< Exodus 5 >

1 Afterward Moses and Aaron came, and said to Pharaoh, "This is what Jehovah, God of Israel, says, 'Let my people go, that they may hold a feast to me in the wilderness.'"
Daga bisani sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna suka ce, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Bari mutanena su tafi domin su yi mini biki a hamada.’”
2 Pharaoh said, "Who is Jehovah, that I should listen to his voice to let Israel go? I do not know Jehovah, and moreover I will not let Israel go."
Fir’auna ya ce, “Wane ne Ubangiji da zan yi biyayya da shi, har in bar Isra’ila su tafi? Ban san Ubangiji ba, kuma ba zan bar Isra’ila su tafi ba.”
3 They said, "The God of the Hebrews has met with us. Please let us go three days' journey into the wilderness, and sacrifice to our God, lest he fall on us with pestilence, or with the sword."
Sai suka ce, “Allah na Ibraniyawa ya sadu da mu. Yanzu bari mu ɗauki tafiyar kwana uku cikin hamada domin mu miƙa hadaya ga Ubangiji Allahnmu, don kada yă buga mu da annoba ko takobi.”
4 The king of Egypt said to them, "Why do you, Moses and Aaron, take the people from their work? Get back to your burdens."
Amma sarkin Masar ya ce wa, “Musa da Haruna, don me kuke hana mutane yin aikinsu? Ku koma wurin aikinku!”
5 Pharaoh said, "Look, the people of the land are now many, and you make them rest from their burdens."
Sa’an nan Fir’auna ya ce, “Ga shi mutane sun yi yawa a ƙasar Masar, ku kuma yanzu kuna so ku hana su yin aiki.”
6 The same day Pharaoh commanded the taskmasters of the people, and their officers, saying,
A wannan rana Fir’auna ya ba da wannan umarni wa shugabannin masu gandu,
7 "You shall no longer give the people straw to make brick, as before. Let them go and gather straw for themselves.
“Kada ku ƙara ba wa mutanen ciyawar tattaka domin su yi tubula, bari su tafi su tattara tattaka da kansu.
8 The number of the bricks, which they made before, you require from them. You shall not diminish anything of it, for they are idle; therefore they cry, saying, 'Let us go and sacrifice to our God.'
Ku kuma bukace su su yi tubula daidai yawan tubalin da suka saba yi, kada ku rage. Ragwaye ne, shi ya sa suke kuka cewa, ‘Bari mu tafi mu yi hadaya ga Allahnmu.’
9 Let heavier work be laid on the men, so they may labor at it and pay no attention to lying words."
Ku sa waɗannan mutane su yi aiki mai tsanani sosai, don kada su sami zarafin kasa kunne ga maganganun ƙarya.”
10 The taskmasters of the people went out, and their officers, and they spoke to the people, saying, This is what Pharaoh says: "I will not give you straw.
Sai shugabannin masu aikin gandu suka fita suka gaya wa mutanen Isra’ila, “Ga abin da Fir’auna ya ce, ‘Ba zan ƙara ba ku tattaka ba.
11 Go yourselves, get straw where you can find it, for nothing of your work shall be diminished."
Ku tafi ku nemo wa kanku tattaka duk inda za ku samu, amma ba za a rage aikinku ba ko kaɗan.’”
12 So the people were scattered abroad throughout all the land of Egypt to gather dry stalks for straw.
Saboda haka mutane suka warwatsu ko’ina a Masar domin tattara bunnun da za su yi amfani da su, maimakon tattaka.
13 The taskmasters kept pressing them, saying, "Fulfill your work quota, your daily amount, as when there was straw."
Shugabannin gandu suka dinga matsa musu suna cewa, “Ku cika aikin da aka bukace ku na kowace rana kamar yadda kuke yi sa’ad da kuke da tattaka.”
14 The officers of the children of Israel, whom Pharaoh's taskmasters had set over them, were beaten, and demanded, "Why haven't you fulfilled your quota both yesterday and today, in making brick as before?"
Manyan Isra’ilawa waɗanda shugabannin gandun Fir’auna suka naɗa, suka sha dūka, aka kuma yi musu tambayoyi ana cewa, “Don me ba ku cika yawan tubula na jiya da na yau kamar yadda kuka saba ba?”
15 Then the officers of the children of Israel came and cried to Pharaoh, saying, "Why do you deal this way with your servants?
Sai manyan Isra’ila masu bi da aikin gandu suka tafi wurin Fir’auna suka yi roƙo suna cewa, “Don me kake yi wa bayinka haka?
16 No straw is given to your servants, and they tell us, 'Make bricks.' And look, your servants are beaten, but the fault is with your own people."
Ba a ba wa bayinka tattaka, duk da haka ana ce mana, ‘Ku yi tubula!’ Ana wa bayinka dūka, amma fa laifin na mutanenka ne.”
17 But he said, "You are slackers! Slackers! Therefore you say, 'Let us go and sacrifice to God.'
Fir’auna ya ce, “Ku ragwaye ne! Shi ya sa kuke cewa, ‘Bari mu tafi mu yi hadaya wa Ubangiji.’
18 Go therefore now, and work, for no straw shall be given to you, yet you shall deliver the same number of bricks."
Ku ɓace yanzu daga nan, ku koma wurin aikinku. Ba za a ba ku tattaka ba, kuma dole ku fid da tubula kamar yadda kuka saba.”
19 The officers of the children of Israel saw that they were in trouble, when it was said, "You shall not diminish anything from your daily quota of bricks."
Manyan Isra’ilawa da suke bi da aikin gandu suka gane cewa sun shiga uku, sa’ad da aka gaya musu, “Ba za ku rage yawan tubulan da aka bukace ku ku yi na kowace rana ba.”
20 They met Moses and Aaron, who stood in the way, as they came forth from Pharaoh:
Da suka bar Fir’auna, sai suka sadu da Musa da Haruna suna jira su sadu da su,
21 and they said to them, "May God look at you, and judge, because you have made us a stench to be abhorred in the eyes of Pharaoh, and in the eyes of his servants, to put a sword in their hand to kill us."
sai suka ce, “Bari Ubangiji yă duba, yă kuma hukunta ku! Kun maishe mu abin ƙyama ga Fir’auna da bayinsa, kuka kuma sa musu takobi a hannunsu don su kashe mu.”
22 Moses returned to Jehovah, and said, "Lord, why have you brought trouble on this people? Why is it that you have sent me?
Musa ya koma wurin Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji, don me ka kawo wahala a kan mutanen nan? Abin da ya sa ka aiko ni ke nan?
23 For since I came to Pharaoh to speak in your name, he has brought trouble on this people; neither have you delivered your people at all."
Gama tun da na tafi wurin Fir’auna, na yi masa magana da sunanka, sai ya fara gasa wa mutanen nan azaba, ba ka kuma ceci mutanenka.”

< Exodus 5 >