< Luke 20 >

1 On one of the days while he was teaching the people in the Temple and preaching the gospel, there came up the priest and the Scribes with the elders.
Wata rana da Yesu yana koyar da mutane, yana musu wa’azin bishara a filin haikalin, sai manyan firistoci da malaman dokoki, tare da dattawan suka zo wurinsa.
2 They spoke to him saying. "Tell us by what authority you are doing these things? Who is it that gave you this authority?"
Suka ce masa, “Gaya mana, da wane iko kake yin waɗannan abubuwa. Wa ya ba ka wannan ikon?”
3 "I will also ask you a question," he replied.
Ya amsa ya ce, “Ni ma zan yi muku wata tambaya. Ku faɗa mini,
4 "Was John’s baptism from heaven or from man?"
baftismar Yohanna, daga sama ne ta fito, ko kuwa daga wurin mutane ne?”
5 So they reasoned among themselves. "If we say, ‘From heaven,’ he will ask us, ‘Why did you not believe in him?’
Sai suka yi shawara da junansu, suka ce, “In muka ce, ‘Daga sama ne,’ zai tambaya, ‘To, don me ba ku gaskata shi ba?’
6 "And if we say, ‘From man,’ all the people will stone us, for they were persuaded that Johnwas a prophet."
Amma in kuma muka ce, ‘Daga mutane ne,’ dukan mutanen za su jajjefe mu da duwatsu, domin sun tabbata cewa, Yohanna annabi ne.”
7 So they answered that they did not know whence it was.
Don haka, sai suka amsa cewa, “Ba mu san inda ta fito ba.”
8 "Nor will I tell you," Jesus answered, "by whose authority I do these things."
Yesu ya ce, “To, ni ma ba zan gaya muku, ko da wane iko ne, nake yin waɗannan abubuwa ba.”
9 Then he began to tell the people this parable. "There was a man who planted a vineyard, and let it out to vine-dressers, and went to another country for a long time.
Sai ya ci gaba da gaya wa mutanen wannan misali ya ce, “Wani mutum ya yi gonar inabi, sai ya ba da hayarta ga waɗansu manoma, sa’an nan ya yi wata doguwar tafiya.
10 "At harvest-time he sent a slave to the vine-dressers, to ask them to give him a share of the crop; but the vine-dresser beat him and sent him away empty-handed.
A lokacin girbi, sai ya aiki bawa zuwa wurin masu hayan, don su ba shi daga cikin’ya’yan inabin. Amma’yan hayan suka yi wa bawan nan dūka, suka kore shi hannu wofi.
11 "Then he sent another slave; and him also they flogged and handled shamefully and sent him away empty-handed.
Ya sāke aikan wani bawa, shi ma suka yi masa dūka, suka kunyata shi, suka kuma kore shi hannu wofi.
12 "Then he sent yet a third, and him to they wounded and threw him out.
Har yanzu, ya sāke aikan na uku, amma suka ji masa rauni, suka jefar da shi waje.
13 "Then the master of the vineyard said. "‘What shall I do? I will send my beloved Son; it may be that they will reverence him.’
“Sai mai gonar inabin ya ce, ‘Me zan yi? Zan aiki ɗana da nake ƙauna, wataƙila za su girmama shi.’
14 "But when the vine-dressers saw him, they reasoned together, saying. ‘This is the heir. Let us kill him so that the inheritance may be ours.’
“Amma da’yan hayan suka gan shi, sai suka tattauna zancen, suka ce, ‘Wannan shi ne magājin, mu kashe shi sa’an nan gādon zai zama namu!’
15 "So they turned him out of the vineyard and killed him. "What will the master of the vineyard do to them?
Sai suka fitar da shi waje, suka kashe shi. “To, me mai gonar inabin zai yi da su?
16 "He will come and destroy those vine-dressers, and will give the vineyard to others."
Zai zo ya karkashe masu hayan nan, ya ba wa waɗansu gonar inabin.” Da mutanen suka ji wannan, sai suka ce, “Allah ya sawwaƙa!”
17 He looked at them and said. "Then what does this scripture mean. "The stone which the builders rejected, the same was made the head of the corner?
Yesu ya zura musu ido ya ce, “To, mene ne ma’anar abin da aka rubuta cewa, “‘Dutsen da magina suka ƙi, shi ne kuwa ya zama dutsen kan ginin’
18 "Every one who falls on that stone will be broken in pieces; but whoever it falls upon will be scattered as dust."
Duk wanda ya fāɗi a kan dutsen nan, zai kakkarye. Kuma in dutsen nan ya fāɗi a kan wani, zai murƙushe shi.”
19 At this the Scribes and the high priests were seeking to arrest him; only they were afraid of the people. For they perceived that he had referred to them in this parable.
Malaman dokoki da manyan firistoci, suka nemi hanyar kama shi nan da nan, domin sun san cewa, ya yi wannan misali a kansu ne, amma suna jin tsoron mutane.
20 So they watched him, and sent spies who pretended to be honest men, in order to seize on his speech, and to deliver him up to authority and jurisdiction of the governor.
Sai suka sa masa ido, suka aiki’yan leƙen asiri, waɗanda suka nuna kamar su masu gaskiya ne, suna nufin su kama shi game da abin da zai faɗa, domin su ba da shi ga gwamna mai mulki, da mai iko.
21 So they put a question to him saying. "Rabbi, we know that you speak and teach what is right, and that you do not regard any man’s person, but teach the way of God honestly.
