutumin, ya same shi yana tsaye wajen raƙuma kusa da rijiyar.
31 And he said, "Come in, you blessed of God. Why do you stand outside? For I have prepared the house and room for the camels."
Sai ya ce, “Zo, ya kai mai albarka na Ubangiji, don me kake tsaye a waje? Gama na shirya gida da wuri domin raƙuma.”
32 So the man went into the house and he unloaded the camels. And he gave straw and fodder for the camels, and water to wash his feet and the feet of the men who were with him.
Don haka mutumin ya tafi gidan, aka kuma saukar da kaya kan raƙuman. Aka kawo wa raƙuman ciyawa da abincin dabbobi, aka kuma kawo ruwa dominsa da mutanensa su wanke ƙafafunsu.
33 And he set before him food to eat, but he said, "I will not eat until I have told my message." And he said, "Say it."
Sa’an nan aka ajiye abinci a gabansa, amma ya ce, “Ba zan ci ba, sai na faɗi abin da yake tafe da ni.” Sai Laban ya ce, “Faɗa mana.”
34 So he said, "I am Abraham's servant.
Saboda haka ya ce, “Ni bawan Ibrahim ne.
35 And the Lord has blessed my master greatly, so that he has become great, and he has given him sheep and cattle, and silver and gold, and male servants and female servants, camels and donkeys.
Ubangiji ya albarkaci maigidana sosai, ya kuma zama mai arziki. Ya ba shi tumaki, shanu, azurfa, zinariya, bayi maza da mata, raƙuma, da kuma jakuna.
36 And Sarah my master's wife bore a son to my master when she was old, and to him he has given all that he has.
Saratu matar maigidana ta haifa masa ɗa a tsufanta, ya kuma ba shi duk mallakarsa.
37 Now my master put me under oath, saying, 'You must not take a wife for my son from the daughters of the Canaanites, in whose land I live,
Maigidana ya sa na yi rantsuwa, ya kuma ce, ‘Kada ka ɗauko wa ɗana mata daga’ya’ya matan Kan’aniyawa, waɗanda nake zama a ƙasarsu,
38 but you must go to my father's house, and to my relatives, and get a wife for my son.'
amma ka tafi wajen gidan mahaifina da kuma dangina, ka ɗauko wa ɗana mata.’
39 And I said to my master, 'What if the woman will not follow me?'
“Sai na ce wa maigidana, ‘A ce matar ba tă yarda tă zo tare da ni ba fa?’
40 But he said to me, 'God, before whom I walk, will send his angel with you, and make your journey successful, and you will get a wife for my son from my relatives, and of my father's house.
“Maigidana ya ce, ‘Ubangiji wanda yake tare da ni zai aiki mala’ikansa tare da kai, yă kuma sa tafiyarka tă yi nasara, don ka samo wa ɗana mata daga dangina, daga kuma gidan mahaifina.
41 Then will you be free from my oath, when you come to my relatives. And if they do not give her to you, then you will be free from my oath.'
Ta haka za ka kuɓuta daga rantsuwata sa’ad da ka tafi wurin dangina, ko ma sun ƙi su ba ka ita, za ka kuɓuta daga rantsuwata.’
42 So today I came to the spring, and said, 'God of my master Abraham, if now you will make my journey successful in which I go—
“Sa’ad da na zo rijiya a yau, na ce, ‘Ya Ubangiji Allah na maigidana Ibrahim, ina roƙonka ka ba ni nasara a tafiyar da na yi.
43 look, I am standing by this spring of water, and may it happen that the young woman who comes out to draw, to whom I will say, "Please give me a little water from your pitcher to drink,"
Duba, ina tsaye kusa da wannan rijiya; in wata yarinya ta fito domin tă ɗiba ruwa, wadda in na ce mata, “Ina roƙonki bari in ɗan sha ruwa daga tulunki,”
44 and she will say to me, "Drink, and I will also draw for your camels,"—may she be the woman who has been chosen for my master's son.'
in ta ce, “Ka sha, zan kuma ba wa raƙumanka ma,” bari tă zama wadda Ubangiji ya zaɓar wa ɗan maigidana.’
45 Before I had finished praying in my heart, look, Rebekah came out with her jug on her shoulder, and she went down to the spring, and drew. And I said to her, 'Please give me a drink.'
“Kafin in gama addu’ar, a zuciyata, sai ga Rebeka ta fito da tulunta a kafaɗarta. Ta gangara zuwa rijiyar ta ɗebo ruwa, na kuma ce mata, ‘Ina roƙonki ki ba ni ɗan ruwa daga tulunki.’
46 And she quickly lowered her jug from her shoulder, and said, 'Drink, and I will also give your camels a drink.' So I drank, and she also gave the camels water.
“Ta yi sauri ta saukar da tulun daga kafaɗarta ta ce, ‘Sha, zan kuma ba wa raƙumanka su ma.’ Sai na sha, ta kuma shayar da raƙumana su ma.
47 Then I asked her, and said, 'Whose daughter are you?' And she replied, 'The daughter of Bethuel, Nahor's son, whom Milcah bore to him.' So I put the ring on her nose, and the bracelets on her wrists.
“Na tambaye ta, ‘Ke’yar wane ne?’ “Ta ce, ‘’Yar Betuwel ɗan Nahor, wanda Milka ta haifa masa.’ “Sai na sa mata zobe a hancinta, woroworo kuma a hannuwata,
48 Then I bowed my head and worshiped God, and blessed the God of my master Abraham, who had guided me on the right road to find the granddaughter of my master's brother for his son.
na kuma sunkuya na yi wa Ubangiji sujada. Na yabi Ubangiji Allah na maigidana Ibrahim wanda ya bi da ni a hanyar da take daidai, don in samo wa ɗan maigidana jikanyar ɗan’uwansa.
