< 1 Corinthians 1 >
1 Paul, called to be an apostle of Christ Jesus by the will of God, and our brother Sosthenes,
Bulus, wanda aka kira domin yă zama manzon Kiristi Yesu, bisa ga nufin Allah, da kuma ɗan’uwanmu Sostenes,
2 to the church of God which is at Corinth, to those who are sanctified in Christ Jesus, called to be saints, with all who call on the name of our Lord Jesus Christ in every place, both theirs and ours:
Zuwa ga ikkilisiyar Allah da take a Korint, da waɗanda aka tsarkake cikin Kiristi Yesu, aka kuma kira domin su zama masu tsarki, tare da dukan waɗanda suke ko’ina da suke kiran sunan Ubangijinmu Yesu Kiristi, Ubangijinsu da kuma namu.
3 Grace to you and peace from God our Father and the Lord Jesus Christ.
Alheri da salama daga Allah Ubanmu, da Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
4 I always thank my God concerning you, for the grace of God which was given you in Christ Jesus;
Ina gode wa Allah kullum dominku, saboda alherinsa da aka ba ku a cikin Kiristi Yesu.
5 that in everything you were enriched in him, in all speech and all knowledge;
Gama a cikinsa kuka sami wadata ta kowace hanya, a cikin dukan maganarku, da kuma cikin dukan saninku
6 even as the testimony of Christ was confirmed in you:
gama shaidarmu game da Kiristi ta tabbata a cikinku.
7 so that you are not lacking in any gift, as you wait for our Lord Jesus Christ to be revealed;
Saboda haka, ba ku rasa kowace baiwa ta ruhaniya ba, yayinda kuke jira da marmari, saboda bayyanuwar Ubangijinmu Yesu Kiristi.
8 who will also strengthen you to the end, blameless in the day of our Lord Jesus Christ.
Zai ƙarfafa ku har zuwa ƙarshe, domin ku zama marasa aibi a ranar Ubangijinmu Yesu Kiristi.
9 God is faithful, through whom you were called into the fellowship of his Son, Jesus Christ, our Lord.
Allah, wanda ya kira ku zuwa ga zumunci tare da Ɗansa Yesu Kiristi Ubangijinmu, shi mai aminci ne.
10 Now I appeal to you, brothers, in the name of our Lord Jesus Christ, that all of you be in agreement, so that there may be no divisions among you, and to be united by the same mind and conviction.
Ina roƙonku’yan’uwa, a cikin sunan Ubangijinmu Yesu Kiristi, dukanku ku yarda da juna, domin kada a sami tsattsaguwa a cikinku, domin kuma ku zama ɗaya, cikakku a cikin halinku da tunaninku.
11 For it has been reported to me concerning you, my brothers, by those who are from Chloe's household, that there are contentions among you.
’Yan’uwana, waɗansu daga iyalin gidan Kulos sun gaya mini cewa, akwai faɗa a cikinku.
12 Now I mean this, that each one of you says, "I follow Paul," "I follow Apollos," "I follow Cephas," and, "I follow Christ."
Abin da nake nufi shi ne, ɗaya daga cikinku na cewa, “Ni ina bin Bulus,” wani na cewa, “Ni ina bin Afollos,” wani kuma, “Ni ina bin Kefas,” har wa yau wani kuma, “Ni ina bin Kiristi.”
13 Is Christ divided? Was Paul crucified for you? Or were you baptized into the name of Paul?
Kiristi a rabe ne? Bulus ne aka gicciye dominku? An yi muku baftisma a cikin sunan Bulus ne?
14 I thank God that I baptized none of you, except Crispus and Gaius,
Ina godiya domin ban yi wa wani baftisma a cikinku ba, sai dai Kirisbus da Gayus kaɗai.
15 so that no one should say that you had been baptized into my own name.
Don haka, ba wanda na iya cewa an yi muku baftisma a cikin sunana.
16 (Now I also baptized the household of Stephanas; beyond that, I do not know whether I baptized any other.)