Sai’yan leƙen asirin suka tambaye shi, suka ce, “Malam, mun sani kana faɗin, kuma kana koyar da abin da yake daidai, ba ka kuma nuna bambanci, amma kana koyar da hanyar Allah bisa ga gaskiya.
22 "Is it lawful for us to pay tribute to Caesar or not?"
Daidai ne mu biya haraji ga Kaisar, ko babu?”
23 But he perceived their knavery and answered.
Ya gane makircinsu, sai ya ce musu,
24 "Show me a shilling. Whose image and superscription does it bear?" "Caesar’s," they replied.
“Nuna mini dinari. Hoton wane ne, kuma rubutun wane ne a kai?” Suka amsa, “Na Kaisar.”
25 "Then give to Caesar what belongs to him," he said, "to God give what is God’s."
Sai ya ce musu, “Ku ba wa Kaisar abin da yake na Kaisar, ku kuma ba wa Allah abin da yake na Allah.”
26 So they could not lay hold of his sayings before the people; and marveling at his answer, they held their peace.
Ba su iya kama shi a kan abin da ya faɗa a fili ba. Amsarsa ya ba su mamaki, shi ya sa suka yi shiru.
27 Next came some of the Sadducees who deny that there is resurrection, and they asked him.
Waɗansu Sadukiyawa da suke cewa, ba tashin matattu, suka zo wurin Yesu da tambaya cewa,
28 "Teacher, Moses wrote a law for us that if a man’s brother should die, but leave no children, his brother should take up his wife and raise up his children for his brother.
“Malam, Musa ya rubuta mana cewa, ‘In ɗan’uwan wani mutum ya mutu, ya bar mata amma ba’ya’ya, dole mutumin ya aure gwauruwar, ya samo wa ɗan’uwansa’ya’ya.’
29 "Now there were seven brothers. the first took a wife and died childless,
To, an yi waɗansu’yan’uwa bakwai. Na fari ya auri wata mace, ya mutu ba’ya’ya.
30 "and the second and third took her,
Na biyun,
31 "and likewise all the seven, but left no children when they died.
da na ukun suka aure ta. Haka nan dukansu bakwai suka mutu babu’ya’ya.
32 "Last of all the woman died too.
A ƙarshe, ita macen ma ta mutu.
33 "In the resurrection whose wife shall she be? For they all seven had her as wife."
Shin, a tashin matattu, matar wa za tă zama? Tun da su bakwan nan, sun aure ta.”
34 "People in this world marry and are given in marriage," said Jesus, (aiōn g165)
Yesu ya amsa ya ce, “Mutanen zamanin nan suna aure, suna kuma ba da aure, (aiōn g165)
35 "but those who are counted worthy to reach that world and the resurrection from the dead, neither marry, nor are given in marriage. (aiōn g165)
amma su waɗanda aka ga sun cancantar kasancewa a zamanin can, da kuma na tashin matattu, ba za su yi aure, ko su ba da aure ba. (aiōn g165)
36 "For indeed they cannot die any more; they are equal to the angels, and through being sons of the resurrection are sons of God.
Kuma ba za su sāke mutuwa ba, gama su kamar mala’iku ne. Su’ya’yan Allah ne, tun da su’ya’yan tashin matattu ne.
37 "But that the dead are raised, even Moses clearly implied in the passage about the Bush, when he calls the Lord. "The God of Abraham, the God of Isaac, the God of Jacob.
Amma bisa ga labari na bishiya nan, mai cin wuta da Musa ya gani a jeji, ko Musa ma, ya nuna cewa, matattu suna tashi. Gama ya kira Ubangiji, ‘Allah na Ibrahim, da Allah na Ishaku, da kuma Allah na Yaƙub.’
38 "Now he is not the God of the dead, but of the living; for to him all are alive.’
Shi ba Allah na matattu ba ne, amma na masu rai ne, gama a gare shi, duka na da rai.”
39 Then some of the Scribes said, "Teacher, that was nobly said,"
Sai waɗansu malaman dokoki suka amsa suka ce, “Ka faɗi daidai, malam!”
40 for they no longer dared to ask him any questions.
Kuma ba wanda ya sami ƙarfin halin yin masa waɗansu tambayoyi.
41 "How is it," he asked them, "that they say that Christ is David’s son?
Sai Yesu ya ce musu, “Yaya suke cewa, ‘Kiristi ɗan Dawuda ne?’
42 "for David himself say’s in the book of the Psalms, "The Lord said to my Lord. Sit at my right hand,
Dawuda da kansa ya faɗa a cikin Zabura, “‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana,
43 Until I make thy enemies the footstool at thy feet.
sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”’
44 "David therefore himself calls him ‘Lord,’ and how can he be his son?"
Dawuda ya kira shi ‘Ubangiji.’ Ta, yaya zai zama ɗansa?”
45 Then, in the hearing of all the people, he said to his disciples.
Yayinda dukan mutane suna cikin sauraronsa, sai Yesu ya ce wa almajiransa,
46 "Beware of the Scribes who like to walk about in long robes, and dote on salutations in the marketplaces, and on securing the front seats in the synagogues and the best places at banquets;
“Ku yi hankali da malaman dokoki. Sukan so sa manyan riguna suna zaga, suna sha’awan karɓan gaisuwa a wuraren kasuwanci, da kuma wuraren zama mafi daraja a majami’u, da wuraren bangirma a bukukkuwa.
47 "but they devour widows’ houses and for a pretense make long prayers. These shall receive severer condemnation."
Suna mamaye gidajen gwauraye, kuma don burga, suna dogayen addu’o’i. Ga irin waɗannan mutane, za a yi musu hukunci mai tsanani sosai.”

< Luke 20 >