< Mark 7 >

1 Then the Pharisees, and some of the scribes gathered together to him, having come from Jerusalem.
Farisawa suka taru wurin Yesu tare da wadansu marubuta wadda suka zo daga Urushalima.
2 Now when they saw some of his disciples eating bread with defiled, that is, unwashed, hands, they found fault.
Sun ga cewa wasu daga cikin almajiransa sun ci gurasa da hannuwa marasa tsabta, wato, basu wanke hannu ba,
3 (For the Pharisees, and all Jewish people, do not eat unless they wash their hands and forearms, holding to the Tradition of the Elders.
(Domin Farisawa da dukan Yahudawa ba su cin abinci sai dole sun wanke hannu da kyau domin suna kiyaye al'adun dattawa.
4 They do not eat when they come from the marketplace unless they wash. And there are many other things which they have received and hold to, the washing of cups and pitchers and copper vessels and dining couches.)
Idan Farisawa suka dawo daga kasuwa, wajibi ne su yi wanka kamin su ci abinci. Akwai sauran al'adun da suke kiyayewa, kamar wanke moda, tukwane, da wasu santula na dalma, har da dakin cin abinci.)
5 The Pharisees and the scribes asked him, "Why do your disciples not walk according to the Tradition of the Elders, but eat their bread with unwashed hands?"
Farisawa da Marubuta suka tambaye Yesu, “Don me almajiran ka basu kiyaye al'adun dattawa, domin suna cin abinci ba tare da sun wanke hannu ba?”
6 He said to them, "Well did Isaiah prophesy of you hypocrites, as it is written, 'This people honors me with their lips, but their heart is far from me.
Amma ya amsa masu cewa, “Ishaya ya yi anabci akan ku masu bautan ganin ido, da ya rubuta cewa 'wadanan mutane suna girmama ni a baka amma zuciyar su tana nesa da ni.
7 And in vain do they worship me, teaching instructions that are the commandments of humans.'
Sujadar wofi suke mani suna koyar da ka'idodi na mutane a matsayin rukunansu'”.
8 "For you set aside the commandment of God, and hold tightly to human tradition."
Kun watsar da dokar Allah sai kuka rungumi al'adun mutane.
9 He said to them, "Full well do you reject the commandment of God, that you may establish your tradition.
Sai yace masu, kun yi nasara wurin kau da dokokin Allah domin ku kiyaye al'adun ku na mutane.
10 For Moses said, 'Honor your father and your mother;' and, 'Anyone who speaks evil of father or mother, let him be put to death.'
Koda shike Musa ya rubuta cewa, “ka girmama Ubanka da Uwarka”, kuma, “duk wanda ya zagi Ubansa ko Uwatasa, ya cancanci mutuwa nan take”.
11 But you say, 'If anyone tells his father or mother, "Whatever profit you might have received from me is Corban, that is to say, given to God;"'
Amma kun ce, 'idan mutum ya ce wa iyayensa, “duk taimakon da ya cacanci ku samu daga guna ya zama kebabbe (wato, 'na mika wa Allah)”'.
12 then you no longer allow him to do anything for his father or his mother,
Sabo da haka, kun ba shi izini kada ya yi wa Ubansa ko Uwatasa wani abu.
13 making void the word of God by your tradition, which you have handed down. You do many things like this."
Kuna mayar da dokan Allah abin banza, sabili da al'adun ku da kuka mika masu. Wannan, da wasu abubuwa kamar haka kuke yi.”
14 And he called the crowd to himself again, and said to them, "Hear me, all of you, and understand.
Ya kara kiran taron jama'ar yace masu, “ku kasa kunne gareni, kuma ku gane.
15 There is nothing from outside of the person, that going into him can defile him; but the things which proceed out of the person are what defile the person."
Babu wani abu daga wajen mutum da zai iya gurbatar da shi har idan ya shiga cikinsa. Amma, abinda ya fita daga cikinsa shike gurbatar da shi”
Bari mai kunnen ji, ya ji.
17 When he had entered into a house away from the crowd, his disciples asked him about the parable.
Da Yesu ya bar taron jama'ar, ya shiga gida, sai almajiransa suka tambaye shi ma'anar wannan misali.
