< Job 18 >
1 Then Bildad the Shuhite answered,
Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
2 "How long will you hunt for words? Consider, and afterwards we will speak.
“Yaushe za ka gama maganganun nan? Ka dawo da hankalinka sa’an nan za mu iya yin magana.
3 Why are we counted as animals, which have become unclean in your sight?
Don me muke kamar shanu a wurinka, ka ɗauke mu mutanen wofi?
4 You who tear yourself in your anger, shall the earth be forsaken for you? Or shall the rock be removed out of its place?
Kai da ka yayyage kanka don haushi, za a yashe duniya saboda kai ne? Ko kuma duwatsu za su matsa daga wurinsu?
5 "Yes, the light of the wicked shall be put out, The spark of his fire shall not shine.
“An kashe fitilar mugu; harshen wutarsa ya daina ci.
6 The light shall be dark in his tent. His lamp above him shall be put out.
Wutar cikin tentinsa ta zama duhu; fitilar da take kusa da shi ta mutu.
7 The steps of his strength shall be shortened. His own counsel shall cast him down.
Ƙarfin takawarsa ya ragu; dabararsa ta ja fāɗuwarsa.
8 For he is cast into a net by his own feet, and he wanders into its mesh.
Ƙafafunsa sun kai shi cikin raga, yana ta yawo a cikin ragar.
9 A snare will take him by the heel. A trap will catch him.
Tarko ya kama ɗiɗɗigensa; tarko ya riƙe shi kam.
10 A noose is hidden for him in the ground, a trap for him in the way.
An ɓoye masa igiya da za tă zarge shi a ƙasa; an sa masa tarko a kan hanyar da zai bi.
11 Terrors shall make him afraid on every side, and shall chase him at his heels.
Tsoro duk ya kewaye shi ta kowane gefe yana bin shi duk inda ya je.
12 His strength shall be famished. Calamity shall be ready at his side.
Masifa tana jiransa; bala’i yana shirye yă fāɗa masa a lokacin da zai fāɗi.
13 The members of his body shall be devoured. The firstborn of death shall devour his members.
Ya cinye wani sashe na gaɓar jikinsa; ɗan fari na mutuwa ya cinye ƙafafunsa.
14 He shall be rooted out of his tent where he trusts. He shall be brought to the king of terrors.
An yage shi daga zaman lafiyar da yake yi a cikin tentinsa aka sa shi tsoro sosai.
15 There shall dwell in his tent that which is none of his. Sulfur shall be scattered on his habitation.
Wuta ta cinye tentinsa; farar wuta ta rufe wurin da yake zama.
16 His roots shall be dried up beneath. Above shall his branch be cut off.
Jijiyoyinsa sun bushe a ƙasa rassansa sun mutu a sama.
17 His memory shall perish from the earth. He shall have no name in the street.
An manta da shi a duniya; ba wanda yake ƙara tunawa da shi.
18 He shall be driven from light into darkness, and chased out of the world.
An tura shi daga cikin haske zuwa cikin duhu, an kore shi daga duniya.
19 He shall have neither son nor grandson among his people, nor any remaining where he sojourned.
Ba shi da’ya’ya ko zuriya cikin mutanensa, ba sauran wanda yake a raye a wurin da ya taɓa zama.
20 Those who come after shall be astonished at his day, as those who went before were frightened.
Mutanen Yamma suna mamakin abin da ya faru da shi; tsoro ya kama mutanen gabas.
21 Surely such are the dwellings of the unrighteous. This is the place of him who doesn't know God."
Ba shakka haka wurin zaman mugun mutum yake, haka wurin zaman wanda bai san Allah ba yake.”