< Exodus 12 >

1 Now the LORD spoke to Moses and Aaron in the land of Egypt, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna a Masar,
2 "This month shall be to you the beginning of months. It shall be the first month of the year to you.
“Wannan wata za tă zama a gare ku wata na farko, wata na fari na shekararku.
3 Speak to all the congregation of Israel, saying, 'On the tenth day of this month, they shall take to them every man a lamb, according to their fathers' houses, a lamb for a household;
Ka faɗa wa dukan jama’ar Isra’ila cewa a rana ta goma ga wannan wata, kowane mutum zai ɗauki ɗan rago domin iyalinsa, ɗaya domin kowane gida.
4 and if the household is too little for a lamb, then he and his neighbor next to his house shall take one according to the number of the souls; according to what everyone can eat you shall make your count for the lamb.
In akwai wani gidan da ba za su iya cinye rago guda ɗungum ba, saboda iyalin kima ne, to, sai su haɗa kai da maƙwabtansu, su ɗauki rago guda gwargwadon yawansu, bisa ga abin da mutum guda zai ci.
5 Your lamb shall be without blemish, a male in its first year. You shall take it from the sheep, or from the goats:
Dabbobin da za ku zaɓa, dole su zama bana ɗaya, namiji marar tabo, za ku kuma kamo su daga cikin tumaki ko awaki.
6 and you shall keep it until the fourteenth day of the same month; and the whole assembly of the congregation of Israel shall kill it at evening.
Za ku turke dabbar har rana ta goma sha huɗu ga wata, wato, sa’ad da dukan taron jama’ar Isra’ila za su yanka ragunansu da yamma.
7 They shall take some of the blood, and put it on the two doorposts and on the lintel, on the houses in which they shall eat it.
Sa’an nan za su ɗauki jinin, su shafa a gefen da yake saman dogaran ƙofa na gidajen da suke cin naman dabbobin.
8 They shall eat the flesh in that night, roasted with fire, and unleavened bread. They shall eat it with bitter herbs.
A wannan dare, za su gasa naman, su ci da ganyaye masu ɗaci, da kuma burodi marar yisti.
9 Do not eat it raw, nor boiled at all with water, but roasted with fire; with its head, its legs and its inner parts.
Kada ku ci nama ɗanye, ko kuma dafaffe, amma a gasa shi, da kan, da ƙafafun, da kuma kayan cikin.
10 You shall let nothing of it remain until the morning; but that which remains of it until the morning you shall burn with fire.
Kada ku bar kome yă kai gobe, abin da ya kai gobe kuwa, sai ku ƙone shi.
11 This is how you shall eat it: with your waist girded, your shoes on your feet, and your staff in your hand; and you shall eat it in haste: it is the LORD's Passover.
Ga yadda za ku ci shi, ku yi ɗamara, takalma kuwa a ƙafafunku, kuna riƙe da sandunan tafiya a hannunku. Ku ci shi da gaggawa; Bikin Ƙetarewa ne na Ubangiji.
12 For I will go through the land of Egypt in that night, and will strike all the firstborn in the land of Egypt, both man and animal. Against all the gods of Egypt I will execute judgments: I am the LORD.
“A wannan dare, zan ratsa Masar, in bugi kowane ɗan fari, na mutum da na dabba, zan kuma hukunta dukan gumakan Masar. Ni ne Ubangiji.
13 The blood shall be to you for a token on the houses where you are: and when I see the blood, I will pass over you, and there shall no plague be on you to destroy you, when I strike the land of Egypt.
Jinin zai zama alama a gare ku, a gidajen da kuke; sa’ad da kuwa na ga jinin, zan ƙetare ku. Ba wata annoba mai hallakarwa da za tă taɓa ku yayinda na bugi Masar.
14 This day shall be to you for a memorial, and you shall keep it a feast to the LORD: throughout your generations you shall keep it a feast by an ordinance forever.
“Wannan rana za tă zama muku abin tunawa dukan zamananku masu zuwa, za ku kiyaye ta kamar biki ga Ubangiji, dawwammamiyar farilla ce har abada.
15 "'Seven days you shall eat unleavened bread; even the first day you shall put away yeast out of your houses, for whoever eats leavened bread from the first day until the seventh day, that soul shall be cut off from Israel.
Kwana bakwai za ku ci burodi marar yisti. A rana ta fari, za ku fid da yisti daga gidajenku gama duk wanda ya ci abu mai yisti daga rana ta fari har zuwa rana ta bakwai, za a fid da shi daga Isra’ila.
16 In the first day there shall be to you a holy convocation, and in the seventh day a holy convocation; no manner of work shall be done in them, except that which every man must eat, that only may be done by you.
A rana ta fari, za ku yi taro mai tsarki, haka kuma za ku sāke yi a rana ta bakwai. Kada ku yi aiki a waɗannan ranaku, sai dai ku shirya abinci domin kowa, abin da za ku yi ke nan kawai.
17 You shall observe the feast of unleavened bread; for in this same day have I brought your regiments out of the land of Egypt: therefore you shall observe this day throughout your generations by an ordinance forever.
