< 1 Chronicles 20 >

1 It happened, at the time of the return of the year, at the time when kings go out, that Joab led forth the army, and wasted the country of the people of Ammon, and came and besieged Rabbah. But David stayed at Jerusalem. Joab struck Rabbah, and overthrew it.
Da bazara, a lokacin da sarakuna kan tafi yaƙi, Yowab ya jagorance mayaƙa. Ya lalatar da ƙasar Ammonawa ya kuma tafi Rabba ya yi mata kwanto, amma Dawuda ya zauna a Urushalima. Yowab ya yaƙi Rabba, ya kuma bar ta kango.
2 David took the crown of their king from off his head, and found it to weigh a talent of gold, and there were precious stones in it; and it was set on David's head: and he brought forth the spoil of the city, a very great amount.
Dawuda ya ɗauki rawani daga kan sarkinsu, nauyinsa ya kai talenti na zinariya, aka kuma yi masa ado da duwatsu masu daraja, sai Dawuda kuwa ya sa a kansa. Ya kuma kwashi ganima mai yawa daga birnin
3 He brought forth the people who were in it, and set them to work with saws, and with iron picks, and with axes. David did so to all the cities of the people of Ammon. David and all the people returned to Jerusalem.
ya kuma fitar da mutanen da suke can, ya sa su aiki da zartuna da makamai masu kaifi da kuma gatura. Dawuda ya yi haka da dukan garuruwan Ammonawa. Sa’an nan Dawuda da mayaƙansa gaba ɗaya suka koma Urushalima.
4 Now it happened afterward that there was again war with the Philistines at Gezer; then Sibbekai the Hushathite killed Saph, a descendant of the Rephaim; and they were subdued.
Ana nan, sai yaƙi ya ɓarke a Gezer tsakanin Isra’ila da Filistiyawa. Sai Sibbekai mutumin Husha ya kashe Siffai, ɗaya daga cikin zuriyar Refahiyawa, ta haka kuma aka ci Filistiyawa da yaƙi.
5 There was again war with the Philistines; and Elhanan the son of Jair the Bethlehemite killed the brother of Goliath the Gittite, the staff of whose spear was like a weaver's beam.
Yaƙi kuma ya sāke tashi tsakanin Isra’ilawa da Filistiyawa, Elhanan ɗan Yayir ya kashe Lahmi ɗan’uwan Goliyat mutumin Gat, wanda yake riƙe da māshi mai sandan masaƙa.
6 There was again war at Gath, where there was a man of great stature, whose fingers and toes were twenty-four, six on each hand, and six on each foot; and he also was descended from the Raphah.
Aka sāke yin wani yaƙin kuma, wanda ya faru a Gat, akwai wani ƙaton mutum mai yatsotsi shida a kowane hannu da kuma yatsotsi shida a kowace ƙafa, yatsotsi ashirin da huɗu ke nan. Shi ma daga zuriyar Rafa ce.
7 When he defied Israel, Jonathan the son of Shimeah David's brother killed him.
Sa’ad da ya yi wa Isra’ila ba’a, sai Yonatan ɗan Shimeya, ɗan’uwan Dawuda ya kashe shi.
8 These were the descendants of the Raphah in Gath; and they fell by the hand of David, and by the hand of his servants.
Waɗannan su ne zuriyar Rafa a Gat, Dawuda da mutanensa sun kashe su.

< 1 Chronicles 20 >