< 1 Kings 1 >

1 Now king David was old and advanced in years; and they covered him with clothes, but he couldn't keep warm.
Sa’ad da Sarki Dawuda ya tsufa ya kuma ƙara shekaru, ba ya iya jin ɗumi ko an rufe shi da abin rufuwa.
2 Therefore his servants said to him, "Let there be sought for my lord the king a young virgin. And let her attend the king, and care for him; and let her lie in your bosom, that my lord the king may keep warm."
Saboda haka bayinsa suka ce masa, “Bari mu nemi wata budurwa wadda za tă yi wa ranka yă daɗe, sarki hidima, tă kuma kula da shi. Za tă dinga kwanta kusa da ranka yă daɗe, yă ji ɗumi.”
3 So they sought for a beautiful young woman throughout all the borders of Israel, and found Abishag the Shunammite, and brought her to the king.
Suka nemi kyakkyawar yarinya cikin fāɗin Isra’ila, sai suka sami Abishag, mutuniyar Shunam, suka kawo ta wa sarki.
4 The young woman was very beautiful; and she became the king's attendant and served him; but the king did not know her intimately.
Yarinyar kuwa kyakkyawa ce ƙwarai; ta kuwa lura da sarki, ta kuma yi masa hidima, amma sarki bai yi jima’i da ita ba.
5 Then Adonijah the son of Haggith exalted himself, saying, "I will be king." So he prepared for himself chariots and horsemen, and fifty men to run before him.
Adoniya, wanda mahaifiyarsa ce Haggit, ya fito ya ce, “Zan zama sarki.” Saboda haka ya nemi kekunan yaƙi, ya kuma shirya dawakai, tare da mutane hamsin da za su sha gabansa.
6 His father had never scolded him at any time by saying, "Why have you done so?" And he was also a very handsome man; and he was born after Absalom.
(A duk rayuwarsa mahaifinsa bai taɓa tsawata masa yă ce, “Me ya sa kake yin haka ba?” Shi kuwa mai kyan gani ne ƙwarai, shi ne aka haifa bayan Absalom.)
7 And he conferred with Joab the son of Zeruiah, and with Abiathar the priest. And they followed Adonijah and helped him.
Adoniya ya haɗa baƙi da Yowab ɗan Zeruhiya da kuma Abiyatar firist, suka kuma ba shi goyon baya.
8 But Zadok the priest, and Benaiah the son of Jehoiada, and Nathan the prophet, and Shimei, and Rei, and the mighty men who belonged to David, were not with Adonijah.
Amma Zadok firist, Benahiya ɗan Yehohiyada, annabi Natan, Shimeyi, Reyi da kuma matsara na musamman na Dawuda ba su bi Adoniya ba.
9 And Adonijah sacrificed sheep and oxen and fatlings by the stone of Zoheleth, which is near En Rogel; and he called all his brothers, the king's sons, and all the men of Judah, the king's servants:
Wata rana Adoniya ya tafi Dutsen Zohelet kusa da En Rogel, inda ya yi hadayar tumaki, da shanun noma, da shanun da ake kiwo a gida. Ya kuma gayyaci’yan’uwansa, wato, sauran’ya’yan Sarki Dawuda, tare da dukan dattawan sarki da suka fito daga Yahuda,
10 but he did not invite Nathan the prophet, or Benaiah, or the mighty men, or his brother Solomon.
amma bai gayyaci annabi Natan, ko Benahiya, ko wani daga matsara na musamman, ko kuwa ɗan’uwansa Solomon ba.
11 Then Nathan spoke to Bathsheba the mother of Solomon, saying, "Haven't you heard that Adonijah the son of Haggith reigns, and David our lord doesn't know it?
Sai Natan ya ce wa Batsheba, mahaifiyar Solomon, “Ki san cewa Adoniya, ɗan Haggit, ya zama sarki ba tare da sanin ranka yă daɗe, sarkinmu Dawuda ba?
12 Now therefore come, please let me give you advice, that you may save your own life, and the life of your son Solomon.
Yanzu bari in ba ki shawara yadda za ki cece ranki da kuma ran ɗanki Solomon.
13 Go in to king David, and tell him, 'Did you not, my lord, king, swear to your handmaid, saying, "Surely Solomon your son shall be king after me, and he shall sit on my throne"? Why then does Adonijah reign?'
