< 1 Corinthians 15 >
1 Now I declare to you, brothers, the Good News which I preached to you, which also you received, in which you also stand,
Yanzu ina tunashshe ku 'yan'uwa, game da bisharar nan da nake shelarwa, wadda kuka karba kuke kuma dogara da ita.
2 by which also you are saved, if you hold firmly the word which I preached to you—unless you believed in vain.
Da wannan bishara aka yi maku ceto, idan kuka rike wa'azi da na yi maku da karfi, sai in dama kun gaskanta a banza.
3 For I delivered to you first of all that which I also received: that Meshikha died for our sins according to the Scriptures,
Domin na baku muhimmin sako kamar na farko da na karba: cewa Almasihu ya mutu domin zunubanmu, bisa ga nassosi,
4 that he was buried, that he was raised on the third day according to the Scriptures,
cewa kuma an bizne shi, ya kuwa tashi daga matattu a rana ta uku bisa ga nassosi.
5 and that he appeared to Kipha, then to the twelve.
Cewa kuma ya bayyana ga Kefas, sa'an nan ga sha biyun.
6 After that he appeared to over five hundred brothers at once, most of whom remain until now, but some have also fallen asleep.
Daga nan ya bayyana ga 'yan'uwa sama da dari biyar a lokaci guda. Wadanda mafi yawan su na da rai har yau, amma wasun su sun yi barci.
7 After that he appeared to Yaquv, then to all the apostles,
Daga nan ya bayyana ga Yakubu, da kuma ga manzannin duka.
8 and last of all, as to the child born at the wrong time, he appeared to me also.
A karshe, sai ya bayyana a gare ni, kamar dan da aka haifa bakwaini.
9 For I am the least of the apostles, who is not worthy to be called an apostle, because I persecuted the church of God.
Gama ni ne mafi kankanta a cikin manzanni. Ban cancanci a kira ni manzo ba, domin na tsanantawa ikklisiyar Allah.
10 But by the grace of God I am what I am. His grace which was bestowed on me was not futile, but I worked more than all of them; yet not I, but the grace of God which was with me.
Amma saboda alherin Ubangiji ina matsayin da nake a yau, kuma alherin sa da ke ciki na ba a banza yake ba. A maimako, nayi aiki tukuru fiye da su duka. Amma duk da haka ba ni bane, amma alherin Allah da ke tare da ni.
11 Whether then it was I or they, this is what we preach, and this is what you believed.
Saboda haka ko nine ko Su, haka mukayi wa'azin, haka kuma kuka gaskata.
12 Now if Meshikha is preached, that he has been raised from the dead, how do some among you say that there is no resurrection of the dead?
To idan anyi shela a matsayin cewa Yesu ya tashi daga matattu, tayaya wadansunku su ke cewa babu tashin matattu?
13 But if there is no resurrection of the dead, neither has Meshikha been raised.
Amma idan babu tashin matattu, Almasihu ma ai ba a tashe shi ba kenan.
14 If Meshikha has not been raised, then our preaching is in vain, and your faith also is in vain.
idan kuwa ba a tashi Almasihu ba, wa'azin mu ya zama banza kenan, haka kuma bangaskiyar ku ta zama banza.
15 Yes, we are found false witnesses of God, because we testified about God that he raised up Meshikha, whom he did not raise up, if it is so that the dead are not raised.
Mun kuma zama shaidun karya game Allah kenan, muna shaida akan Allah cewa ya tashi Almasihu daga matattu alhali ko bai tashe shi ba.
16 For if the dead are not raised, neither has Meshikha been raised.
Domin idan babu tashin matattu, kai, ko Almasihu ma ba a tashe shi ba kenan.
17 If Meshikha has not been raised, your faith is vain; you are still in your sins.
Idan har ba a tashi Almasihu ba, bangaskiyar ku a banza take, har yanzu kuma, kuna cikin zunuban ku.
18 Then they also who are fallen asleep in Meshikha have perished.
To wadanda suka mutu cikin Almasihu kuma sun hallaka kenan,
19 If we have only hoped in Meshikha in this life, we are of all people most to be pitied.
idan a wannan rayuwa ce kadai muke da bege cikin Almasihu, to cikin dukkan mutane munfi kowa zama abin tausayi.
20 But now Meshikha has been raised from the dead, the first fruits of those who are asleep.
Amma yanzu, Almasihu ya tashi daga matattu, wanda ya sa shi ya zama nunar fari cikin tashi daga matattu.
21 For since death came by a man, the resurrection of the dead also came by a man.
Domin yadda mutuwa ta shigo duniya ta hanyar mutum guda, hakkan nan ma tashi daga matattu.
