< John 17 >
1 Jesus said these things, and lifting up his eyes to heaven, he said, "Father, the time has come. Glorify your Son, that your Son may also glorify you;
Da Yesu ya fadi wandannan abubuwa, sai ya tada idanunsa sama ya ce, ya Uba, sa'a ta zo; ka daukaka Danka, domin Dan shi ya daukaka ka,
2 even as you gave him authority over all flesh, he will give everlasting life to all whom you have given him. (aiōnios )
kamar yadda ka ba shi iko akan dukkan 'yan adam, ya ba da rai madawwami ga duk wanda ka ba shi. (aiōnios )
3 This is everlasting life, that they may know you, the only true God, and him whom you sent, Jesus Christ. (aiōnios )
Wannan ne rai madawwami: wato su san ka, Allah makadaici na gaskiya, da shi kuma wanda ka aiko, Yesu Almasihu. (aiōnios )
4 I glorified you on the earth by accomplishing the work which you have given me to do.
Na daukaka ka a duniya, na gama aikin da ka ba ni in yi.
5 Now, Father, glorify me with your own self with the glory which I had with you before the world existed.
Yanzu, ya Uba, ka daukaka ni tare da kai da daukaka wadda ni ke da ita tare da kai tun kafin duniya ta kasanci.
6 I revealed your name to the people whom you have given me out of the world. They were yours, and you have given them to me. They have kept your word.
Na bayyana sunanka ga mutunen da ka ba ni acikin duniya. Na ka suke, ka ba ni su, sun kuwa kiyaye maganarka.
7 Now they have known that all things whatever you have given me are from you,
Yanzu kuwa sun san duk iyakar abinda ka ba ni daga gare ka yake,
8 for the words which you have given me I have given to them, and they received them, and knew for sure that I came forth from you, and they have believed that you sent me.
don kuwa maganganun da ka fada mani. Na fada masu, sun kuma karba, sun sani kuwa hakika na fito daga gareka ne, kuma sun gaskata kai ne ka aiko ni.
9 I pray for them. I do not pray for the world, but for those whom you have given me, for they are yours.
Ina yi masu addu'a. Ba domin duniya ni ke yin addu'a ba, amma domin wadanda ka bani gama na ka ne.
10 All things that are mine are yours, and yours are mine, and I am glorified in them.
Gama dukan abinda ke nawa na ka ne, naka kuwa nawa ne, an kuma daukaka ni a cikinsu.
11 I am no more in the world, but they are in the world, and I am coming to you. Holy Father, keep them through your name which you have given me, that they may be one, even as we are.
Ba na cikin duniya kuma, amma wadannan mutane suna cikin duniya, ni kuwa ina zuwa wurin ka. Ya Uba mai Tsarki, ka adanasu cikin sunanka da ka ba ni domin su zama daya, kamar dai yadda muke daya.
12 While I was with them, I kept them in your name which you have given me, and I guarded them, and not one of them perished, except the son of destruction, that the Scripture might be fulfilled.
Lokacin da ina tare da su, na adanasu acikin sunanka da ka ba ni. Na kiyaye su, kuma ko daya kuwa daga cikinsu ba ya bace ba, sai dai dan hallakar nan, domin Nassi ya cika.
13 But now I come to you, and I say these things in the world, that they may have my joy made full in themselves.
Amma yanzu ina zuwa wurinka, Ina fadar wadannan abubuwa tun ina duniya, domin farin cikina ya zama cikakke a zukatansu.
14 I have given them your word. The world hated them, because they are not of the world, even as I am not of the world.
Na ba su maganarka, kuma duniya ta tsane su domin su ba na duniya ba ne, kamar yadda ni ba na duniya ba ne.
15 I pray not that you would take them from the world, but that you would keep them from the evil one.
Ba ina roko ka dauke su daga cikin duniya ba, amma domin ka tsare su daga mugun nan.
16 They are not of the world even as I am not of the world.
Su ba na duniya ba ne, kamar yadda ni ba na duniya ba ne.
17 Sanctify them in the truth. Your word is truth.
Ka kebe su domin kanka cikin gaskiya. maganarka gaskiya ce.
18 As you sent me into the world, even so I have sent them into the world.
Kamar dai yadda ka aiko ni cikin duniya, haka kuma na aike su cikin duniya.
19 For their sakes I sanctify myself, that they themselves also may be sanctified in truth.
Na kebe kaina gareka sabili da su, domin su ma kansu a kebe su gareka cikin gaskiya.
20 Not for these only do I pray, but for those also who believe in me through their word,
Ina addu'a ba domin wadannan kadai ba, amma har da wadanda zasu gaskata da ni ta wurin maganarsu,
21 that they may all be one; even as you, Father, are in me, and I in you, that they also may be in us; that the world may believe that you sent me.
Domin su zama daya dukansu, kamar yadda kai, ya Uba, ka ke ciki na, ni kuma na ke cikin ka. Ina roko suma su kasance a cikinmu, domin duniya ta gaskata cewa ka aiko ni
22 The glory which you have given me, I have given to them; that they may be one, even as we are one;
Daukakar da ka bani, ita nake basu, domin su zama daya, kamar yadda mu ke daya;
23 I in them, and you in me, that they may be perfected into one; that the world may know that you sent me, and loved them, even as you loved me.
ni a cikinsu, kai kuma a ciki na. Domin su kammalu cikin zama daya, domin duniya ta sani cewa ka aiko ni, kuma ka kaunace su, kamar yadda ka kaunace ni.
24 Father, I desire that they also whom you have given me be with me where I am, that they may see my glory, which you have given me, for you loved me before the foundation of the world.
Ya Uba, ina so wadanda ka ba ni, su ma su kasance tare da ni inda nake, domin su dubi daukakata da ka yi mani. Domin ka kaunace ni tun kafin halittar duniya.
25 Righteous Father, the world hasn't known you, but I knew you; and these knew that you sent me.
Ya Uba mai adalci, duniya kam, ba ta sanka ba, amma ni na sanka; kuma wadannan sun sani kai ne ka aiko ni.
26 I made known to them your name, and will make it known; that the love with which you loved me may be in them, and I in them."
Na sanar masu da sunanka, zan kuma sanar da shi domin kaunar da ka yi mani ta kasance a cikinsu, ni kuma in kasance a cikinsu,