< 2 Samuel 17 >

1 Moreover Ahithophel said to Absalom, "Let me now choose twelve thousand men, and I will arise and pursue after David tonight.
Ahitofel ya ce wa Absalom, “Zan zaɓi mutum dubu goma sha biyu su fita a daren nan in fafari Dawuda.
2 And I will catch up with him while he is weary and discouraged, and will thow him into a panic, and all the people who are with him will flee. And I will strike the king alone.
Zan fāɗa masa sa’ad da yake cikin gajiya da karayar zuciya. Zan firgita shi, mutanen da suke tare da shi kuwa za su gudu. Sarki ne kaɗai zan kashe
3 Then all the people will come back to you, as a bride returns to her husband. You seek the life of only one man; then all the people will be in peace."
in dawo da dukan mutanen a gare ka. Mutuwar wanda kake nema zai zama dawowar duka; dukan mutanen ba za su cutu ba.”
4 And the advice seemed good to Absalom and all the elders of Israel.
Wannan shawara ta gamshi Absalom da dukan dattawan Isra’ila.
5 Then Absalom said, "Now call Hushai the Archite, and let's hear what he says."
Amma Absalom ya ce, “A kira mini Hushai mutumin Arkitawan nan shi ma, mu ji abin da zai ce.”
6 When Hushai came to Absalom, Absalom said to him, "Ahithophel has spoken thus. Should we follow his advice? And if not, speak up."
Da Hushai ya zo wurinsa, sai Absalom ya ce, “Ahitofel ya ba da wannan shawara. Mu yi abin da ya ce? In ba haka ba, sai ka ba mu ra’ayinka.”
7 So Hushai said to Absalom, "The counsel that Ahithophel has given this time is not good."
Hushai ya ce wa Absalom, “Shawarar da Ahitofel ya bayar a wannan lokaci kam, ba ta da kyau.
8 Moreover, Hushai said, "You know your father and his men, that they are warriors, and that they are as fierce as a bear robbed of her cubs in the wild, or a sow snared in the wild. Your father is expert in war, and will not camp with the people.
Ka san mahaifinka da mutanensa mayaƙa ne, suna cikin fushi kamar mugun beyar da aka ƙwace mata’ya’ya. Ban da haka ma, mahaifinka gogagge ne a yaƙi; ba zai kwana da rundunar ba.
9 Look, he is now hidden in some pit, or in some other place. And it will happen when some of them have fallen first, that whoever hears it will say, 'There is a slaughter among the people who follow Absalom.'
Kai, ko yanzu ma, ya riga ya ɓuya cikin kogo ko kuma a wani wuri. In har ya fara kai wa rundunarka hari duk wanda ya ji, zai ce, ‘An yi kaca-kaca da rundunar da suka bi Absalom.’
10 Then even the one who is brave, whose heart is like the heart of a lion, will utterly melt; for all Israel knows that your father is a warrior, and those who are with him are brave men.
Kai, ko jarumi mai zuciya kamar na zaki ma, zai narke don tsoro, gama dukan Isra’ila sun sani mahaifinka mayaƙi ne, sun kuma san cewa waɗanda suke tare da shi jarumawa ne.
11 But, I strongly advise as follows: Let all Israel be gathered to you from Dan to Beersheba, as the sand that is by the sea in number, and that you personally go into battle.
“Saboda haka ina ba ka shawara, bari a tara maka dukan Isra’ila, daga Dan zuwa Beyersheba da yawansu ya yi kamar yashin bakin teku, kai kanka ka jagorance su zuwa fagen fama.
12 So we will come upon him in some place where he can be found, and we will fall on him as the dew falls on the ground, and of him and all the men with him not one will be left.
Sa’an nan za mu fāɗa masa duk inda yake, za mu fāɗa masa kamar yadda raɓa takan fāɗo a bisa ƙasa. Da shi da mutanensa babu ko ɗaya da za a bari da rai.
13 Moreover, if he withdraws into a city, then all Israel will take up ropes to that city, and we will drag it into the riverbed, until there isn't one pebble to be found there."
In ma ya janye zuwa cikin birni, sai dukan Isra’ila su kawo igiyoyi wa wannan birni, su ja shi zuwa kwari yă wargaje, yadda ba za a bar wani dutse a kan wani ba.”
14 Then Absalom and all Israel said, "The counsel of Hushai the Archite is better than the counsel of Ahithophel." For Jehovah had commanded that Ahithophel's counsel should be defeated, so that that Jehovah could bring Absalom to ruin.
Absalom da dukan mutanen Isra’ila suka ce, “Shawarar Hushai mutumin Arkitawa ta fi ta Ahitofel kyau.” Gama Ubangiji ya ƙudura yă wofinta kyakkyawar shawarar Ahitofel, don yă jawo wa Absalom masifa.
15 Then Hushai said to Zadok and to Abiathar the priests, "Here is the council Ahithophel gave Absalom and the elders of Israel, and here is what I counseled.
Hushai ya ce wa Zadok da Abiyatar, firistoci, “Ahitofel ya ba wa Absalom da dattawan Isra’ila shawara su yi kaza da kaza, amma na ba su shawara su yi haka, su yi haka.
16 Now therefore send quickly and tell David, saying, 'Do not stay the night at the fords of the wilderness, but by all means pass over. Otherwise the king and all the people who are with him will be swallowed up.'"