22 For as in Adom all die, so also in Meshikha all will be made alive.
Gama kamar yadda a cikin Adamu duka suka mutu, haka kuma a cikin Almasihu za a rayar da duka.
23 But each in his own order: Meshikha the first fruits, then those who are Meshikha's, at his coming.
Amma kowanne da tsarinsa: Almasihu, nunan fari, sannan su wadanda ke na Almasihu za a rayar da su lokacin zuwansa.
24 Then the end comes, when he will deliver up the Kingdom to God, even the Father; when he will have abolished all rule and all authority and power.
Sa'an nan karshen zai gabato, lokacin da Almasihu zai mika mulkin ga Allah Uba. sa'an nan ne zaya kawar da dukkan mulki, martaba da iko.
25 For he must reign until he has put all his enemies under his feet.
Gama mulkinsa zai habaka har sai ya sa dukkan makiyansa a karkashin sawayen sa.
26 The last enemy that will be abolished is death.
Mutuwa kuwa, ita ce makiyi na karshe da za'a hallaka.
27 For, "He put all things under his feet." But when he says "all things" are put under, it is evident that the one who put all things under is the exception.
Domin “yasa dukkan komai a karkashin ikonsa,” Amma da aka ce” yasa dukkan komai a karkashin ikonsa,” a sarari yake cewa wannan baya hada da wanda yasa dukan komai a karkashin ikonsa ba.
28 When all things have been subjected to him, then the Son will also himself be subjected to him who subjected all things to him, that God may be all in all.
Idan dukan abu na karkashin mulkinsa, to Dan da kansa zaya kasance a karkashin ikon shi wanda yasa komai a karkashin ikonsa. Wannan zaya kasance ne saboda Allah Uba ya zama dukkan komai cikin dukkan komai.
29 Or else what will they do who are baptized for the dead? If the dead are not raised at all, why then are they baptized for them?
ko kuma me zai faru da wadanda ake yi wa baftisma domin matattu? Idan kuwa babu tashin matattu sam sam, ina amfanin yi masu baftisma domin su?
30 Why do we also stand in jeopardy every hour?
Kuma me yasa muke cikin hadari kowace sa'a?
31 I affirm, brothers, by the boasting in you which I have in Meshikha Yeshua our Lord, I die daily.
Ina mutuwa kullum. Wannan nake furtawa ta wurin fahariya, 'yan'uwa, wadda nake da ita cikin Almasihu Yesu Ubangijinmu.
32 If I fought with animals at Ephesus for human purposes, what does it profit me? If the dead are not raised, then "let us eat and drink, for tomorrow we die."
Menene ribata, a idanun mutane, idan nayi kokowa da bisashe a Afisa, idan babu tashin matattu? “bari mu ci mu sha, domin gobe zamu mutu.”
33 Do not be deceived. "Bad company corrupts good morals."
Kada fa a yaudare ku, domin “tarayya da mugaye takan bata halayen kirki.”
34 Become sober-minded, and do not sin, for some are ignorant about God. I say this to your shame.
“Ku natsu! kuyi zaman adalci! kada ku cigaba da zunubi. Domin wasunku basu da sanin Allah. Ina fadar wannan domin in baku kunya.
35 But someone will say, "How are the dead raised?" and, "With what kind of body do they come?"
Amma wani zaya ce, “Yaya za'a yi tashin matattu? Wane irin jiki kuma zasu tashi da shi?
36 You foolish one, that which you yourself sow is not made alive unless it dies.
Ku jahilai ne sosai! Abinda ka shuka ba zaya fara girma ba sai ya mutu.
37 That which you sow, you do not sow the body that will be, but a bare grain, maybe of wheat, or of some other kind.
Abinda ka shuka ba jikin da zaya kasance bane, amma kwayar irin ne kawai. Wanda zaya zama alkama ko wani abu daban.
38 But God gives it a body even as it pleased him, and to each seed a body of its own.
Amma Allah zaya bashi jiki yadda ya zaba, ga kowane kwayar iri da nashi jikin.
39 All flesh is not the same flesh, but there is one flesh of humans, another flesh of animals, another of fish, and another of birds.
Ba duka jiki ne yake iri daya ba. A maimako, akwai jiki irin na mutane, akwai kuma wani irin na dabbobi, kuma wani jikin irin na tsuntsaye, kuma da irin na kifi.
40 There are also celestial bodies, and terrestrial bodies; but the glory of the celestial differs from that of the terrestrial.
Akwai kuma jikina na samaniya da jikina na duniya. Amma daukakar jikin samaniya wata daban ce kuma daukakar jikin duniya daban ce.