“Ku yi Bikin Burodi Marar Yisti domin a wannan rana ce na fitar da ku ɓangare-ɓangare daga Masar. Ku kiyaye wannan rana ta zama muku dawwammamiyar farilla wa tsara masu zuwa.
18 In the first month, on the fourteenth day of the month at evening, you shall eat unleavened bread, until the twenty first day of the month at evening.
A wata na fari, za ku ci burodi marar yisti daga yammancin ranar goma sha huɗu har zuwa yammancin ranar ashirin da ɗaya.
19 For seven days yeast must not be found in your houses, for whoever eats that which is leavened, that person must be cut off from the congregation of Israel, whether he is a foreigner, or one who is born in the land.
Kada a sami yisti a gidajenku har kwana bakwai. Kuma duk wanda ya ci wani abu mai yisti, za a fid da shi daga taron jama’ar Isra’ila, ko baƙo ne, ko haifaffen ɗan ƙasa.
20 You must eat nothing leavened. In all your places where you live you must eat unleavened bread.'"
Kada ku ci wani abincin da aka yi da yisti. Ko’ina kuka zauna, dole ku ci burodi marar yisti.”
21 Then Moses called for all the elders of the children of Israel, and said to them, "Go and select lambs according to your clans, and kill the Passover lamb.
Sa’an nan Musa ya kira dukan dattawan Isra’ila ya ce musu, “Ku je da sauri ku zaɓi dabbobin iyalanku, ku yanka ragon Bikin Ƙetarewa.
22 And you are to take a bunch of hyssop and dip it in the blood that is in the basin, and apply it on the top and on both sides of the doorframe with the blood that is in the basin. And none of you is to go out of the door of his house until morning.
Ku ɗauki ƙunshin itacen hizzob, ku tsoma cikin jinin da yake a kwano, ku yayyafa wa dogaran ƙofa duka biyu, da bisa kan ƙofar. Kada wani daga cikinku yă fita daga ƙofar gidansa sai da safe.
23 For the LORD will pass through to strike the Egyptians, and when he sees the blood on the top and sides of the doorframe, the LORD will pass over the door and will not allow the destroyer to enter your houses to strike you.
Sa’ad da Ubangiji yake ratsa ƙasar don yă bugi Masarawa, zai ga jinin a bisa da kuma gefen madogaran ƙofa, zai ƙetare ƙofar, ba zai bar mai hallakawa yă shiga gidajenku, yă buge ku ba.
24 And you must observe this as an ordinance for you and your children forever.
“Ku kiyaye waɗannan dokokin a matsayin dawwammamiyar farilla, da ku da’ya’yanku har abada.
25 And it shall come to pass when you enter the land which the LORD will give you, as he has promised, you must keep this ceremony.
Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji zai ba ku yadda ya alkawarta, ku kiyaye wannan biki.
26 And it shall be, when your children ask you, 'What do you mean by this ceremony?'
Sa’ad da kuma’ya’yanku suka tambaye ku, ‘Mece ce manufar wannan biki?’
27 that you shall say, 'It is the sacrifice of the LORD's Passover, because he passed over the houses of the children of Israel in Egypt, when he struck the Egyptians but spared our houses.'" And the people bowed down and worshiped.
Sai ku faɗa musu, ‘Hadaya ce ta Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji, domin ya tsallake gidajen Isra’ilawa a Masar, lokacin da ya kashe Masarawa, amma bai taɓa gidajenmu ba.’” Sai mutane suka rusuna, suka yi sujada.
28 Then the children of Israel went away and did as the LORD had commanded Moses and Aaron, so they did.
Isra’ilawa suka tafi suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa da Haruna.
29 And it came to pass at midnight that the LORD killed all the firstborn in the land of Egypt, from the firstborn of Pharaoh who sat on his throne to the firstborn of the prisoner who was in the prison, and all the firstborn of livestock.
Da tsakar dare, sai Ubangiji ya karkashe dukan’ya’yan fari a ƙasar Masar, tun daga ɗan farin Fir’auna, wato, magājinsa, har zuwa ɗan fari na ɗan sarƙa da yake kurkuku, har da’ya’yan fari na dabbobi.
30 And Pharaoh got up during the night, he, and all his servants, and all Egypt, and there was loud wailing in Egypt, for there was not a house where there was not someone dead.
Fir’auna da dukan fadawansa da kuma dukan Masarawa, suka tashi a cikin daren da kuka mai zafi, aka kuma ji kukan a ko’ina a cikin ƙasar Masar, gama ba gidan da ba a yi mutuwa ba.
31 Then he summoned for Moses and Aaron during the night, and said, "Get up, get out from among my people, both you and the children of Israel; and go, serve the LORD, as you have requested.
A cikin daren, Fir’auna ya aika a kira Musa da Haruna ya ce, “Ku tashi, ku da jama’arku, ku fita daga cikin jama’ata. Ku tafi, ku bauta wa Ubangiji yadda kuka ce.
32 Take your flocks and your herds, as you have requested, and be gone, but bless me also."
Ku kwashi garkunanku na tumaki da na awaki, da na shanu, ku yi tafiyarku kamar yadda kuka ce, amma ku sa mini albarka.”