(I, na kuma yi wa iyalin gidan Istifanas baftisma, ban da wannan, ban tuna da wani da na yi masa baftisma ba.)
17 For Christ sent me not to baptize, but to preach the Good News—not in wisdom of words, so that the cross of the Christ would not be made void.
Gama Kiristi bai aike ni yin baftisma ba, sai dai wa’azin bishara ba da kalmomin hikimar mutum ba, domin kada gicciyen Kiristi ya rasa ikonsa.
18 For the message about the cross is foolishness to those who are perishing, but to us who are being saved it is the power of God.
Gama saƙon gicciye wauta ne ga waɗanda suke hallaka, amma a gare mu, mu da ake ceto, ikon Allah ne.
19 For it is written, "I will destroy the wisdom of the wise, and the discernment of the discerning I will nullify."
Gama a rubuce yake cewa, “Zan rushe hikimar mai hikima, basirar mai azanci kuma zan rikita shi.”
20 Where is the wise? Where is the scribe? Where is the debater of this age? Hasn't God made foolish the wisdom of this world? (aiōn )
Ina mai hikima? Ina mai zurfin bincike? Ina masana na wannan zamani? Ashe, Allah bai wofinta hikimar duniya ba? (aiōn )
21 For seeing that in the wisdom of God, the world through its wisdom did not know God, it was God's good pleasure through the foolishness of the preaching to save those who believe.
Gama tun da a cikin hikimar Allah, duniya a cikin hikimarta ba tă san shi ba, Allah ya ji daɗin ceton waɗanda suka ba da gaskiya ta wurin wautar wa’azin bishara.
22 For Jews ask for signs, and Greeks seek after wisdom,
Yahudawa suna so su ga alama, Hellenawa kuma suna neman hikima,
23 but we preach Christ crucified, a stumbling block to Jews and foolishness to the non-Jews,
amma mu, muna wa’azin Kiristi wanda aka gicciye ne, wanda ya zama dutsen tuntuɓe ga Yahudawa, wauta kuma ga Al’ummai,
24 but to those who are called, both Jews and Greeks, Christ is the power of God and the wisdom of God.
amma ga su waɗanda Allah ya kira, Yahudawa da Hellenawa, Kiristi ikon Allah ne, da kuma hikimar Allah.
25 Because the foolishness of God is wiser than man's, and the weakness of God is stronger than man's.
Gama wautar Allah ta fi hikimar mutum, kuma rashin ƙarfin Allah ya fi ƙarfin mutum.
26 For consider your calling, brothers, that not many were wise from a human perspective, not many mighty, not many of noble birth.
’Yan’uwa, ku tuna yadda kuke sa’ad da aka kira ku. Babu masu hikima da yawa a cikinku, bisa ga ganin mutum; babu masu iko da yawa, babu masu martaba da yawa bisa ga haihuwa.
27 But God chose the foolish of the world to shame the wise. And God chose the weak of the world to shame the strong.
Amma Allah ya zaɓi abubuwa masu wautata duniya, don yă kunyata masu hikima. Allah ya zaɓi abubuwa marasa ƙarfi na duniya, domin ya ba wa masu ƙarfi kunya.
28 And God chose the lowly of the world, and the despised, what is considered to be nothing, to bring to nothing what is considered to be something,
Ya zaɓi abubuwa marasa martaba na wannan duniya da kuma abubuwan da aka rena da abubuwan da ba a ɗauka a bakin kome ba, domin a wofinta abubuwan da ake ganinsu da daraja,
29 that no flesh might boast before God.
domin kada wani ya yi taƙama a gabansa.
30 And because of him you are in Christ Jesus, who became for us wisdom from God, and righteousness and sanctification and redemption,
Saboda Allah ne kuke cikin Kiristi Yesu, shi wanda ya zama hikima a gare mu daga Allah. Kiristi shi ne adalcinmu, da tsarkinmu, da kuma fansarmu.
31 so that, as it is written, "Let him who boasts, boast in the Lord."
Saboda haka, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Duk wanda yake taƙama, ya yi taƙama a cikin Ubangiji.”