18 He said to them, "Are you thus without understanding also? Do you not perceive that whatever goes into the person from outside cannot defile him,
Sai Yesu yace, 'ashe baku da ganewa? ko baku sani cewa abin da ya shiga cikin mutum daga waje ba zai iya gurbatar da shi ba,
19 because it does not go into his heart, but into his stomach, then into the latrine, cleansing all the foods?"
domin ba zai iya kai wa cikin zuciyarsa ba, sai dai ya shiga cikin sa ya kuma fita a matsayin bayan gari a salga”. Da wannan magana, Yesu ya mayar da dukan abinci ya zama da tsabta.
20 He said, "That which proceeds out of the man, that defiles the man.
Ya ce, abinda ke cikin mutum shike gurbatar da shi
21 For from within, out of a person's heart, proceed evil thoughts, adulteries, sexual sins, murders, thefts,
Domin daga cikin mutum, kuma daga cikin zuciyarsa ne, mugun tunani, lalata, sata, kisa,
22 covetings, wickedness, deceit, lustful desires, an evil eye, blasphemy, pride, and foolishness.
zina, kwadayi, mugunta, hai'inci, mugun guri, kishi, zargi, girmankai, wawanci.
23 All these evil things come from within, and defile the man."
Duk wadannan miyagun abubuwa suna fitowa ne daga cikin mutum, kuma suke gurbatar da shi.”
24 From there he arose, and went away into the region of Tyre and Sidon. He entered into a house, and did not want anyone to know it, but he could not escape notice.
Ya tashi daga nan ya tafi shiyyar Sur da Sida. Ya shiga wani gida don baya son wani ya sani cewa yana nan, amma bai iya boyuwa ba.
25 But immediately a woman whose young daughter had an unclean spirit heard of him and came and fell at his feet.
Amma nan da nan wata mace, wadda diyarta ke da mugun ruhu-wannan mace kuwa ta ji game da Yesu sai ta zo ta durkusa a gabansa.
26 Now the woman was a Greek, a Syrophoenician by race. She begged him that he would cast the demon out of her daughter.
Matar yar kasar Girka ce, kuma asalinta daga Fonishiya take. Ta roke shi da ya fitar da mugun ruhun nan daga diyarta.
27 But he said to her, "Let the children be filled first, for it is not appropriate to take the children's bread and throw it to the dogs."
Sai ya ce mata, “Bari a ciyar da 'ya'ya tukuna. Domin bai kamata a dauki abincin yaya a ba karnuka ba”.
28 But she answered him, "Yes, Sir. Yet even the dogs under the table eat the children's crumbs."
Sai ta amsa masa cewa, “I, Ubangiji, Karnukan ma sukan ci abincin da ke fadowa daga teburin 'ya'yan.”
29 He said to her, "For this saying, go your way. The demon has gone out of your daughter."
Ya ce mata, “domin kin fadi haka, kina iya ki tafi domin aljani ya fita daga diyarki.”
30 And when she went away to her house, she found the child lying on the bed, the demon having left.
Ta koma gida sai ta iske diyarta na kwance akan gado, aljanin ya fice daga jikinta.
31 Again he departed from the borders of Tyre, and came through Sidon to the sea of Galilee, through the midst of the region of Decapolis.
Ya sake fita daga shiyar Sur, ya biyo ta Sidon, har zuwa tekun Galili a shiyar Dikafolis.
32 They brought to him one who was deaf and had a speech difficulty, and they begged Jesus to lay his hand on him.
Sun kawo masa wani kurma, kuma bebe ne shi, suna rokansa ya dora hanuwansa a bisansa.
33 He took him aside from the crowd, privately, and put his fingers into his ears, and he spat, and touched his tongue.
Sai ya jawo shi daga taron jama'ar, zuwa gefe, sai ya sa hanunsa a kunuwan beben bayan ya tufa yawunsa, sannan ya taba harshensa.
34 Looking up to heaven, he sighed, and said to him, "Ephphatha." that is, "Be opened."
Ya dubi sama, ya ja numfashi ya ce masa, “Ifatha”, wato, “bude!”
35 And his ears were opened, and the impediment of his tongue was released, and he spoke clearly.
Nan da nan ya mayar masa da jinsa. abinda ya daure harshensa ya sake shi, sai ya fara magana da kyau.
36 He commanded them that they should tell no one, but the more he commanded them, so much the more widely they proclaimed it.
Ya umarce su da kada su gaya wa wani. Amma duk da umarnin da yake basu, suna ta shaida shi ko'ina.
37 They were astonished beyond measure, saying, "He has done all things well. He makes even the deaf hear, and the mute speak."
kuma suna ta mamaki cewa, “Yayi kowanne abu da kyau, har ya sa kurame suna jin magana, da kuma bebaye na magana.”

< Mark 7 >