< Mark 9 >
1 He said to them, "Truly I tell you, there are some standing here who will in no way taste death until they see the Kingdom of God come with power."
Ya kuma ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, waɗansu da suke tsattsaye a nan ba za su mutu ba, sai sun ga mulkin Allah ya bayyana da iko.”
2 After six days Yeshua took with him Kipha, Yaquv, and Yukhanan, and brought them up onto a high mountain privately by themselves, and he was changed into another form in front of them.
Bayan kwana shida, sai Yesu ya ɗauki Bitrus, Yaƙub da Yohanna tare da shi, ya kai su kan wani dutse mai tsawo, suka kasance su kaɗai a wurin. A can aka sāke kamanninsa a gabansu.
3 His clothing became glistening, exceedingly white, such as no launderer on earth can whiten them.
Tufafinsa suka zama fari suna ƙyalli, fiye da yadda wani a duniya zai iya yi su.
4 Eliya and Mushe appeared to them, and they were talking with Yeshua.
Iliya da Musa suka bayyana a gabansu, suna magana da Yesu.
5 Kipha said to Yeshua, "Rabbi, it is good for us to be here. Let us make three tents: one for you, one for Mushe, and one for Eliya."
Bitrus ya ce wa Yesu, “Rabbi, ya yi kyau da muke nan. Bari mu kafa bukkoki guda uku, ɗaya dominka, ɗaya domin Musa, ɗaya kuma domin Iliya.”
6 For he did not know what to answer, for they became very afraid.
(Bai san abin da zai faɗa ba ne, gama sun tsorata ƙwarai.)
7 A cloud came, overshadowing them, and a voice came out of the cloud, "This is my beloved Son. Listen to him."
Sai wani girgije ya bayyana, ya rufe su, wata murya kuma ta fito daga girgijen, ta ce, “Wannan Ɗana ne, wanda nake ƙauna, ku saurare shi!”
8 Suddenly looking around, they saw no one with them anymore, except Yeshua alone.
Farat ɗaya, da suka waiwaya, ba su ƙara ganin kowa tare da su ba, sai dai Yesu.
9 As they were coming down from the mountain, he commanded them that they should tell no one what things they had seen, until after the Son of Man had risen from the dead.
Da suna saukowa daga dutsen, Yesu ya umarce su kada su gaya wa kowa abin da suka gani, sai bayan Ɗan Mutum ya tashi daga matattu.
10 They kept this saying to themselves, questioning what the "rising from the dead" meant.
Suka riƙe wannan zance a ɓoye tsakaninsu, suna tattaunawa ko mece ce ma’anar “tashi daga matattu.”
11 They asked him, saying, "Why do the scribes say that Eliya must come first?"
Suka tambaye shi, suka ce, “Don me malaman dokoki suke cewa, sai Iliya ya fara zuwa?”
12 And he said to them, "Eliya indeed comes first, and restores all things. And why is it written of the Son of Man that he should suffer many things and be rejected?
Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya ne, Iliya zai zo da fari, yă kuma mayar da dukan abubuwa. Don me kuma aka rubuta cewa, dole Ɗan Mutum yă sha wahala sosai, kuma a ƙi shi?
13 But I tell you that Eliya has come, and they have also done to him whatever they wanted to, even as it is written about him."
Amma ina faɗa muku, Iliya ya riga ya zo, kuma suka yi duk abin da suka ga dama da shi, kamar yadda aka rubuta game da shi.”
14 And when they came to the disciples, they saw a large crowd around them, and scribes questioning them.
Da suka dawo wurin sauran almajiran, sai suka ga babban taro kewaye da su, malaman dokoki suna gardama da su.
15 Immediately all the crowd, when they saw him, were greatly amazed, and running to him greeted him.
Nan take da dukan mutanen suka ga Yesu, sai suka cika da mamaki, suka ruga da gudu don su gai da shi.
16 He asked them, "What are you arguing about with them?"
Ya tambaye su ya ce, “Gardamar me kuke yi da su?”
17 And one out of the crowd answered him, "Teacher, I brought to you my son, who has a mute spirit;
Wani mutum a cikin taron ya amsa ya ce, “Malam, na kawo maka ɗana mai wani ruhun da yake hana shi magana.
