< Acts 4 >

1 As they spoke to the people, the priests and the captain of the temple and the Sadducees came to them,
Yayin da Bitrus da Yahaya suna kan magana da mutanen, sai firistoci da shugaban masu tsaron Haikali da kuma Sadukiyawa suka afko masu.
2 being upset because they taught the people and proclaimed in Jesus the resurrection from the dead.
Sun damu sosai domin Bitrus da Yahaya suna koyar da mutane game da Yesu kuma suna shelar tashinsa daga matattu.
3 They laid hands on them, and put them in custody until the next day, for it was now evening.
Suka kama su suka jefa kurkuku sai washegari, domin yamma ta riga ta yi.
4 But many of those who heard the word believed, and the number of the men came to be about five thousand.
Amma mutane da yawa da suka ji sakon suka ba da gaskiya; kimanin mazaje dubu biyar ne kuwa suka ba da gaskiya.
5 It happened in the morning, that their rulers, elders, and scribes were gathered together in Jerusalem.
Washegari, da shugabaninsu, da dattawansu, da Marubuta suka taru a Urushalima.
6 Annas the high priest was there, with Caiaphas, John, Alexander, and as many as were relatives of the high priest.
Anas babban firist, yana nan, da Kayafa, da Yahaya da Iskandari, da dukan dangin babban firist
7 When they had stood them in the middle of them, they inquired, "By what power, or in what name, have you done this?"
Da suka kawo Bitrus da Yahaya a tsakiyarsu sai suka tambaye su, “Da wanne iko, ko cikin wanne suna k ka yi haka?”
8 Then Peter, filled with the Holy Spirit, said to them, "Rulers of the people, and elders,
Sai Bitrus, cike da Ruhu Mai Tsarki, ya ce, “Ku shugabanni da dattawan jama'a,
9 if we are examined today concerning a good deed done to a crippled man, by what means this man has been healed,
idan mu yau ana tuhumarmu saboda aikin kirki da aka yi ga wannan mara lafiya - ta yaya wannan mutum ya sami lafiya?
10 be it known to you all, and to all the children of Israel, that in the name of Jesus Christ the Nazorean, whom you crucified, whom God raised from the dead, in him does this man stand here before you whole.
Bari ku da dukan mutanen Isra'ila, ku san wannan, cikin sunan Yesu Almasihu Banazare, wanda kuka giciye, wanda Allah ya tayar daga matattu ta dalilinsa ne wannan mutumin yake tsaye a gaban ku lafiyayye.
11 This one is the stone which was regarded as worthless by you, the builders, which has become the head of the corner.
Yesu Almasihu ne dutsen da ku magina kuka ki, amma an mai da shi kan gini.
12 And there is salvation in no one else, for there is no other name under heaven that is given among people by which we must be saved."
Babu ceto daga kowanne mutum, domin babu wani suna da aka bayar karkashin sama, a cikin mutane wanda ta wurinsa za a iya samu ceto.''
13 Now when they saw the boldness of Peter and John, and had perceived that they were unlearned and ignorant men, they were amazed. They recognized that they had been with Jesus.
Sa'adda, suka ga karfin halin Bitrus da Yahaya, suka gane mutane ne talakawa marasa ilimi, sai suka yi mamaki, suka kuma lura suka gane Bitrus da Yahaya sun kasance tare da Yesu.
14 Seeing the man who was healed standing with them, they could say nothing against it.
Da yake suna ganin mutumin nan da aka warkar tare da su, sai suka rasa abin yi.
15 But when they had commanded them to go aside out of the council, they conferred among themselves,
Amma bayan sun fitar da manzannin daga majalisa sai suka tattauna a tsakaninsu.
16 saying, "What should we do with these men? Because indeed a notable miracle has been done through them, as can be plainly seen by all who dwell in Jerusalem, and we cannot deny it.
Suka ce, “Yaya za mu yi da wadannan mutane? Babu shakka aikin al'ajibi ya faru ta wurinsu, kuma sananne ne ga dukan mazauna Urushalima, kuma ba mu da iko mu musanci haka.
17 But so this does not spread any further among the people, let us severely threaten them, that from now on they do not speak to anyone in this name."
Amma saboda kada ya cigaba da yaduwa cikin mutane, bari mu yi masu kashedi kada su kara magana da kowa cikin wannan suna.''
18 They called them, and commanded them not to speak at all nor teach in the name of Jesus.
Suka kira Bitrus da Yahaya suka dokace su kada su kara magana ko kuma koyarwa ko kadan a cikin sunan Yesu.
19 But Peter and John answered them, "Whether it is right in the sight of God to listen to you rather than to God, judge for yourselves,
Amma Bitrus da Yahaya suka amsa suka ce, ''Ko ya yi daidai a gaban Allah mu yi maku biyayya fiye da shi, ku hukunta.