Ki shiga wurin Sarki Dawuda ki ce masa, ‘Ranka yă daɗe sarki, ba ka rantse mini ni baiwarka cewa, “Tabbatacce Solomon ɗanka ne zai zama sarki bayana, yă kuma zauna a kujerar sarautar ba”? To, me ya sa Adoniya ya zama sarki?’
14 And look, while you are still there speaking with the king, I also will come in after you and confirm your words."
Yayinda kike can kina magana da sarki, zan shiga in kuma tabbatar da abin da kika faɗa.”
15 Bathsheba went in to the king into the room. The king was very old; and Abishag the Shunammite was attending to the king.
Saboda haka Batsheba ta je don tă ga sarki. A yanzu dai sarki ya tsufa, yana nan kuma a cikin ɗakinsa, inda Abishag mutuniya Shunam take masa hidima.
16 Bathsheba bowed, and showed respect to the king. The king said, "What would you like?"
Batsheba ta rusuna ta kuma durƙusa a gaban sarki. Sai sarki ya tambaye ta ya ce, “Me kike so?”
17 And she said to him, "My lord, you swore by the LORD your God to your handmaid, 'Assuredly Solomon your son shall be king after me, and he shall sit on my throne.'
Ta ce masa, “Ranka yă daɗe, kai kanka ka rantse mini ni baiwarka da sunan Ubangiji Allahnka cewa, ‘Solomon ɗanka zai zama sarki bayana, zai kuma zauna a kujerar sarautata.’
18 Now, look, Adonijah reigns; and you, my lord the king, do not know it.
Amma yanzu Adoniya ya zama sarki, kai kuwa ranka yă daɗe sarki, ba ka san wani abu game da shi ba.
19 And he has sacrificed many oxen and fatlings and sheep, and has invited all the sons of the king, and Abiathar the priest, and Joab the commander of the army; but he hasn't invited Solomon your servant.
Ya miƙa hadayun shanu, da shanun da ake kiwo a gida, da tumaki masu yawa, ya kuma gayyaci dukan’ya’yan sarki maza, da Abiyatar firist, da Yowab shugaban mayaƙa, amma bai gayyaci Solomon bawanka ba.
20 And now, my lord the king, the eyes of all Israel are on you to announce to them who shall sit on the throne of my lord the king after him.
Ranka yă daɗe sarki, idanun dukan Isra’ila suna a kanka, domin su san wa zai zauna a kujerar ranka yă daɗe sarkina, a bayanka.
21 Otherwise it will happen, when my lord the king shall sleep with his fathers, that I and my son Solomon will be considered criminals."
In ba haka, bayan an binne ranka yă daɗe sarki, tare da kakanninsa, za a wulaƙance ni da Solomon ɗana, kamar masu laifi.”
22 And look, while she was still speaking with the king, Nathan the prophet came in.
Yayinda take cikin magana tare da sarki, sai annabi Natan ya iso.
23 And they told the king, saying, "Look, Nathan the prophet." And when he came in before the king, he bowed himself before the king with his face to the ground.
Sai aka faɗa wa sarki, “Ga annabi Natan.” Da Natan ya je gaban sarki, sai ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
24 And Nathan said, "My lord, king, have you said, 'Adonijah shall be king after me, and he shall sit on my throne?'
Natan ya ce, “Ranka yă daɗe, sarki, ko ka furta cewa Adoniya ne zai zama sarki a bayanka, yă kuma zauna a kujerar sarautarka?
25 For he has gone down today and has sacrificed oxen and fatlings and sheep in abundance, and has invited all the king's sons, and the commanders of the army, and Abiathar the priest. Look, they are eating and drinking before him, and say, 'Long live king Adonijah.'
Yau ya gangara, ya kuma miƙa hadayun shanu, da shanun da ake kiwo a gida, da tumaki masu yawa. Ya gayyaci dukan’ya’yan sarki maza, da shugaban mayaƙa, da kuma Abiyatar firist. A yanzu haka suna ci, suna sha, tare da shi, suna cewa, ‘Ran Sarki Adoniya yă daɗe!’
26 But me, me your servant, and Zadok the priest, and Benaiah the son of Jehoiada, and your servant Solomon, he has not invited.
Amma bai gayyace ni bawanka, da Zadok firist, da Benahiya ɗan Yehohiyada, da kuma bawanka Solomon ba.
27 Has this thing been brought about by my lord the king, and you haven't told your servants who should sit on the throne of my lord the king after him?"
