< Matthew 18 >

1 In that hour the disciples came to Jesus, saying, "Who then is greatest in the kingdom of heaven?"
Daidai wannan lokacin, almajiran suka zo wurin Yesu suka ce, ''Wanene mafi girma a mulkin sama?''
2 He called a little child to himself, and set him in the midst of them,
Sai Yesu ya kira karamin yaro gunsa, ya sa shi a tsakaninsu,
3 and said, "Truly I tell you, unless you turn, and become as little children, you will in no way enter into the kingdom of heaven.
ya ce, ''Hakika ina gaya maku, idan baku juya kun zama kamar kananan yara ba, babu yadda zaku shiga mulkin sama.
4 Whoever therefore humbles himself as this little child, the same is the greatest in the kingdom of heaven.
Saboda haka, duk wanda ya kaskantar da kansa kamar karamin yaron nan, shi ne mafi girma a mulkin sama.
5 Whoever receives one such little child in my name receives me,
Duk wanda ya karbi karamin yaro a suna na, ya karbe ni.
6 but whoever causes one of these little ones who believe in me to stumble, it would be better for him that a huge millstone should be hung around his neck, and that he should be sunk in the depths of the sea.
Amma duk wanda ya sa daya daga cikin 'yan yaran nan da suka gaskanta da ni zunubi, gwamma a rataya dutsen nika a wuyansa a jefa shi cikin zurfin teku.
7 "Woe to the world because of stumbling blocks. For there will always be something to cause people to stumble, but woe to the person through whom the stumbling block comes.
Kaiton duniya saboda lokacin tuntube! Lallai ne wadannan lokuta su zo, amma kaiton mutumin da ta wurinsa ne wadannan lokutan za su zo!
8 If your hand or your foot causes you to stumble, cut it off, and cast it from you. It is better for you to enter into life maimed or crippled, rather than having two hands or two feet to be cast into the everlasting fire. (aiōnios g166)
Idan hannunka ko kafarka ce za ta sa ka tuntube, ka yanke ta, ka yar daga gare ka. Zai fi maka kyau ka shiga rai da nakasa ko gurguntaka, da a jefa ka cikin madawwamiyar wuta tare da hannayenka ko kafafunka. (aiōnios g166)
9 If your eye causes you to stumble, pluck it out, and cast it from you. It is better for you to enter into life with one eye, rather than having two eyes to be cast into the fire of hell. (Geenna g1067)
Idan idonka zai sa ka tuntube, ka kwakule shi, ka yar. Zai fi maka kyau ka shiga rai da ido daya, da a jefa ka cikin madawwamiyar wuta da idanu biyu. (Geenna g1067)
10 See that you do not despise one of these little ones, for I tell you that in heaven their angels always see the face of my Father who is in heaven.
Ku kula fa kada ku rena kananan nan. Domin koyaushe a sama, mala'ikunsu na duban fuskar Ubana da ke sama.
[Dan Mutum ya zo ya ceci abinda ya bata].
12 "What do you think? If someone has one hundred sheep, and one of them goes astray, does he not leave the ninety-nine, go to the mountains, and seek that which has gone astray?
Menene tunaninku? Idan mutum na da tumaki dari, sa'annan daya ta bata, ashe ba zai bar tassa'in da tara a gefen tudu ya tafi neman wadda ta bata ba?
13 If he finds it, truly I tell you, he rejoices over it more than over the ninety-nine which have not gone astray.
In ya same ta, hakika ina gaya maku, farin cikinsa na samun dayan nan da ta bace, zai fi na tassa'in da taran nan da basu bata ba.
14 Even so it is not the will of my Father who is in heaven that one of these little ones should perish.
Hakanan fa, ba nufin Ubanku dake sama ba ne da ya daga cikin wadannan kananan ya hallaka.
15 "If your brother sins against you, go, show him his fault between you and him alone. If he listens to you, you have gained back your brother.
Idan dan'uwanka yayi maka laifi, fada masa tsakaninku, kai da shi kadai. Idan ya saurare ka, ka maido da dan'uwanka kenan.
16 But if he does not listen, take one or two more with you, that at the mouth of two or three witnesses every word may be established.
Amma in ya ki ya saurare ka, ka je da 'yan'uwa biyu ko uku su zama shaidu, don ta wurin shaidu biyu ko uku ake tabbatar da kowacce kalma.
17 If he refuses to listen to them, tell it to the church. If he refuses to hear the church also, let him be to you as an unbeliever or a tax collector.
In kuma ya ki ya saurare su, ka kai lamarin ga ikklisiya. Idan ya ki ya saurari ikklisiya, ka maishe shi ba'al'umme da mai karbar haraji.