33 The Egyptians were urgent with the people to send them out of the land quickly, for they said, "We will all be dead."
Masarawa suka matsa wa Isra’ilawa su fita daga ƙasarsu da sauri. Gama mutanen Masar sun ce, “Ai, za mu mutu duka, in ba su tafi ba!”
34 So the people took their dough before it was leavened, with their kneading bowls wrapped in their clothing on their shoulders.
Sai mutanen suka ɗauki garin da sun kwaɓa ba yisti a ciki, tare da ƙwaryansu na aikin kwaɓan, suka nannaɗe su a mayafansu, suka rataye a kafaɗunsu.
35 Now the children of Israel did according to what Moses told them, for they had asked the Egyptians for articles of silver and articles of gold and clothing.
Isra’ilawa kuwa suka yi yadda Musa ya umarce su, suka roƙi Masarawa kayan adonsu na azurfa da na zinariya, da kuma tufafi.
36 And the LORD gave the people favor in the sight of the Egyptians, and they gave them whatever they wanted. And so they plundered Egypt.
Ubangiji kuwa ya sa Isra’ilawa suka yi farin jini a wurin Masarawa, Masarawa kuma suka saki hannu wa mutanen, suka ba su duk abin da suka roƙa; ta haka Isra’ilawa suka washe Masarawa.
37 And the children of Israel traveled from Rameses to Succoth, about six hundred thousand men on foot, besides their dependents.
Isra’ilawa suka kama tafiya daga Rameses zuwa Sukkot. Akwai maza dubu ɗari shida da suke tafiya da ƙafa, ban da mata da yara.
38 And a mixed crowd also went up with them, and a huge number of livestock, both flocks and herds.
Waɗansu mutane da yawa da ba Isra’ilawa ba, suka haura tare da su, da garkunan shanu, da na tumaki da awaki.
39 And they baked unleavened loaves using the dough that they had brought out of Egypt; for it wasn't leavened, because they were thrust out of Egypt, and couldn't wait, nor had they prepared any provisions for themselves.
Suka toya burodi marar yisti da garin da aka kwaɓa wanda suka kawo daga Masar. Garin da aka kwaɓan ba shi da yisti, domin an kore su daga Masar, ba su kuwa sami damar shirya wa kansu abinci ba.
40 Now the time that the children of Israel lived in Egypt was four hundred and thirty years.
Zaman da Isra’ilawa suka yi a Masar, ya kai shekara 430.
41 And it came to pass at the end of four hundred thirty years, to the day, it came to pass that all the regiments of the LORD went out from the land of Egypt.
A ranar da shekara 430 ɗin nan suka cika, a ran nan ne dukan ɓangare-ɓangare na mutanen Ubangiji suka bar Masar.
42 It was a night when the LORD kept vigil to bring them out from the land of Egypt. So on this night all the children of Israel must keep a vigil to the LORD throughout their generations.
Gama Ubangiji ya yi tsaro a wannan dare, domin yă fitar da su daga Masar, a wannan dare, dole dukan Isra’ilawa su yi tsaro, don su girmama Ubangiji, cikin dukan tsararraki masu zuwa.
43 And the LORD said to Moses and Aaron, "This is the ordinance of the Passover. No foreigner may eat of it,
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna, “Waɗannan ne ƙa’idodin Bikin Ƙetarewa. “Ba baƙon da zai ci shi.
44 but every man's servant who is bought for money, after you have circumcised him, may he eat of it.
Duk bawan da kuka sayo, yana iya ci, in dai an yi masa kaciya,
45 A foreigner and a hired servant must not eat of it.
amma wanda ba ya zama tare da ku na ɗinɗinɗin, da kuma wanda aka ɗauki hayansa, ba zai ci ba.
46 It is to be eaten in one house. You must not take any of the meat outside the house, and you are not to break any of its bones.
“Dole a ci shi a cikin gida ɗaya; kada a kai naman waje. Kada a karya wani daga ƙasusuwansa.
47 All the congregation of Israel is to keep it.
Dole dukan taron jama’ar Isra’ila su yi bikin.
48 If a foreigner lives with you and wants to keep the Passover to the LORD, all his males must be circumcised, and then he may take part and observe it, and he will be like one who is born in the land. But no uncircumcised person may eat of it.
“Baƙon da yake zama tare da ku da yake so yă yi Bikin Ƙetarewar Ubangiji, dole yă yi wa dukan mazan da suke cikin gidansa kaciya; sa’an nan ne zai iya yin abubuwa kamar haifaffen ɗan ƙasa.
49 The same law will apply to the native-born and to the foreigner who lives among you."
Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ta shafi ɗan ƙasa da kuma baƙon da yake zama a tsakaninku.”
50 So all the children of Israel did as the LORD commanded Moses and Aaron, so they did.
Dukan Isra’ilawa suka yi na’am da shi, suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa da Haruna.
51 And it happened on this very day that the LORD brought the children of Israel out of the land of Egypt by their regiments.
A wannan rana, Ubangiji ya fito da Isra’ilawa ɓangare-ɓangare daga Masar.

< Exodus 12 >