41 There is one glory of the sun, another glory of the moon, and another glory of the stars; for one star differs from another star in glory.
Akwai daukaka irin ta rana, da kuma wata daukakar irin ta wata, da kuma wata daukakar irin ta taurari. Domin wani tauraron ya bambanta da wani wajen daukaka.
42 So also is the resurrection of the dead. It is sown in corruption; it is raised in incorruption.
Haka yake a tashin matattu. Abinda aka shuka mai lalacewa ne, wanda aka tayar marar lalacewa ne.
43 It is sown in dishonor; it is raised in glory. It is sown in weakness; it is raised in power.
An shuka shi cikin rashin daraja; an tayar da shi cikin daukaka. An shuka shi cikin rauni; an tayar da shi cikin iko.
44 It is sown a natural body; it is raised a spiritual body. There is a natural body and there is also a spiritual body.
An shuka shi jiki na zahiri; an tayar da shi jiki na ruhaniya. Idan akwai jiki na zahiri, to akwai jiki na ruhaniya.
45 So also it is written, "The first man, Adom, became a living soul." The last Adom became a life-giving spirit.
Haka kuma aka rubuta, “Adamu na farko ya zama rayayyen taliki.” Adamu na karshe ya zama Ruhu mai bayar da rai.
46 However that which is spiritual is not first, but that which is natural, then that which is spiritual.
Amma na ruhaniyar ba shine ya fara zuwa ba amma na zahirin, daga nan na ruhaniyar.
47 The first man is of the earth, made of dust. The second man is from heaven.
Mutumin farkon ai daga turbaya ya fito, wato na duniya. Amma shi na biyun daga sama yake.
48 As is the one made of dust, such are those who are also made of dust; and as is the heavenly, such are they also that are heavenly.
kamar yadda mutumin ya fito daga turbaya haka ma wadanda aka halitta da turbaya. kamar yadda mutumin yake daga sama haka ma wadanda ke na sama.
49 As we have borne the image of those made of dust, we will also bear the image of the heavenly.
Kamar yadda muke dauke da jiki mai kamannin turbaya, haka ma zamu kasance da kamannin mutumin sama.
50 Now I say this, brothers, that flesh and blood cannot inherit the Kingdom of God; neither does corruption inherit incorruption.
To wannan na fada, 'yan'uwa, cewa nama da jini ba za su gaji mulkin Allah ba. Haka kuma mai lalacewa ba za ya gaji marar lalacewa ba.
51 Look, I tell you a mystery. We will not all sleep, but we will all be changed,
Duba! ina gaya maku asirtacciyar gaskiya: Ba dukanmu zamu mutu ba, amma dukanmu za a canza mu.
52 in a moment, in the twinkling of an eye, at the last trumpet. For the trumpet will sound, and the dead will be raised incorruptible, and we will be changed.
Za a canza mu nan da nan, cikin keftawar ido, a kaho na karshe. Domin za a busa kaho, kuma za a tada matattu marasa lalacewa, kuma za a canza mu.
53 For this corruptible must put on incorruption, and this mortal must put on immortality.
Domin wannan jiki mai lalacewa dole ya sanya jiki marar lalacewa, kuma wannan jiki mai mutuwa dole ya sanya marar mutuwa.
54 But when this corruptible will have put on incorruption, and this mortal will have put on immortality, then what is written will happen: "Death is swallowed up in victory."
Amma idan wannan jiki mai lalacewa ya sanya marar lalacewa, kuma wannan jiki mai mutuwa ya sanya marar mutuwa, sai abinda aka rubuta ya cika, “An hadiye mutuwa cikin nasara.”
55 "Death, where is your victory? Death, where is your sting?" (Hadēs )
“Mutuwa, ina nasararki? Mutuwa, ina dafinki?” (Hadēs )
56 The sting of death is sin, and the power of sin is the law.
Gama dafin mutuwa zunubi ne, kuma ikon zunubi shari'a ce.
57 But thanks be to God, who gives us the victory through our Lord Yeshua Meshikha.
Amma godiya ga Allah, wanda ya bamu nasara ta wurin Ubangijinmu Yesu Almasihu!
58 Therefore, my beloved brothers, be steadfast, immovable, always abounding in the Lord's work, because you know that your labor is not in vain in the Lord.
Saboda haka, ya ku 'yan'uwana kaunatattu, ku dage kuma kada ku jijjigu. Ko yaushe ku habaka da aikin Ubangiji, domin kun san cewa aikinku cikin Ubangiji ba a banza yake ba.