20 for we cannot help telling the things which we saw and heard."
Baza mu iya daina magana game da abubuwan da muka ji kuma muka gani ba.''
21 When they had further threatened them, they let them go, finding no way to punish them, because of the people; for everyone glorified God for that which was done.
Bayan sun sake yi wa Bitrus da yahaya kashedi, sai suka sake su, su tafi. Domin ba su iya samu wata hujja da za su hore su a kai ba, domin dukan mutane suna yabon Allah saboda abin da ya faru.
22 For the man on whom this miracle of healing was performed was more than forty years old.
Mutumin da ya sami wannan al'ajibi na warkarwa yana sama da shekara arba'in.
23 Being let go, they came to their own company, and reported all that the chief priests and the elders had said to them.
Bayan an sake su, Bitrus da Yahaya suka zo cikin mutanensu suka ba da rahoton duk abin da manyan firistoci da dattawa suka fada masu.
24 When they heard it, they lifted up their voice to God with one accord, and said, "Lord, you made the heaven and the earth and the sea, and all that is in them.
Da suka ji haka, suka daga muryarsu tare ga Allah suka ce, ''Ubangiji, kai da ka yi sama da duniya da teku da duk abin da ke cikinsu,
25 You said through the Holy Spirit, through the mouth of our father David your servant: 'Why do the nations rage, and the peoples plot in vain?
kai wanda ta wurin Ruhu Mai Tsarki ta bakin ubanmu Dauda bawanka, ya ce, 'Me ya sa al'ummai suka tunzura, kuma mutane suke tunanin abubuwan banza?
26 The kings of the earth take a stand, and the rulers take council together, against the Lord, and against his Christ.'
Sarakunan duniya sun hada kansu tare, kuma shugabanninsu sun taru don su yi gaba da Ubangiji, da kuma Almasihunsa.'
27 "For truly, in this city against your holy servant, Jesus, whom you anointed, both Herod and Pontius Pilate, with the non-Jews and the people of Israel, were gathered together
Hakika, Hiridus da Buntus Bilatus, tare da al'ummai da mutanen Isra'ila, sun taru a wannan birni domin su yi jayayya da bawanka mai tsarki Yesu, shafaffe.
28 to do whatever your hand and your council foreordained to happen.
Sun taru domin su aiwatar da dukan abin da hannunka da nufinka ya shirya zai faru.
29 Now, Lord, look at their threats, and grant to your servants to speak your word with all boldness,
Yanzu, Ya Ubangiji ka dubi kashedin su, ka ba bayin ka ikon furta maganar ka gabagadi.
30 while you stretch out your hand to heal; and that signs and wonders may be done through the name of your holy Servant Jesus."
Sa'adda ka mika hannunka domin warkarwa, alamu da al'ajibai su faru ta wurin sunan bawanka mai tsarki Yesu.”
31 When they had prayed, the place was shaken where they were gathered together. They were all filled with the Holy Spirit, and they spoke the word of God with boldness.
Bayan sun gama addu'a, wurin da suka taru ya girgiza, suka cika da Ruhu Mai Tsarki, suka furta maganar Allah gabagadi.
32 And the full number of those who believed were of one heart and soul. Not one of them claimed that anything of the things which he possessed was his own, but they had all things in common.
Babban taron da suka ba da gaskiya kansu hade yake; kuma ba wanda ya ce da abinda ya mallaka nasa ne; maimakon haka, komai na su daya ne.
33 With great power, the apostles gave their testimony of the resurrection of the Lord Jesus. Great grace was on them all.
Da iko mai karfi manzannin suka yi shelar shaidarsu game da tashin Yesu Ubangiji daga matattu, babban alheri kuma na bisansu.
34 For neither was there among them any who lacked, for as many as were owners of lands or houses sold them, and brought the proceeds of the things that were sold,
Babu wani a cikinsu wanda ya rasa komai, domin masu filaye da gidaje suka sayar suka kawo kudin abin da suka sayar
35 and put them at the apostles' feet, and distribution was made to each, according as anyone had need.
sai suka kawo kudin gaban manzanni. Aka rarraba wa kowanne mutum bisa ga bukatarsa.
36 Joseph, who by the apostles was surnamed Barnabas (which is translated, Son of Encouragement), a Levite, a native of Cyprus by birth,
Yusufu, Balawi, mutumin tsibirin Kubrus, wanda manzannisu ka yi wa lakani da suna Barnaba. (wato, mai karfafa zuciya).
37 having a field, sold it, and brought the money and put it at the apostles' feet.
Yana da fili sai ya sayar da shi ya kawo kudin gaban manzanni.

< Acts 4 >