< Hebrews 5 >

1 For every high priest, being taken from among people, is appointed for people in things pertaining to God, that he may offer both gifts and sacrifices for sins.
Kowanne babban firist, da yake an zabe shi ne daga cikin mutane, a kansa shi ya wakilci mutane ga al'amarin Allah, don ya mika sadakoki da kuma hadayu domin kawar da zunubai.
2 The high priest can deal gently with those who are ignorant and going astray, because he himself is also surrounded with weakness.
Yana kuma iya tafiyar da jahilai da sangartattu a cikin salihanci, tun da shi ke rarrauna ne shi ta ko'ina.
3 Because of this, he must offer sacrifices for sins for the people, as well as for himself.
Saboda haka, wajibi ne ya mika hadayu, ba saboda kawar da zunuban jama'a kadai ba, har ma da na kansa.
4 Nobody takes this honor on himself, but he is called by God, just like Ahrun was.
Ba wanda zai kai kansa wannan matsayi mai girma, sai dai Allah ya yi kiransa ga haka, kamar yadda aka kirayi Haruna.
5 So also Meshikha did not glorify himself to be made a high priest, but it was he who said to him, "You are my Son. Today I have become your Father."
Haka kuma, Almasihu, ba shi ya daukaka kansa ya zama Babban firist ba, sai dai wannan ne ya sa shi, wanda ya ce da shi, “Kai Dana ne; Yau na zama Uba a gare ka.''
6 As he says also in another place, "You are a priest forever, after the order of Malki-Zedeq." (aiōn g165)
Kamar dai yadda a wani wuri kuma ya ce, “Kai firist ne na har abada, bisa ga kwatancin Malkisadak.” (aiōn g165)
7 In the days of his flesh, he offered up prayers and petitions with loud cries and tears to him who was able to save him from death, and he was heard because of his reverence.
Almasihu, a lokacin zamansa a duniya, ya yi addu'o'i da roke-roke, tare da kuka mai tsanani, har da hawaye, ga wannan da yake da ikon cetonsa daga mutuwa, aka kuwa saurare shi saboda tsannin mika kansa.
8 Although he was a Son, he learned obedience by the things which he suffered.
Ko da yake shi Da ne, ya koyi biyayya ta wurin wuyar da ya sha.
9 Having been made perfect, he became to all of those who obey him the author of everlasting salvation, (aiōnios g166)
Har ya kai ga kammala, sai ya zama tushe madawwami, ceto ga dukkan wadanda suke masa biyayya. (aiōnios g166)
10 named by God a high priest after the order of Malki-Zedeq.
Gama Allah yana kiransa Babban firist, bisa ga kwatancin Malkisadak.
11 About him we have many words to say, and hard to interpret, seeing you have become dull of hearing.
Muna da abu da yawa da za mu fada a game da Yesu, amma zai yi wuyar bayani, da yake basirarku ta dushe.
12 For when by reason of the time you ought to be teachers, you again need to have someone teach you the rudiments of the first principles of the oracles of God. You have come to need milk, not solid food.
Ko da yake yanzu kam, ya kamata ku zama masu koyarwa, duk da haka, ashe, ba ku wuce wani ya sake koya muku jigajigan farko na Maganar Allah ba? har ya zamana sai an ba ku madara ba abinci mai tauri ba?
13 For everyone who lives on milk is not experienced in the word of righteousness, for he is a baby.
To, duk wanda yake madara ce abincinsa, bai kware da maganar adalci ba, kamar jariri yake.
14 But solid food is for those who are full grown, who by reason of use have their senses exercised to discern good and evil.
Amma abinci mai tauri, ai, na manya ne, wato wadanda hankalinsu ya horu yau da kullum, don su rarrabe nagarta da mugunta.

< Hebrews 5 >