Ranka yă daɗe, sarki, ko ka tabbatar da haka, amma ba ka ko faɗa wa fadawanka, cewa ga wanda zai gāje Ranka yă daɗe, sarki ba?”
28 Then king David answered, "Summon Bathsheba to me." So she came into the king's presence, and stood before him.
Sai Dawuda ya ce, “Kira Batsheba tă shiga.” Sai ta zo gaban sarki ta kuma tsaya a gabansa.
29 And the king vowed, saying, "As the LORD lives, who has redeemed my soul out of all adversity,
Sai sarki ya yi rantsuwa, “Muddin Ubangiji yana a raye, wanda ya cece ni daga kowace damuwa,
30 most certainly as I vowed to you by the LORD, the God of Israel, saying, 'Assuredly Solomon your son shall be king after me, and he shall sit on my throne in my place;' so I certainly will do this day."
tabbatacce a yau zan aikata abin da na yi miki rantsuwa da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila; Solomon ɗanki zai zama sarki bayana, kuma shi zai zauna a kan kujerar sarautata a maimakona.”
31 Then Bathsheba bowed with her face to the ground, paying homage to the king, and said, "Let my lord king David live forever."
Sai Batsheba ta rusuna da fuskarta har ƙasa, ta kuma durƙusa a gaban sarki ta ce, “Bari ran Sarkina Dawuda yă daɗe, har abada!”
32 And King David said, "Summon to me Zadok the priest, Nathan the prophet, and Benaiah the son of Jehoiada." They came before the king.
Sarki Dawuda ya ce, “Ku kira mini Zadok firist, annabi Natan, da Benahiya ɗan Yehohiyada.” Da suka zo gaban sarki,
33 The king said to them, "Take with you the servants of your lord, and have Solomon my son ride on my own mule, and bring him down to Gihon.
sai ya ce musu, “Ku ɗauki bayin sarki tare da ku, ku kuma sa ɗana Solomon a kan dokina, ku gangara da shi zuwa Gihon.
34 And have Zadok the priest and Nathan the prophet anoint him there king over Israel. Blow the trumpet, and say, 'Long live king Solomon.'
A can ku sa Zadok firist, da annabi Natan su shafe shi sarki a bisa Isra’ila. Ku busa ƙaho, ku kuma yi ihu, kuna cewa, ‘Ran Sarki Solomon yă daɗe!’
35 Then you shall come up after him, and he shall come and sit on my throne; for he shall be king in my place. I have appointed him to be prince over Israel and over Judah."
Sa’an nan ku haura tare da shi, zai kuwa zo yă zauna a kujera sarautata, yă yi mulki a maimakona. Na naɗa shi mai mulki a bisa Isra’ila da Yahuda.”
36 Benaiah the son of Jehoiada answered the king, and said, "Amen. May the LORD, the God of my lord the king, say so.
Benahiya ɗan Yehohiyada ya amsa wa sarki, ya ce, “Amin! Bari Ubangiji Allah na ranka yă daɗe sarkina, yă tabbatar da haka.
37 As the LORD has been with my lord the king, even so may he be with Solomon, and make his throne greater than the throne of my lord king David."
Kamar yadda Ubangiji ya kasance da ranka yă daɗe, sarki, haka ma bari yă kasance da Solomon, yă kuma mai da kujerar sarautarsa tă fi kujerar sarautar ranka yă daɗe, Sarki Dawuda, girma!”
38 So Zadok the priest, and Nathan the prophet, and Benaiah the son of Jehoiada, and the Cherethites and the Pelethites, went down, and caused Solomon to ride on king David's mule, and brought him to Gihon.
Sai Zadok firist, annabi Natan, Benahiya ɗan Yehohiyada, Keretawa, da Feletiyawa suka gangara, suka sa Solomon a kan dokin Sarki Dawuda, suka raka shi zuwa Gihon.
39 Zadok the priest took the horn of oil out of the Tent, and anointed Solomon. They blew the trumpet; and all the people said, "Long live king Solomon."
Zadok firist ya ɗauki ƙahon mai daga tenti mai tsarki, ya shafe Solomon. Sa’an nan suka busa ƙaho, sai dukan mutane suka yi ihu, suna cewa “Ran Sarki Solomon yă daɗe!”
40 All the people came up after him, and the people piped with pipes, and rejoiced with great joy, so that the earth split open at their sound.