Yanzu sai ku aika wa Dawuda saƙo nan da nan ku ce masa, ‘Kada ka kwana a mashigai cikin hamada; ka tabbata ka haye ba faci, in ba haka ba sarki da dukan mutanensa za su hallaka.’”
17 Now Jonathan and Ahimaaz were staying at En Rogel, and a female servant was to go and tell them, and they would go and inform king David. For they were not to be seen going into the city.
Yonatan da Ahimawaz suna zaune a En Rogel. Wata baranya ce za tă je ta faɗa musu, su kuma su tafi su gaya wa Sarki Dawuda don suna tsoro kada a ga suna shiga birnin.
18 But a young man saw them and told Absalom. So they both departed quickly and reached the house of a man in Bahurim who had a well in his courtyard, and they went down into it.
Amma wani saurayi ya gan su, ya gaya wa Absalom. Sai dukansu biyu suka tashi da sauri suka shiga gidan wani mutum a Bahurim. Yana da rijiya a cikin gida, sai suka shiga cikinta.
19 And the woman took a covering and spread it over the top of the well and scattered some grain on it, so that nothing could be noticed.
Matarsa mutumin kuwa ta kawo tabarma ta shimfiɗa a bakin rijiyar, sai ta kawo hatsi ta baza a kanta. Ba kuwa wanda ya san abin da ta yi.
20 Then Absalom's servants came to the woman at the house, and they asked, "Where are Ahimaaz and Jonathan?" And the woman said to them, "They have crossed the brook of water." And when they had searched and could not find them, they returned to Jerusalem.
Da mutanen Absalom suka zo wurin matan a gidan, suka ce, “Ina Yonatan da Ahimawaz?” Matar ta ce, “Tuni, sun haye rafi.” Sai mutanen suka yi ta nemansu amma ba su ga kowa, sai suka koma Urushalima.
21 It came about after they had left that they climbed out of the well, and left and told king David. And they said to him, "Get up and cross quickly over the water, for Ahithophel has given such and such counsel against you."
Bayan mutanen suka tafi, sai su biyun suka fito daga rijiyar suka je suka gaya wa Sarki Dawuda. Suka ce masa, “Maza ka ƙetare kogi; Ahitofel ya ba wa Absalom shawara a yi maka kaza da kaza.”
22 Then David and all the people who were with him got up and they crossed the Jordan. By dawn there was no one left who had not crossed the Jordan.
Saboda haka Dawuda da dukan mutanen da suke tare da shi suka tashi suka ƙetare Urdun. Kafin wayewar gari, babu wanda ya rage da bai haye ba.
23 Now when Ahithophel saw that his counsel was not followed, he saddled his donkey and went up to his home in his city. Then he set his house in order and hanged himself, and he died and was buried in the tomb of his father.
Da Ahitofel ya ga ba a bi shawararsa ba, sai ya hau jakinsa ya koma gidansa a garinsu. Ya kintsa gidansa sa’an nan ya rataye kansa. Ta haka ya mutu, aka kuma binne shi a kabarin mahaifinsa.
24 Then David came to Mahanaim. And Absalom crossed the Jordan, he and all Israel with him.
Dawuda kuwa ya tafi Mahanayim. Absalom kuma ya ƙetare Urdun tare da dukan mutanen Isra’ila.
25 And Absalom had put Amasa over the army in place of of Joab. Now Amasa was the son of a man whose name was Jether the Ishmaelite, who had married Abigail the daughter of Jesse, sister to Zeruiah, Joab's mother.
Absalom ya riga ya naɗa Amasa a kan sojoji a maimakon Yowab. Amasa kuwa ɗan wani mutum mai suna Itra ne, mutumin Ishmayel wanda ya auri Abigiyel,’yar Nahash,’yar’uwar Zeruhiya mahaifiyar Yowab.
26 So Israel and Absalom camped in the land of Gilead.
Isra’ilawa da Absalom suka kafa sansani a ƙasar Gileyad.
27 Now it happened when David came to Mahanaim, Shobi the son of Nahash from Rabbah of the people of Ammon, Makir the son of Ammiel of Lo Debar, and Barzillai the Gileadite of Rogelim,
Sa’ad da Dawuda ya zo Mahanayim, sai Shobi ɗan Nahash daga Rabba ta Ammonawa, da Makir ɗan Ammiyel daga Lo Debar, da Barzillai mutumin Gileyad daga Rogelim
28 brought couches for sleeping, and covers, and basins, and pottery utensils, and wheat, and barley, and meal, and parched grain, and beans, and lentils,
suka kawo wa Dawuda da mutanensa tabarmai, da kwanoni, da kayayyakin da aka yi da yumɓu. Suka kuma kawo alkama da sha’ir, da gari, da soyayyen hatsi, da wake, da waken barewa,
29 and honey, and curd of the flock, and cheese of the herd. And they presented them to David and to the people who were with him to eat. For they said, "The people are hungry and tired and thirsty in the wilderness."
da zuma, da kindirmo, da tumaki, da cukun madarar shanu wa Dawuda da mutanensa su ci. Gama sun ce, “Mutanen suna jin yunwa, sun kuma gaji, ga ƙishirwa a hamada.”

< 2 Samuel 17 >