18 and wherever it seizes him, it throws him down, and he foams at the mouth, and grinds his teeth, and wastes away. I asked your disciples to cast it out, and they weren't able."
Duk lokacin da mugun ruhun ya kama shi, yakan jefa shi a ƙasa. Bakinsa yakan yi kumfa, yă cije haƙorarsa, yakan sa jikinsa ya sandare, yă zama da ƙarfi. Na roƙi almajiranka su fitar da ruhun, amma ba su iya ba.”
19 And answering, he said to them, "You unbelieving generation, how long must I be with you? How long must I put up with you? Bring him to me."
Yesu ya ce, “Ya ku zamani marar bangaskiya, har yaushe zan kasance tare da ku? Har yaushe zan yi haƙuri da ku? Kawo mini yaron.”
20 They brought him to him, and when he saw him, immediately the spirit convulsed him, and he fell on the ground, wallowing and foaming at the mouth.
Sai suka kawo shi. Da ruhun ya ga Yesu, nan da nan sai ya buge yaron da farfaɗiya. Ya fāɗi a ƙasa, yana birgima, bakinsa yana kumfa.
21 He asked his father, "How long has it been since this has come to him?" He said, "From childhood.
Yesu ya tambayi mahaifin yaron ya ce, “Tun yaushe yake haka?” Ya ce, “Tun yana ƙarami.
22 And it has often cast him both into fire and into water, to destroy him. But if you can do anything, have compassion on us, and help us."
Ya sha jefa shi cikin wuta, ko ruwa don yă kashe shi. Amma in za ka iya yin wani abu, ka ji tausayinmu ka taimake mu.”
23 Yeshua said to him, "'If you can?' All things are possible to him who believes."
Yesu ya ce, “‘In za ka iya’? Ai, kome mai yiwuwa ne ga wanda ya gaskata.”
24 Immediately the father of the child cried out and said, "I believe. Help my unbelief."
Nan da nan mahaifin yaron ya faɗa da ƙarfi ya ce, “Na gaskata, ka taimake ni in sha kan rashin bangaskiyata!”
25 When Yeshua saw that a crowd came running together, he rebuked the unclean spirit, saying to him, "You deaf and mute spirit, I command you, come out of him, and never enter him again."
Da Yesu ya ga taron suna zuwa can a guje, sai ya tsawata wa mugun ruhun ya ce, “Kai ruhun kurma, da na bebe, na umarce ka, ka fita daga cikinsa, kada kuma ka ƙara shigarsa.”
26 Having screamed, and convulsed greatly, it came out of him. The boy became like one dead; so much that most of them said, "He is dead."
Sai ruhun ya yi ihu, ya buge shi da ƙarfi da farfaɗiya, ya fita. Yaron ya kwanta kamar matacce, har mutane da yawa suka ce, “Ai, ya mutu.”
27 But Yeshua took him by the hand, and raised him up; and he arose.
Amma Yesu ya kama shi a hannu ya ɗaga, ya kuwa tashi tsaye.
28 And when he had come into the house, his disciples asked him privately, "Why could we not cast it out?"
Da Yesu ya shiga gida, almajiransa suka tambaye shi a ɓoye, suka ce, “Me ya sa ba mu iya fitar da shi ba?”
29 And he said to them, "This kind cannot come out by anything but prayer and fasting."
Ya amsa ya ce, “Sai da addu’akaɗai irin wannan yakan fita.”
30 They went out from there, and passed through Galila. He did not want anyone to know it.
Suka bar wurin suka bi ta Galili. Yesu bai so wani yă san inda suke ba,
31 For he was teaching his disciples, and said to them, "The Son of Man is being handed over to the hands of men, and they will kill him; and when he is killed, after three days he will rise again."
gama yana koya wa almajiransa. Ya ce musu, “Za a ci amanar Ɗan Mutum, a ba da shi ga hannun mutane. Za su kashe shi, bayan kwana uku kuma zai tashi.”
32 But they did not understand the saying, and were afraid to ask him.
Amma ba su fahimci abin da yake nufi ba, suka kuma ji tsoro su tambaye shi game da wannan.
33 He came to Kepharnakhum, and when he was in the house he asked them, "What were you arguing on the way?"
Suka iso Kafarnahum. Da yana cikin gida, sai ya tambaye su ya ce, “Gardamar me kuke yi a hanya?”