18 Truly I tell you, whatever you bind on earth will be bound in heaven, and whatever you loose on earth will be loosed in heaven.
Hakika ina gaya maku, duk abin da kuka daure a duniya, a daure yake a sama. Abin da kuka kwance kuma, a kwance yake a sama.
19 Again, truly I tell you, that if two of you agree on earth concerning anything that they will ask, it will be done for them by my Father who is in heaven.
Kuma ina gaya maku, idan mutum ku biyu zaku yarda akan duk abin da zaku roka, Ubana wanda ke a sama zai yi maku shi.
20 For where two or three are gathered together in my name, there I am in the midst of them."
Wurin da mutum biyu ko uku suka taru a cikin sunana, zan kasance tare da su.''
21 Then Peter came to him and said, "Lord, how often can my brother sin against me, and I forgive him? Up to seven times?"
Bitrus ya zo ya ce wa Yesu, ''Ubangiji, sau nawa ne dan'uwana zai yi mani laifi in gafarta masa? Har sai ya kai sau bakwai?''
22 Jesus said to him, "I do not tell you up to seven times, but up to seventy times seven.
Yesu ya amsa ya ce masa, ''Ban gaya maka sau bakwai ba, amma bakwai din ma har sau saba'in.
23 Therefore the kingdom of heaven is like a certain king, who wanted to reconcile accounts with his servants.
Saboda haka, za a kwatanta mulkin sama da wani sarki da yake so ya lisafta dukiyarsa dake a hannun barorinsa.
24 When he had begun to reconcile, one was brought to him who owed him ten thousand talents.
Da ya fara yin haka, sai aka kawo masa daya daga cikin barorinsa da yake binsa talanti dubu goma.
25 But because he could not pay, his lord commanded him to be sold, with his wife and children, and all that he had, and payment to be made.
Amma tunda ba shi da abin biya, ubangidansa ya bada umurni a sayar da shi, tare da matarsa da 'ya'yansa da duk mallakarsa, domin a biya.
26 The servant therefore fell down and kneeled before him, saying, 'Lord, have patience with me, and I will repay you all.'
Sai baran ya fadi kasa, ya rusuna a gaban ubangidansa ya ce, “Maigida, kayi mani hakuri, zan biya duk abin da na karba.”
27 The lord of that servant, being moved with compassion, released him, and forgave him the debt.
Don haka ubangidansa yayi juyayi, sai ya ce, ya yafe bashin, a saki baran.
28 "But that servant went out, and found one of his fellow servants, who owed him one hundred denarii, and he grabbed him, and took him by the throat, saying, 'Pay what you owe.'
Amma bayan an saki wannan baran, ya je ya sami wani baran kamar sa da yake bi bashin dinari dari. Ya cafke shi, ya shake shi a wuya, ya ce, 'Ka biya bashin da nake bin ka.'
29 "So his fellow servant fell down at his feet and begged him, saying, 'Have patience with me, and I will repay you all.'
Amma dan'uwansa bara ya roke shi ya ce, kayi mani hakuri, zan biya ka duk abinda na karba.'
30 He would not, but went and cast him into prison, until he should pay back that which was due.
Amma baran nan na farko ya ki. A maimakon haka, ya sa aka jefa dan'uwansa bara a kurkuku sai ya biya bashin nan.
31 So when his fellow servants saw what was done, they were exceedingly sorry, and came and told to their lord all that was done.
Da sauran barori suka ga abin da ya faru, suka damu kwarai. Sai suka je suka fada wa ubangidansu yadda abin ya faru duka.
32 Then his lord called him in, and said to him, 'You wicked servant. I forgave you all that debt, because you begged me.
Sai ubangidansa ya kirawo shi, ya ce masa, ''Kai mugun bawa, na gafarta maka bashin nan duka, domin ka roke ni.
33 Should you not also have had mercy on your fellow servant, even as I had mercy on you?'
Ashe, bai kamata kaima ka nuna jinkai ga dan'uwanka bara kamar yadda na nuna maka jinkai ba?'
34 His lord was angry, and delivered him to the tormentors, until he should pay all that was due.
Ubangidansa yayi fushi, ya danka shi ga masu azabtarwa, har sai ya gama biyan dukan bashin da ake binsa.
35 So my heavenly Father will also do to you, if you do not each forgive your brother his trespasses from your heart."
Hakanan Ubana dake a sama zai yi maku, idan kowannenku bai gafarta wa dan'uwansa daga zuciya ba.''

< Matthew 18 >