Dukan mutane kuwa suka haura suka bi shi, suna busan sarewa, suna farin ciki sosai, har ƙasa ta girgiza saboda sowa.
41 Adonijah and all the guests who were with him heard it as they had made an end of eating. When Joab heard the sound of the trumpet, he said, "Why is this noise of the city being in an uproar?"
Adoniya tare da dukan baƙin da suke tare da shi kuwa suka ji wannan sa’ad da suke gama bikinsu. Da jin busan ƙaho, sai Yowab ya yi tambaya, ya ce, “Me ya jawo surutu haka a birni?”
42 While he yet spoke, look, Jonathan the son of Abiathar the priest came: and Adonijah said, "Come in; for you are a worthy man, and bring good news."
Tun yana cikin magana, sai Yonatan ɗan Abiyatar ya iso. Adoniya ya ce, “Shigo! Ai, mutumin kirki irinka, lalle ka kawo labari mai daɗi ne.”
43 Jonathan answered Adonijah, "No. Our lord king David has made Solomon king.
Yonatan ya ce wa Adoniya, “A ina! Ranka yă daɗe, Sarkinmu Dawuda ya naɗa Solomon sarki.
44 The king has sent with him Zadok the priest, Nathan the prophet, Benaiah the son of Jehoiada, and the Cherethites and the Pelethites; and they have caused him to ride on the king's mule.
Sarki ya aika shi tare da Zadok firist, annabi Natan, Benahiya ɗan Yehohiyada, Keretawa, da Feletiyawa, suka sa shi a kan dokin sarki,
45 Zadok the priest and Nathan the prophet have anointed him king in Gihon. They have come up from there rejoicing, so that the city rang again. This is the noise that you have heard.
Zadok firist kuwa da annabi Natan sun shafe shi sarki a Gihon. Daga can suka haura suna kirari, birni kuwa ta ɓarke da sowa. Surutun da kake ji ke nan.
46 Also, Solomon sits on the throne of the kingdom.
Ban da haka ma, Solomon ne sarki yanzu.
47 Moreover the king's servants came to bless our lord king David, saying, 'May your God make the name of Solomon better than your name, and make his throne greater than your throne;' and the king bowed himself on the bed.
Yanzu haka, fadawa sun zo suna wa ranka yă daɗe, Sarki Dawuda, sam barka, suna cewa, ‘Bari Allahnka yă sa sunan Solomon yă zama sananne fiye da naka, bari kuma sarautarsa tă fi taka girma!’ Sarki kuwa ya rusuna, ya yi sujada a kan gadonsa
48 Also thus said the king, 'Blessed be the LORD, the God of Israel, who has given one to sit on my throne this day, my eyes even seeing it.'"
ya ce, ‘Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya bar idanuna suka ga magāji a kan kujerar sarautata a yau.’”
49 All the guests of Adonijah were afraid, and rose up, and each man went his way.
A nan fa, dukan baƙin Adoniya suka taso da rawar jiki suka watse.
50 Adonijah feared because of Solomon; and he arose, and went, and caught hold on the horns of the altar.
Amma Adoniya, don tsoron Solomon, ya je ya kama ƙahon bagade ya riƙe.
51 It was told Solomon, saying, "Look, Adonijah fears king Solomon; for, look, he has laid hold on the horns of the altar, saying, 'Let king Solomon swear to me first that he will not kill his servant with the sword.'"
Sa’ad da aka faɗa wa Solomon cewa, “Adoniya yana tsoron Sarki Solomon, kuma ya manne wa ƙahonin bagade. Yana cewa, ‘Bari Sarki Solomon yă rantse mini a yau cewa ba zai kashe bawansa da takobi ba.’”
52 Solomon said, "If he shows himself a worthy man, not a hair of him shall fall to the earth; but if wickedness be found in him, he shall die."
Solomon ya amsa ya ce, “In ya nuna kansa mai biyayya, ba gashin kansa da zai fāɗi ƙasa; amma in aka same mugunta a cikinsa, zai mutu.”
53 So king Solomon sent, and they brought him down from the altar. He came and bowed down to king Solomon; and Solomon said to him, "Go to your house."
Sai Sarki Solomon ya aiki mutane, suka kuma sauko da shi daga bagade. Adoniya kuwa ya zo, ya rusuna wa Sarki Solomon, sai Solomon ya ce, “Tafi gidanka.”

< 1 Kings 1 >