34 But they were silent, for they had disputed one with another on the way about who was the greatest.
Amma suka yi shiru, don a hanya suna gardama ne, a kan ko wane ne a cikinsu ya fi girma?
35 And he sat down, and called the twelve; and he said to them, "If anyone wants to be first, he must be last of all, and servant of all."
Da Yesu ya zauna, sai ya kira Sha Biyun ya ce, “In wani yana so yă zama na fari, dole yă zama na ƙarshe duka, da kuma bawan kowa.”
36 He took a little child, and set him in the midst of them. Taking him in his arms, he said to them,
Ya ɗauki wani ƙaramin yaro ya sa yă tsaya a tsakiyarsu. Ya ɗauke shi a hannunsa, ya ce musu,
37 "Whoever receives one such little child in my name, receives me, and whoever receives me, does not receive me, but him who sent me."
“Duk wanda ya karɓi ɗaya daga cikin waɗannan ƙananan yara a cikin sunana, ni ya karɓa. Duk wanda kuma ya karɓe ni, ba ni ya karɓa ba, amma wanda ya aiko ni ne ya karɓa.”
38 Yukhanan said to him, "Teacher, we saw someone casting out demons in your name; and we forbade him, because he was not following us."
Yohanna ya ce, “Malam mun ga wani mutum yana fitar da aljanu a cikin sunanka, sai muka ce yă daina, domin shi ba ɗaya daga cikinmu ba ne.”
39 But Yeshua said, "Do not forbid him, for there is no one who will do a mighty work in my name, and be able quickly to speak evil of me.
Yesu ya ce, “Kada ku hana shi. Ba wanda yake yin ayyukan banmamaki a cikin sunana, nan take yă faɗi wani abu mummuna game da ni.
40 For whoever is not against us is for us.
Gama duk wanda ba ya gāba da mu, namu ne.
41 For whoever will give you a cup of water to drink in my name, because you belong to the Meshikha, truly I tell you, he will in no way lose his reward.
Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ya ba ku ruwan sha a sunana, saboda ku na Kiristi ne, lalle, ba zai rasa ladarsa ba.
42 Whoever will cause one of these little ones who believe in me to stumble, it would be better for him if he was thrown into the sea with a millstone hung around his neck.
“Idan kuma wani yă sa ɗaya daga cikin waɗannan’yan yara masu gaskatawa da ni yă yi laifi, zai fiye masa a rataya wani babban dutsen niƙa a wuyarsa, a jefa shi cikin teku.
43 If your hand causes you to stumble, cut it off. It is better for you to enter into life maimed, rather than having your two hands to go into Gihana, into the unquenchable fire, (Geenna )
In hannunka yana sa ka yin zunubi, yanke shi. Ai, gwamma ka shiga rai da hannu ɗaya, da ka shiga jahannama ta wuta, inda ba a iya kashe wutar ba, da hannuwanka biyu. (Geenna )
45 If your foot causes you to stumble, cut it off. It is better for you to enter into life lame, rather than having your two feet to be cast into Gihana. (Geenna )
In kuma ƙafarka tana sa ka yin zunubi, yanke ta. Ai, gwamma ka shiga rai da ƙafa ɗaya, da a jefa ka cikin jahannama ta wuta, da ƙafafunka biyu. (Geenna )
47 If your eye causes you to stumble, cast it out. It is better for you to enter into the Kingdom of God with one eye, rather than having two eyes to be cast into Gihana, (Geenna )
In kuma idonka yana sa ka zunubi, ƙwaƙule shi. Ai, gwamma ka shiga mulkin Allah da ido ɗaya, da a jefa ka cikin jahannama ta wuta, da idanu biyu, (Geenna )
48 'where their worm does not die, and the fire is not quenched.'
inda “‘tsutsotsinsu ba sa mutuwa, wutar kuma ba a iya kashewa.’
49 For everyone will be salted with fire, and every sacrifice will be salted with salt.
Za a tsarkake kowa da wuta.
50 Salt is good, but if the salt has lost its saltiness, how can you make it salty? Have salt in yourselves, and be at peace with one another."
“Gishiri yana da daɗi, amma in ya rabu da ɗanɗanonsa, ta yaya za a sāke mai da ɗanɗanonsa? Ku kasance da gishiri a cikinku, ku kuma yi zauna lafiya da juna.”