< 1 Thessalonians 5 >
1 But concerning the times and the seasons, brothers, you have no need that anything be written to you.
Yanzu fa game da zancen lokatai da zamanai 'yan'uwa, ba ku da bukatar a rubuta maku wani abu.
2 For you yourselves know well that the day of the Lord comes like a thief in the night.
Domin ku da kanku kun sani kwarai cewa ranar zuwan Ubangiji kamar barawo take da dare.
3 Now when they are saying, "Peace and safety," then sudden destruction will come on them, like birth pains on a pregnant woman; and they will in no way escape.
Da suna zancen “zaman lafiya da kwanciyar rai,” sai hallaka ta zo masu ba zato ba tsammani. Zai zama kamar nakudar haihuwa ce da ke kama mace mai ciki. Ba su kwa da wata hanyar kubuta.
4 But you, brothers, are not in darkness, that the day should overtake you like a thief.
Amma ku, 'yan'uwa, ai ba cikin duhu kuke ba har da wannan rana zata mamaye ku kamar barawo.
5 You are all sons of light, and sons of the day. We do not belong to the night, nor to darkness,
Domin dukkan ku 'ya'yan haske ne 'ya'yan rana kuwa. Mu ba 'ya'yan dare ba ne ko na duhu,
6 so then let us not sleep, as the rest do, but let us watch and be sober.
Don haka, kada muyi barci kamar yadda sauran ke yi. Maimakon haka, bari mu kasance muna zaman tsaro kuma muna a fadake.
7 For those who sleep, sleep in the night, and those who are drunk are drunk in the night.
Don masu yin barci da dare suke yin barci, haka kuma masu sha su bugu ma da dare suke yi.
8 But let us, since we belong to the day, be sober, putting on the breastplate of faith and love, and, for a helmet, the hope of salvation.
Tunda shike mu 'ya'yan rana ne, bari mu zauna a natse. Bari musa sulke na bangaskiya da kauna, mu kuma sa kwalkwali don ceton mu dake gaba.
9 For God did not appoint us to wrath, but to the obtaining of salvation through our Lord Jesus Christ,
Domin Allah bai kaddara mu ga fushinsa ba, sai dai ga samun ceto ta wurin Ubangijin mu Yesu Almasihu.
10 who died for us, that, whether we wake or sleep, we should live together with him.
Shi ne wanda ya mutu domin mu, don ko da muna raye ko muna mace, mu iya rayuwa tare da shi,
11 Therefore exhort one another, and build each other up, even as you also do.
Domin haka ku ta'azantar da juna ku kuma inganta juna, kamar yadda kuke yi.
12 But we ask you, brothers, to recognize those who labor among you, and are over you in the Lord, and admonish you,
Muna rokon ku, 'yan'uwa, ku bada daraja ga wadanda suke aiki a tsakaninku wadanda kuma suke shugabanci a kan ku cikin Ubangiji, wadanda kuma suke horonku.
13 and to respect and honor them in love for their work's sake. Be at peace among yourselves.
Muna kuma rokon ku, da ku kula dasu ku kuma kaunacesu sabili da irin ayyukansu. Ku kuma yi zaman lafiya da junan ku.
14 We exhort you, brothers, admonish the disorderly, encourage the fainthearted, support the weak, be patient toward all.
Muna yi maku gargadi 'yan'uwa; ku jawa marassa ji kunne, ku karfafa marassa karfin zuciya, ku taimaki gajiyayyu, kuyi zaman hakuri da kowa.
15 See that no one returns evil for evil to anyone, but always seek what is good both for each other and for all.
Ku lura kada wani ya rama mugunta da mugunta, Maimakon haka ma, Ku cigaba da abinda ke mai kyau ga juna da kowa duka.
Kuyi farin ciki koyaushe.
18 In everything give thanks, for this is the will of God in Christ Jesus toward you.
A cikin kome kuyi godiya. Domin wannan ne nufin Allah a cikin Yesu Almasihu game daku.
19 Do not quench the Spirit.
Kada ku hana Ruhun Allah aiki a cikin ku.
20 Do not treat prophecies with contempt,
Kada ku raina anabce anabce.
21 but test all things; hold firmly that which is good.
Ku gwada komai. Ku rike abinda ke mai kyau.
22 Abstain from every form of evil.
Ku kaucewa duk wani abinda yayi kama da mugunta.
23 May the God of peace himself sanctify you completely. May your whole spirit, soul, and body be preserved blameless at the coming of our Lord Jesus Christ.
Bari Allah na salama ya mai da ku cikakun tsarkaka. Bari dukkan ruhun ku, da zuciyar ku, da jikin ku su zama adanannu marassa zargi domin zuwan Ubangijin mu Yesu Almasihu.
24 He who calls you is faithful, who will also do it.
Wanda ya kira ku mai aminci ne, wanda kuma zai aikata.
25 Brothers, pray for us also.
Yan'uwa, kuyi addu'a domin mu.
26 Greet all the brothers with a holy kiss.
Ku gaida dukkan yan'uwa da tsattsarkar sumba.
27 I solemnly command you by the Lord that this letter be read to all the holy brothers.
Ina rokon ku saboda Ubangiji ku karanta wasikar nan ga dukkan 'yan'uwa.
28 The grace of our Lord Jesus Christ be with you.
Bari alherin Ubangijin mu Yesu Almasihu shi kasance tareda ku.