49 Now if you will show kindness and truth to my master, tell me. And if not, tell me, that I may turn to the right hand, or to the left."
Yanzu fa in za ku nuna wa maigidana alheri da aminci, ku faɗa mini, in kuma ba haka ba, ku faɗa mini, don in san hanyar da zan juya.”
50 Then Laban and Bethuel answered, "The matter comes from God. We can't speak to you bad or good.
Laban da Betuwel suka ce, “Wannan daga wurin Ubangiji ne, ba abin da za mu ce I, ko a’a ba.
51 Look, Rebekah is before you. Take, and go, and let her become the wife of your master's son, as God has spoken."
Ga Rebeka, ɗauke ta ku tafi, bari tă zama matar ɗan maigidanka, yadda Ubangiji ya umarta.”
52 And it happened when Abraham's servant heard their words, that he bowed himself down to the ground.
Sa’ad da bawan Ibrahim ya ji abin da suka ce, sai ya rusuna har ƙasa a gaban Ubangiji.
53 Then the servant brought out articles of silver and articles of gold, and clothing, and gave them to Rebekah. And he also gave valuable gifts to her brother and to her mother.
Sa’an nan bawan ya fito da kayan ado na zinariya da azurfa da kayayyaki na tufafi ya ba wa Rebeka; ya kuma ba wa ɗan’uwanta da mahaifiyarta kyautai masu tsada.
54 Then he and the men who were with him ate and drank, and spent the night. Then they got up in the morning, and he said, "Send me away to my master."
Sa’an nan shi da mutanen da suke tare da shi suka ci, suka sha, suka kuma kwana a can. Kashegari da safe da suka tashi sai ya ce, “A sallame ni in koma wurin maigidana.”
55 But her brother and her mother said, "Let the young woman stay with us ten days or so. After that she may go."
Amma ɗan’uwanta da mahaifiyarta suka ce, “Bari yarinyar ta ɗan zauna tare da mu kwana goma ko fiye, sa’an nan ka ta fi.”
56 But he said to them, "Do not delay me, seeing that he has made my journey successful. Send me away that I may go to my master."
Amma ya ce musu, “Kada ku tsai da ni, tun da Ubangiji ya ba ni nasara a tafiyata. Ku sallame ni domin in tafi wurin maigidana.”
57 Then they said, "We will call the young woman and ask her."
Sa’an nan suka ce, “Bari mu kira yarinyar mu tambaye ta game da zancen.”
58 So they called Rebekah, and said to her, "Will you go with this man?" And she replied, "I will go."
Saboda haka suka kira Rebeka suka ce mata, “Za ki tafi tare da mutumin nan?” Sai ta ce, “Zan tafi.”
59 So they sent away their sister Rebekah, and her nurse, and Abraham's servant, and his men.
Saboda haka suka sallame Rebeka,’yar’uwarsu, duk da uwar goyonta da bawan Ibrahim da mutanensa.
60 And they blessed Rebekah, and said to her, "Our sister, may you be the mother of thousands of ten thousands, and may your descendants possess the gate of those who hate them."
Suka kuma albarkaci Rebeka suka ce mata, “’Yar’uwarmu, bari ki zama mahaifiyar dubu dubbai, bari zuriyarki su mallaki ƙofofin abokan gābansu.”
61 And Rebekah and her female servants got ready, and they rode on the camels and followed the man. So the servant took Rebekah and went on his way.
Sa’an nan Rebeka da bayinta mata suka shirya suka hau raƙumansu suka koma tare da mutumin. Da haka bawan ya ɗauki Rebeka ya tafi.
62 Now Isaac had come from the way of Beer Lahai Roi, for he was living in the land of the Negev.
Ishaku kuwa ya zo daga Beyer-Lahai-Royi, gama yana zama a Negeb.
63 And Isaac went out in the field to think in the early evening. And he lifted up his eyes and looked, and look, he saw camels approaching.
Wata rana da yamma ya fita zuwa fili domin yă yi tunani, sa’ad da ya ɗaga ido, sai ya ga raƙuma suna zuwa.
64 And Rebekah lifted up her eyes, and when she saw Isaac, she dismounted from the camel.
Rebeka ma ta ɗaga ido sai ta ga Ishaku. Ta sauka daga raƙuminta da sauri,
65 And she asked the servant, "Who is the man who is walking in the field to meet us?" And the servant said, "It is my master." Then she took her veil and covered herself.
ta ce wa bawan, “Wane ne mutumin can a fili, da yake zuwa yă tarye mu?” Bawan ya ce, “Maigidana ne.” Saboda haka ta ɗauki mayafinta to rufe kanta.
66 And the servant told Isaac all the things that he had done.
Sai bawan ya faɗa wa Ishaku duk abin da ya yi.
67 Then Isaac brought her into his mother Sarah's tent, and took Rebekah, and she became his wife. And he loved her. So Isaac was comforted after his mother's death.
Ishaku ya kawo ta cikin tentin mahaifiyarsa Saratu, ya kuma auri Rebeka. Ta haka ta zama matarsa, ya kuwa ƙaunace ta; Ishaku kuma ya ta’azantu bayan rasuwar mahaifiyarsa.

< Genesis 24 >